< 1 Kings 5 >

1 Hiram, the king of Tyre [city], had always been a close friend of King David. When he heard that Solomon had been appointed to become the king after his father was no longer king, he sent some messengers to Solomon [to congratulate him].
Sa’ad da Hiram sarkin Taya ya ji an shafe Solomon sarki yă gāji mahaifinsa Dawuda, sai ya aika da jakadunsa zuwa wurin Solomon, gama shi da Dawuda abokai ne sosai dukan kwanakinsa.
2 Solomon [gave those messengers] this message to take back to Hiram:
Solomon ya mayar da wannan saƙo ga Hiram ya ce,
3 “You know that my father David [led his soldiers to] fight many wars against his enemies in the nearby countries. So he could not [arrange to] build a temple in which we [MTY] could worship Yahweh our God, until after Yahweh enabled [the Israeli army] to defeat [IDM] all his enemies.
“Ka san cewa saboda yaƙe-yaƙen da abokan gāba suka yi da mahaifina a kowane gefe, ya sa bai iya gina haikali domin Sunan Ubangiji Allahnsa ba, sai da Ubangiji ya sa abokan gābansa a ƙarƙashin ƙafafunsa.
4 But now Yahweh our God has enabled us to have peace with all the surrounding countries. [(There is no danger that/We do not need to worry that)] we will be attacked.
Amma yanzu Ubangiji Allahna ya ba ni hutu a kowane gefe, babu kuma gāba ko masifa.
5 Yahweh promised my father David, ‘Your son, whom I will enable to be king after you are no longer king, will build a temple for me [MTY].’ Because of that, I have decided to build a temple in which we can worship [MTY] Yahweh our God.
Ina niyya in gina haikali domin Sunan Ubangiji Allahna, yadda Ubangiji ya faɗa wa mahaifina Dawuda, sa’ad da ya ce, ‘Ɗanka wanda zai gāje ka, shi zai gina haikali domin Sunana.’
6 “So [I am requesting that] you command your workers to cut cedar trees for me. My men will work with them, and I will pay your workers whatever you decide. [But] my men [cannot do the work alone, ] because they do not know how to cut down trees like your workers from Sidon [city] do.”
“Don haka, ka ba da umarni a yanka mini itatuwan al’ul na ƙasar Lebanon. Ma’aikatana za su haɗa hannu da ma’aikatanka, ni kuwa zan biya ka albashin ma’aikatanka kamar yadda ka faɗa. Gama ka san cewa babu wani a cikinmu da ya iya yanka itacen katako kamar Sidoniyawa.”
7 When Hiram heard the message from Solomon, he was very happy and said, “I praise Yahweh today for giving David a very wise son to rule that great nation!”
Da Hiram ya ji saƙon Solomon, sai ya ji daɗi ƙwarai, ya kuma ce, “Yabo ga Ubangiji a yau, gama ya ba wa Dawuda ɗa mai hikima yă yi mulki a bisa wannan al’umma mai girma.”
8 He sent this message back to Solomon: “I have heard the message that you sent to me, and I am ready to do what you ask. I will provide cedar and cypress logs.
Sai Hiram ya aike wa Solomon da kalmomin nan, “Na sami saƙon da ka aika mini, zan kuma yi duk abin da kake so ta wurin tanada katakan al’ul da na fir.
9 My workers will bring the logs down from [the] Lebanon [mountains] to the [Mediterranean] sea. Then they will [tie them together to] make rafts to float them [in the water] along the coast to the place that you indicate. Then my workers will untie the logs, and your workers will take them from there. What I want you to do is to supply food for the people who work in my palace.”
Ma’aikatana za su gangara da su daga Lebanon zuwa bakin teku. Zan sa a ɗaɗɗaura su su bi ruwan teku daga Lebanon zuwa bakin Bahar Rum da za ka nuna mini. A can zan kunce maka su, sa’an nan ka kwashe. Kai kuma za ka biya bukatata ta wurin tanadin abinci wa gidana.”
10 So Hiram [arranged for his workers to] supply all the cedar and cypress logs that Solomon wanted.
A haka Hiram ya ci gaba da aika wa Solomon al’ul da kuma fir da yake bukata.
11 Each year Solomon gave Hiram 100,000 bushels of wheat and 110,000 gallons of pure [olive] oil to feed the people who worked in his palace.
Solomon kuma ya ba wa Hiram mudu gari dubu ashirin na alkama a matsayin abinci domin gidansa, ya ƙara da garwa dubu ashirin na tataccen man zaitun. Solomon ya ci gaba da yin haka ga Hiram, shekara-shekara.
12 Yahweh enabled Solomon to be wise, just like he had promised. Solomon and Hiram made a treaty/agreement that there would be peace between their [two governments/countries].
Ubangiji ya ba wa Solomon hikima, kamar yadda ya yi masa alkawari. Dangantakar zaman lafiya ta kasance tsakanin Hiram da Solomon, su biyun suka yi yarjejjeniya.
13 King Solomon forced 30,000 men from all over Israel to become his workers.
Sarki Solomon ya ɗebi ma’aikata daga dukan Isra’ila, su dubu talatin.
14 Adoniram was their boss. Solomon divided the men into three groups. Each month 10,000 of them went to Lebanon and worked for a month there, and then they came back home for two months.
Ya riƙa aika su dubu goma-goma zuwa Lebanon kowane wata, saboda su yi wata ɗaya a Lebanon, watanni biyu kuma a gida. Adoniram ne ya lura da aikin gandun.
15 Solomon also forced 80,000 men to cut stones in the hilly area and 70,000 men to haul the stones [to Jerusalem].
Solomon ya kasance da’yan ɗauko guda dubu saba’in da masu yankan duwatsu guda dubu tamanin a cikin tuddai,
16 And he also assigned 3,600 men to supervise their work.
ya kuma kasance da shugabanni dubu uku da ɗari uku waɗanda suke lura da aikin, su ne kuma suke bi da ma’aikatan.
17 The king also commanded his workers to cut huge blocks of stones from the quarries and to smooth the sides of the stones. Those huge stones were for the foundation of the temple.
Bisa ga umarnin sarki sai suka cire manyan duwatsu masu kyau don a tanada tushen duwatsun da aka gyara domin haikalin daga wurin haƙar duwatsun.
18 Solomon’s workers and Hiram’s workers and men from Gebal/Byblos [city] shaped the stones and prepared the timber to build the temple.
Gwanayen Solomon da na Hiram da kuma mutanen Gebal, su suka yanka, suka kuma shirya katako da dutse don ginin haikali.

< 1 Kings 5 >