< 1 Kings 2 >

1 When David [knew that he] was about to die, he gave these final instructions to his son Solomon:
Da lokacin mutuwar Dawuda ya yi kusa, sai ya gargaɗe Solomon ɗansa, ya ce,
2 “I am about to die [EUP], like everyone else on earth does. Be courageous and conduct yourself as an adult should.
“Ina gab da bin hanyar da kowa a duniya zai bi. Saboda haka ka yi ƙarfin hali, ka nuna kanka namiji,
3 Do what Yahweh our God tells you to do. Conduct yourself as he wants you to do. Obey all of his laws and commands and precepts and instructions that are written in the laws that Moses [gave us]. Do this in order that you will prosper in all that you do and wherever you go.
ka kiyaye abin da Ubangiji Allahnka yake bukata. Yi tafiya a hanyoyinsa, ka kiyaye ƙa’idodi, da umarnai, da dokoki, da kuma farillansa, kamar yadda suke a rubuce a Dokar Musa, don ka yi nasara a cikin kome da za ka yi, da kuma inda za ka tafi.
4 If you continually do that, Yahweh will do what he promised me: He said, ‘If your descendants do what I tell them to do, and faithfully obey my commands with all their inner beings, they will always be [LIT] the ones who will rule [MTY] Israel.’
Ubangiji kuwa zai kiyaye alkawarinsa gare ni da ya ce, ‘In zuriyarka suka lura da yadda suke rayuwa, in kuma suka yi tafiya da aminci a gabana da dukan zuciyarsu, da kuma dukan ransu, ba za ka kāsa samun mutum a kujerar sarautar Isra’ila ba.’
5 “There is something else [that I want you to do]. You know what Joab did to me. He killed my two army commanders, Abner and Amasa. He murdered them violently [MTY] during a time of peace, pretending that it was a time of war. Those two men (were innocent/had not done what was wrong). But Joab [killed them and] their blood to stain his belt and his sandals.
“Yanzu fa, kai kanka ka san abin da Yowab ɗan Zeruhiya ya yi mini. Abin da ya yi wa shugabanni biyun nan na mayaƙan Isra’ila, wato, Abner ɗan Ner, da Amasa ɗan Yeter. Ya kashe su, ya kuma zub da jininsu a lokacin salama sai ka ce a fage yaƙi, da wannan jini ya yi ɗamara a gindinsa, ya kuma sa takalma a ƙafafunsa.
6 Because you are wise, do to him what you think is best [for you to do], but do not allow him to become old [MTY] and then die [IDM] peacefully. (Sheol h7585)
Ka yi da shi gwargwadon hikimarka, amma kada ka bari yă gangara kabari da furfura cikin salama. (Sheol h7585)
7 “But be kind to the sons of Barzillai, the man from [the] Gilead [region], and be sure that they always have enough food to eat [MTY]. Do that because Barzillai helped me when I was running away from your older brother Absalom.
“Amma ka yi alheri ga’ya’yan Barzillai mutumin Gileyad, ka sa su kasance a cikin waɗanda suke ci a teburinka. Sun goyi bayana sa’ad da nake gudu daga ɗan’uwanka Absalom.
8 Also, [you remember] Gera’s son Shimei from Bahurim [town] in the area where the descendants of Benjamin live. [You know what he did to me]. He cursed me terribly on the day I [left Jerusalem and] went to Mahanaim [town]. But when he later came down to see me at the Jordan [River], I solemnly promised, while Yahweh listened [MTY], that I would not cause him to be executed.
“Ka tuna, akwai kuma Shimeyi ɗan Gera, mutumin Benyamin daga Bahurim, wanda ya yi ta yin mini muguwar la’ana a ranar da na tafi Mahanayim. Sa’ad da ya gangara ya same ni a Urdun, na rantse masa da sunan Ubangiji na ce, ‘Ba zan kashe ka da takobi ba.’
9 But now you must [LIT] surely punish him. You are a wise man, so you will know what you should do to him. He is an old man [MTY], but be sure that he [loses/sheds] a lot of blood when you kill him [MTY].” (Sheol h7585)
Amma yanzu, kada ka ɗauke shi marar laifi. Kai mutum ne mai hikima; za ka san abin da za ka yi da shi. Ka kawo furfuransa zuwa kabari da jini.” (Sheol h7585)
10 Then David died [EUP] and was buried in [that part of Jerusalem which was called] ‘The City of David’.
Sa’an nan Dawuda ya huta tare da kakanninsa. Sai aka binne shi a Birnin Dawuda.
11 David had been the king of Israel for 40 years: He ruled for seven years in Hebron and for 33 years in Jerusalem.
Ya yi sarauta shekaru arba’in a bisa Isra’ila. Wato, shekaru bakwai a Hebron da kuma talatin da uku a Urushalima.
12 Solomon became the ruler/king [MTY] to take the place of his father David and took control of all of the kingdom.
Solomon kuwa ya zauna a kan kujerar sarautar mahaifinsa Dawuda, mulkinsa kuwa ya kahu sosai.
13 [One day] Adonijah came to Solomon’s mother Bathsheba. She said to him, “Have you come because you want things to go well?” He replied, “Yes.”
To, sai Adoniya, ɗan Haggit ya tafi wurin Batsheba mahaifiyar Solomon. Ita kuwa ta tambaye shi ta ce, “Lafiya?” Ya amsa ya ce, “I, lafiya.”
14 But then he said, “I have something to ask you to do.” She said, “Tell me [what you want me to do].”
Sa’an nan ya ƙara da cewa, “Ina da ɗan wani abin da zan faɗa miki.” Ta ce, “Faɗa.”
15 He said, “You know that all the Israeli people expected me to be their king [because I am David’s oldest surviving son]. But that did not happen. Instead, my [younger] brother became king, because that is what Yahweh wanted.
Sai ya ce, “Kamar yadda kika sani, mulkin nan nawa ne. Dukan Isra’ila suna ɗaukana a matsayin sarki. Amma abubuwa suka canja, sai mulkin ya koma ga ɗan’uwana; gama ya zo masa daga Ubangiji ne.
16 Now I have one thing that I ask you to do. Please do not refuse to do it.” She replied, “Tell me [what you want me to do].”
Yanzu ina da roƙo guda da zan yi gare ki. Kada ki hana mini.” Ta ce, “Sai ka faɗa.”
17 He said, “Please ask King Solomon to give to me Abishag, the woman from Shunem [town], to be my wife. [I am sure that] he will not refuse.”
Sai ya ci gaba, “In kin yarda, ki yi magana da Sarki Solomon, gama ba zai ƙi jinki ba, ki ce yă ba ni yarinyan nan, Abishag, mutuniyar Shunam, tă zama matata.”
18 Bathsheba replied, “Okay, I will speak to the king for you.”
Batsheba ta ce, “Da kyau, zan yi magana da sarki dominka.”
19 So Bathsheba went to King Solomon, to tell him what Adonijah wanted. The king got up [from his throne] and went to greet her and bowed down to her. Then he sat on his throne again and asked someone to bring a chair for her. So she sat down at the king’s right side.
Sai Batsheba ta tafi wurin Sarki Solomon don tă yi masa magana a kan Adoniya. Sarki ya miƙe tsaye don yă sadu da ita, ya rusuna mata, ya kuma zauna a kujerar sarautarsa. Ya sa aka kawo wa mahaifiyar sarki kujerar sarauta, ta kuwa zauna a gefen damansa.
20 Then she said, “I have one small thing which I want you to do; please do not say that you will not do it.” The king replied, “Mother, what do you want? I will not refuse you.”
Ta ce, “Ina da ɗan roƙon da zan nema ka yi mini. Ina fata ba za ka hana ni ba.” Sai sarki ya amsa ya ce, “Mahaifiyata, sai ki faɗa in ji, ba zan hana miki ba.”
21 She said, “Allow Abishag to be given to your [older] brother Adonijah to be his wife.”
Saboda haka sai ta ce, “Ka sa a ba wa ɗan’uwanka Adoniya, Abishag mutuniyar Shunam tă zama matarsa.”
22 The king replied [angrily], “What? Are you requesting me to give Abishag to Adonijah? [Does he want me] to allow him to rule the kingdom, too? Because he is my older brother, [does he think that he should be the king]? Does he think that Abiathar should be the priest [instead of Zadok], and that Joab [should be the army commander instead of Benaiah] because they supported him [when he tried to become the king]?”
Sarki Solomon ya amsa wa mahaifiyarsa ya ce, “Me ya sa kika roƙar wa Adoniya Abishag mutuniyar Shunam kawai? Ki ma sa a ba shi mulkin mana. Ai, shi yayana ne. I, ki roƙa dominsa, da domin Abiyatar firist, da kuma domin Yowab ɗan Zeruhiya mana!”
23 Then Solomon solemnly promised, requesting Yahweh to listen, “I wish God would strike me and kill me if I do not cause Adonijah to be executed for requesting this!
Sai Sarki Solomon ya rantse da sunan Ubangiji ya ce, “Bari Allah yă yi mini hukunci mai tsanani, idan ban sa Adoniya ya biya wannan roƙo da ransa ba!
24 Yahweh has appointed me to be the king and placed me here to rule [MTY] as my father David did. He has promised that my descendants [MTY] will be the kings of Israel. So just as surely as Yahweh lives, I solemnly promise that Adonijah will be executed today!”
Yanzu kuwa, muddin Ubangiji yana a raye, shi wanda ya kafa ni sosai a kan kujerar sarautar mahaifina Dawuda, ya kuma kafa mini mulki kamar yadda ya yi alkawari; za a kashe Adoniya yau!”
25 So King Solomon gave orders to Benaiah to [go and] kill Adonijah, and Benaiah did that.
Saboda haka Sarki Solomon ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada yă kashe Adoniya; ya kuwa kashe shi.
26 Then Solomon said to Abiathar the priest, “Go to Anathoth [town], to your land there. You deserve to be killed, but I will not execute you now, because you were the one who [supervised the men who] carried Yahweh’s Sacred Chest for David my father, and you endured all the troubles that my father endured.”
Ga Abiyatar firist kuwa sarki ya ce, “Tafi gonarka a Anatot. Ka cancanci ka mutu, amma ba zan kashe ka yanzu ba, domin ka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji Mai Iko Duka a gaban mahaifina Dawuda, ka kuma sha wahala tare mahaifina.”
27 So Solomon dismissed Abiathar from being the priest of Yahweh. By doing that he caused to happen what Yahweh had said [many years previously] at Shiloh, [that some day he would get rid] of the descendants [MTY] of Eli.
Saboda haka Solomon ya cire Abiyatar daga aikin firist na Ubangiji, ya cika maganar da Ubangiji ya yi a Shilo game da gidan Eli.
28 Joab had not supported Absalom [when he tried to become the king], but he had supported Adonijah. So when Joab heard what had happened, he ran to the Sacred Tent, and he grasped the projections on the corners of the altar, [because he knew that no one would kill him there].
Sa’ad da labarin ya kai wurin Yowab, wanda ya haɗa kai da Adoniya, ko da yake bai haɗa kai da Absalom ba, sai ya gudu zuwa tentin Ubangiji, ya kama ƙahonin bagade ya riƙe.
29 When someone told Solomon that Joab had run to the Sacred Tent and was standing alongside the altar, Solomon told Benaiah, “Go and execute Joab.”
Aka faɗa wa Sarki Solomon cewa Yowab ya gudu zuwa tentin Ubangiji, yana kuma kusa da bagade. Sai Solomon ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada ya ce, “Je ka kashe shi!”
30 So Benaiah went to the Sacred Tent and said to Joab, “The king commands you to come out!” But Joab replied, “No, I will die here.” So Benaiah went back to the king and reported [what he had said to Joab, and] what Joab had replied.
Sai Benahiya ya shiga tentin Ubangiji ya ce wa Yowab, “Sarki ya ce, ‘Ka fita!’” Amma Yowab ya amsa ya ce, “A’a, a nan zan mutu.” Sai Benahiya ya ce wa sarki, “Ga yadda Yowab ya amsa mini.”
31 The king replied to him, “Do what he has requested. Kill him and bury his body. If you do that, my descendants [MTY] and I will no longer be punished for what Joab did when he killed [MTY] two men who (were innocent/had not done anything that is wrong).
Sai sarki ya umarci Benahiya ya ce, “Yi kamar yadda ya faɗa. Ka kashe shi, ka kuma binne shi, ka wanke ni da gidan mahaifina daga laifin jini marasa laifin da Yowab ya zubar.
32 But Yahweh will punish [MTY] Joab for attacking and killing Abner, the commander of the army of Israel, and Amasa, the commander of the army of Judah, two men who were more righteous and better [DOU] men than he is. My father David did not even know that Joab [was planning to murder them].
Ubangiji zai sāka masa saboda jinin da ya zubar, domin ba da sanin mahaifina Dawuda ne ya fāɗa wa mutum biyun nan da takobi ba. Dukansu biyu, Abner ɗan Ner, shugaban mayaƙan Isra’ila, da Amasa ɗan Yeter, shugaban mayaƙan Yahuda, mutane ne mafi kyau da kuma mafi adalci fiye da shi.
33 Joab and his descendants will be punished [IDM] forever for his murdering Abner and Amasa. But things will forever go well for David’s descendants [MTY] who rule [MTY] as King David did.”
Bari alhakin jininsu yă koma a kan Yowab da kuma zuriyarsa har abada. Amma bari salamar Ubangiji tă kasance a kan Dawuda da zuriyarsa, da gidansa, da kuma mulkinsa, har abada.”
34 So Benaiah went [into the Sacred Tent] and killed Joab. Joab was buried on his property in the desert [part of Judah].
Sai Benahiya ɗan Yehohiyada ya haura ya bugi Yowab, ya kashe shi, ya kuwa binne shi a gidansa a ƙauye.
35 Then the king appointed Benaiah to be the commander of the army instead of Joab, and he appointed Zadok to be the priest instead of Abiathar.
Sai sarki ya sa Benahiya ɗan Yehohiyada ya zama shugaba a bisa mayaƙa a matsayin Yowab, ya kuma sa Zadok firist a wurin Abiyatar.
36 Then the king sent [a messenger] to summon Shimei, and the king said to him, “Build a house for yourself here in Jerusalem. Remain there and do not leave the city to go anywhere.
Sa’an nan sarki ya aika aka kawo Shimeyi, ya kuma ce masa, “Ka gina wa kanka gida a nan a Urushalima, ka zauna a ciki, kada ka kuskura ka tafi wani wuri.
37 Be sure that the day that you leave Jerusalem and go across the Kidron Brook, you will be executed, and it will be (your own fault/what you deserve).”
Gama ran da ka fita, ka haye Kwarin Kidron, ka tabbata za ka mutu, alhakin jininka kuwa zai koma kanka.”
38 Shimei replied, “Your Majesty, what you say is good. I will do what you have said.” So Shimei remained in Jerusalem for several years.
Shimeyi ya amsa wa sarki ya ce, “Abin da ka faɗa yana da kyau. Bawanka zai yi kamar yadda ranka yă daɗe sarki, ya faɗa.” Shimeyi kuwa ya yi zama a Urushalima na dogon lokaci.
39 But three years later, two of Shimei’s slaves ran away. They went to stay with Maacah’s son Achish, the king of Gath [city]. When someone told Shimei that they were in Gath,
Amma bayan shekaru uku, biyu daga cikin bayin Shimeyi suka gudu zuwa wurin Akish ɗan Ma’aka, sarkin Gat. Aka faɗa wa Shimeyi cewa, “Bayinka suna a Gat.”
40 he put a saddle on his donkey and [got on it and] went to Gath. He found his slaves staying with King Achish and brought them back home.
Da jin haka, sai ya tashi ya shimfiɗa wa jakinsa abin zama, ya hau, ya tafi Gat wurin Akish domin neman bayinsa. Shimeyi kuwa ya dawo da su gida daga Gat.
41 But someone told King Solomon that Shimei had gone from Jerusalem to Gath and had returned.
Da aka faɗa wa Solomon cewa Shimeyi ya bar Urushalima zuwa Gat, har ya dawo.
42 So the king sent [a soldier] to summon Shimei and said to him, “I told you to solemnly promise, knowing that Yahweh [MTY] was listening, that you must not leave Jerusalem. I told you [RHQ], ‘Be sure that if you ever leave Jerusalem, you will be executed.’ And you replied [RHQ] to me, ‘What you have said is good; I will do what you have said.’
Sai sarki ya aika a kawo Shimeyi, ya ce masa, “Ban sa ka rantse da sunan Ubangiji, na kuma ja maka kunne cewa, ‘A ranar da ka kuskura ka bar nan ka tafi wani wuri, ka tabbata za ka mutu ba’? A lokacin ka ce mini, ‘Abin da ka faɗa yana da kyau. Zan kuwa kiyaye.’
43 So why did you not do what you solemnly promised to Yahweh? Why did you disobey what I commanded you?”
To, me ya sa ba ka kiyaye rantsuwar da ka yi ga Ubangiji, ka kuma yi biyayya da umarnin da na ba ka ba?”
44 The king also said to Shimei, “You know all the evil things that you did to my father David. So Yahweh will now punish you for the evil things that you did.
Sarki ya ce wa Shimeyi, “Ka sani a zuciyarka dukan muguntar da ka yi wa mahaifina Dawuda. Yanzu Ubangiji zai sāka maka saboda muguntarka.
45 But Yahweh will bless me, and he will enable David’s descendants [MTY] to rule forever.”
Amma za a yi wa Sarki Solomon albarka, sarautar Dawuda kuma za tă kasance a tsare a gaban Ubangiji har abada.”
46 Then the king gave an order to Benaiah, and he went and killed Shimei. So Solomon was completely in control of the kingdom.
Sai sarki ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada, yă fita, yă bugi Shimeyi, yă kashe shi. Ya kuwa kashe shi. Mulki kuwa ya kahu sosai a hannun Solomon.

< 1 Kings 2 >