< 1 John 1 >

1 [I, John, am writing to you about] the one who existed before [there was anything else]. He is the one whom we [apostles] listened to [as he taught us!] We saw him! We ourselves looked at him and touched him! [He is the one who taught us] the message that [enables people to have eternal] life (OR, live [spiritually]).
Wannan da ya kasance tun farko, wanda muka ji, wanda muka gani da idanunmu, wanda muka duba, hannuwanmu kuma suka taɓa, wannan ne muke shela game da Kalman rai.
2 Because he came here [to the earth] and we have seen him, we proclaim to you clearly that the one whom we have seen is the [one who] has always lived. He was [previously] with his Father in heaven, but he came to live among us. (aiōnios g166)
Wannan Rai ya bayyana, muka kuwa gan shi, muka kuma shaida shi, muna kuwa yin muku shelar wannan rai madawwami, wanda dā yake tare da Uba, ya kuma bayyana a gare mu. (aiōnios g166)
3 We proclaim to you the [message about Jesus], the one whom we saw and heard, in order that you may have a close relationship with us. The ones whom we have a close relationship with are God our Father and his Son Jesus Christ.
Muna yin muku shelar abin da muka gani, muka kuma ji ne, domin ku ma ku yi zumunci tare da mu. Zumuncinmu kuwa yana tare da Uba da kuma Ɗansa, Yesu Kiristi.
4 I am writing to you about these things so that [you (will be convinced/believe]) [that they are true, and as a] result we may be completely joyful.
Muna rubuta wannan domin farin cikinmu yă zama cikakke.
5 The message that we heard from Christ and proclaim to you is this: God is [pure in every way. He never sins. He is like] [MET] a [brilliant] light that has no darkness at all.
Wannan shi ne saƙon da muka ji daga wurinsa, muna kuma sanar da ku cewa Allah haske ne; a cikinsa kuwa babu duhu ko kaɗan.
6 If we claim to have a close relationship with [God], but [we conduct our lives in an impure manner, that is like] living [MET] in [evil] darkness. We are lying. We are not conducting our lives according to [God’s] true message.
In muka ce muna zumunci da shi amma muna tafiya cikin duhu, ƙarya muke yi, kuma ba ma rayuwa bisa ga gaskiya.
7 But living [in a pure manner], as God is [living in a pure manner] [MET] [in every way, is like living] in God’s light. If we do that, we have a close relationship with each other. Not only that, but [God] (acquits us/removes [the guilt]) [of] all our sins because [he accepts] what his Son Jesus did for us [when his] blood [flowed from his body when he died. So we should conduct our lives] ([in a manner according to what God says is pure]).
Amma in muna tafiya cikin haske, yadda yake cikin haske, muna da zumunci da juna ke nan, kuma jinin Yesu, Ɗansa, yana tsarkake mu daga dukan zunubi.
8 Those who say they never behave sinfully are deceiving themselves, and refusing [to accept as] true [what God says about them].
In muka ce ba mu da zunubi, muna ruɗin kanmu ne, gaskiya kuwa ba ta cikinmu.
9 But God will do what he says that he will do, and what he does is [always] right. So, if we confess to him that we [have behaved] sinfully, he will forgive [us for] our sins and (will free us from/remove) [the guilt of] all our sins. [Because of that], [we should confess to him that we have behaved sinfully].
In muka furta zunubanmu, shi mai aminci ne, mai adalci kuma, zai gafarta mana zunubanmu, yă kuma tsarkake mu daga dukan rashin adalci.
10 [Because God says that everyone has sinned], those who say/claim that they have never behaved sinfully talk [as though] God lies! They reject what God says [about us]!
In muka ce ba mu yi zunubi ba, mun mai da shi maƙaryaci ke nan, maganarsa kuwa ba ta da wuri a cikinmu.

< 1 John 1 >