< 1 Chronicles 10 >

1 The army of Philistia [again] fought against the Israelis. The Israeli soldiers ran away from them, and many Israelis were killed {the soldiers of Philistia killed many Israelis} on Gilboa Mountain.
To, fa, Filistiyawa suka yi yaƙi da Isra’ilawa; Isra’ilawa kuwa suka gudu a gabansu, da yawa kuma suka mutu a kan Dutsen Gilbowa.
2 The soldiers of Philistia caught up with Saul and his sons, and they killed his sons Jonathan, Abinadab, and Malchishua.
Filistiyawa suka matsa sosai suna bin Shawulu da’ya’yansa maza, suka kuma kashe’ya’yansa maza Yonatan, Abinadab da Malki-Shuwa.
3 The fighting was very fierce around Saul, and the (archers/men who shot arrows) shot Saul and wounded him severely.
Yaƙin ya yi tsanani kewaye da Shawulu, kuma sa’ad da maharba suka rutsa shi, sai suka ji masa rauni.
4 Saul said to the man who was carrying his weapons, “Take out your sword and kill me with it, in order that these heathen Philistines will not be able to injure me [further] and make fun of me [while I am dying].” But the man who was carrying Saul’s weapons was terrified and refused to do that. So Saul took his own sword and fell on it [and died].
Sai Shawulu ya ce wa mai riƙe masa kayan yaƙi, “Zare takobinka ka soke ni, in ba haka ba waɗannan marasa kaciya za su zo su yi mini ba’a.” Amma mai ɗaukar masa kayan yaƙi ya ji tsoro bai kuwa yi haka ba; saboda haka Shawulu ya zāre takobinsa ya fāɗi a kansa.
5 When the man carrying his weapons saw that Saul was dead, he also threw himself on his own sword and died.
Da mai ɗaukar masa kayan yaƙi ya ga Shawulu ya mutu, sai shi ma ya fāɗi a kan takobinsa ya mutu.
6 So Saul and three of his sons all died, and none of his descendants ever became king.
Ta haka Shawulu da’ya’yansa maza uku suka mutu, dukan gidansa kuwa suka mutu tare.
7 When the Israelis who were living in the valley saw that their army had run away and that Saul and his three sons were dead, they left their towns and ran away. Then the soldiers from Philistia came and (occupied/lived in) those towns.
Sa’ad da dukan Isra’ilawa a cikin kwari suka ga cewa mayaƙansu suna gudu, kuma cewa Shawulu da’ya’yansa maza sun mutu, sai suka bar garuruwansu suka gudu. Filistiyawa kuwa suka zo suka zauna a cikinsu.
8 The next day, when the Philistines came to take away the weapons of the dead [Israeli soldiers], they found the corpses of Saul and his three sons on Gilboa Mountain.
Kashegari, da Filistiyawa suka zo don su tuttuɓe waɗanda suka mutu, sai suka sami Shawulu da’ya’yansa maza sun mutu a Dutsen Gilbowa.
9 They took the clothes off Saul’s corpse and [cut off] his head and took it and Saul’s armor.
Suka tuttuɓe shi suka yanke kansa suka ɗauka duk da kayan yaƙinsa, suka kuma aika’yan aika ko’ina a ƙasar Filistiyawa, a yi shela labarin a cikin gumakansu da kuma mutanensu.
10 Then they sent messengers throughout their land, to proclaim the news throughout their own area, to their idols and to the other people. They put Saul’s armor in the temple where their idols were, and they hung Saul’s head in the temple of [their god] Dagon.
Suka sa kayan yaƙinsa a haikalin allahnsu suka kuma rataye kansa a haikalin Dagon.
11 All the people who lived in Jabesh in [the] Gilead [region] heard what the Philistines had done to Saul’s [corpse].
Sa’ad da mazaunan Yabesh Gileyad suka ji dukan abin da Filistiyawa suka yi wa Shawulu,
12 So the bravest men/soldiers of Jabesh went and got the corpses of Saul and his sons and brought them back to Jabesh. They buried their bones under a large tree in Jabesh. Then the people of Jabesh (fasted/abstained from eating food) for seven days.
sai dukan jarumawa suka tafi suka ɗauki jikunan Shawulu da na’ya’yansa maza suka kawo Yabesh. Sa’an nan suka binne ƙasusuwan a ƙarƙashin babban itace oak a Yabesh, suka kuma yi azumi kwana bakwai.
13 Saul died because he did not faithfully obey what Yahweh told him to do. He even went to a woman who talks to the spirits of dead people and asked her what he should do,
Shawulu ya mutu domin rashin aminci ga Ubangiji; bai kiyaye maganar Ubangiji ba, ya ma nemi shawarar mace mai duba,
14 instead of asking Yahweh what he should do. So Yahweh caused him to die, and he appointed David, the son of Jesse, to be the king [of Israel].
bai kuwa nemi nufin Ubangiji ba. Saboda haka Ubangiji ya kashe shi, ya miƙa mulkin ga Dawuda ɗan Yesse.

< 1 Chronicles 10 >