< Luke 8 >

1 Soon afterward Jesus was going through every city and village, preaching and proclaiming the good news of the kingdom of God. The twelve were with him,
Bayan wannan sai Yesu ya zazzaga gari da ƙauye, yana wa’azin bisharar mulkin Allah. Sha Biyun nan kuwa suna tare da shi,
2 as well as some women who had been healed of evil spirits and infirmities: Mary (called Magdalene) from whom seven demons had gone out,
da kuma waɗansu mata waɗanda aka warkar da su daga cututtukansu, da kuma mugayen ruhohi. Cikinsu akwai Maryamu (wadda ake kira Magdalin) wadda aljanu bakwai suka fito daga cikinta.
3 Joanna the wife of Chuza (Herod's steward), Susanna, and many others. These women provided for Jesus and his disciples out of their own resources.
Da Yowanna matar Kuza, manajan iyalin Hiridus; da Suzana; da waɗansu mata da yawa. Waɗannan mata suna taimaka musu cikin hidima, daga cikin abin da suke da shi na zaman gari.
4 As a large crowd was gathering and people were coming to Jesus from town after town, he spoke by way of a parable:
Yayinda taron mai girma na taruwa, mutane kuma daga garuruwa dabam-dabam suna zuwa wurin Yesu, sai ya ba da wannan misali ya ce,
5 “A sower went out to sow his seed. As he sowed, some seed fell along the path and was trampled underfoot, and the birds of the sky devoured it.
“Wani manomi ya fita domin ya shuka irinsa. Da yana watsa irin, sai waɗansu suka fāɗi a kan hanya, aka tattaka su, tsuntsayen sararin sama kuma suka cinye su.
6 Other seed fell on the rock, and as it grew up, it withered away because it had no moisture.
Waɗansu suka fāɗi a kan dutse, da suka tsira sai suka yanƙwane don babu ruwa a wurin.
7 Other seed fell among the thorns, and the thorns grew up with it and choked it.
Waɗansu kuma suka fāɗi a cikin ƙaya. Da suka yi girma tare, sai ƙayan suka shaƙe su.
8 But other seed fell into good soil, and when it grew, it produced a hundred times more than what was sown.” As he said this, he called out, “He who has ears to hear, let him hear.”
Waɗansu kuma har yanzu, suka fāɗi a ƙasa mai kyau, suka yi girma, suka ba da amfani riɓi ɗari-ɗari, fiye da abin da aka shuka.” Da faɗin haka sai ya ce, “Duk mai kunnen ji, yă ji.”
9 Then his disciples asked him, “What does this parable mean?”
Almajiransa suka tambaye shi ma’anar wannan misali.
10 He said, “To you it has been given to know the mysteries of the kingdom of God, but to the rest I speak in parables, so that ‘they may see but not perceive, and hear but not understand.’
Sai ya ce, “Ku ne aka ba sanin asirin mulkin Allah, amma ga sauran mutane kam, ina magana da misalai, saboda, “‘ko da yake suna kallo, ba za su gani ba, ko da yake suna ji, ba za su gane ba.’
11 “Now this is the meaning of the parable: The seed is the word of God.
“Ga ma’anar misalin, irin, shi ne maganar Allah.
12 The ones along the path are those who hear; then the devil comes and takes away the word from their heart, so that they may not believe and be saved.
Waɗanda suka fāɗi a kan hanya su ne mutanen da suka ji, amma Iblis, yakan zo ya ɗauke maganar daga zuciyarsu, don kada su gaskata, su sami ceto.
13 The ones on the rock are those who, when they hear the word, receive it with joy. Yet they have no root; they believe for a while, but in a time of testing they fall away.
Na kan dutse kuwa, su ne da jin maganar, sukan karɓa da murna, amma ba su da saiwa. Sukan gaskata na ɗan lokaci, amma lokacin gwaji, sai su ja da baya.
14 The seed that fell among the thorns are those who have heard, but as they go on their way they are choked by the cares, riches, and pleasures of this life, and their fruit does not mature.
Irin da suka fāɗi a cikin ƙaya kuwa, su ne mutanen da suka ji, amma a kwana a tashi, tunanin kayan duniya, da neman arziki, da son jin daɗi, sukan hana su ba da’ya’ya.
15 But the seed in the good soil are those who hear the word, hold fast to it with an honest and good heart, and bear fruit with patient endurance.
Amma irin da suka fāɗi a ƙasa mai kyau kuwa, su ne mutane masu kyakkyawar zuciya, mai kyau, da suka ji, suka riƙe, suka kuma jimre har suka ba da’ya’ya.”
16 “No one lights a lamp and covers it with a container or puts it under a bed. Instead, it is put on a lampstand, so that those who come in may see its light.
“Ba mai ƙuna fitila sa’an nan ya ɓoye ta a cikin tulu, ko kuma ya sa ta a ƙarƙashin gado ba. A maimakon haka, yakan sa ta a kan wurin ajiye fitila, saboda mutane masu shigowa su ga haske.
17 For nothing is hidden that will not be made manifest, nor is anything hidden away that will not be made known and come to light.
Ba abin da yake ɓoye da ba za a fallasa ba. Kuma ba abin da yake rufe, da ba za a sani ba, ko a fitar da shi a fili ba.
18 Therefore consider how you hear, for whoever has will be given more, but whoever does not have, even what he thinks he has will be taken away from him.”
Saboda haka, ku yi tunani da kyau yadda kuke saurara. Duk wanda yake da shi, za a ƙara masa, duk wanda ba shi da shi kuma, abin da yake tsammani yana da shi ma, za a karɓe daga gare shi.”
19 Then Jesus' mother and brothers came to him, but they were not able to reach him because of the crowd.
Sai uwar Yesu da’yan’uwansa suka zo, domin su gan shi, amma ba su iya zuwa kusa da shi ba, saboda taron.
20 So some people told him, “Yoʋr mother and yoʋr brothers are standing outside, wishing to see yoʋ.”
Sai wani ya faɗa masa cewa, “Ga uwarka da’yan’uwanka suna tsaye a waje suna so su gan ka.”
21 But he answered them, “My mother and my brothers are those who hear the word of God and obey it.”
Ya amsa ya ce, “Mahaifiyata da’yan’uwana, su ne waɗanda suke jin maganar Allah, suna kuma aikata ta.”
22 One day Jesus got into a boat with his disciples and said to them, “Let us cross over to the other side of the lake.” So they set out,
Wata rana Yesu ya ce wa almajiransa, “Mu haye zuwa wancan gefen tafkin.” Sai suka shiga jirgin ruwa suka fara tafiya.
23 and as they were sailing along, he fell asleep. Then a windstorm came down on the lake, and they were in danger as the boat was being swamped by the waves.
Da suna cikin tafiya, sai barci ya kwashe shi. Sai wata babban iska ta taso kan tafkin, har ruwa ya fara shiga cikin jirgin. Suka shiga babban hatsari.
24 So they came to Jesus and woke him up, saying, “Master, Master, we are perishing!” Then he rose and rebuked the wind and the raging water. They ceased, and all was calm.
Almajiran suka je suka tashe shi daga barci, suka ce, “Ubangiji, Ubangiji, za mu nutse!” Ya tashi ya kwaɓe iskar da kuma haukar ruwan. Sai ruwan da iskar suka natsu. Kome ya yi tsit.
25 Then he said to his disciples, “Where is your faith?” But they were afraid and amazed, saying to one another, “Who then is this, that he commands even the winds and the water, and they obey him?”
Sai ya tambayi almajiransa, “Ina bangaskiyarku?” A cikin tsoro da mamaki, suka ce wa junansu, “Wane ne wannan? Yana ba da umarni ga iska da ruwa ma, kuma suna biyayya da shi?”
26 Then they sailed to the region of the Gadarenes, which is across the lake from Galilee.
Suka shiga jirgin ruwa zuwa yankin Gerasenawa da yake a hayin tafkin, daga wajen Galili.
27 When Jesus stepped ashore, he was met by a man from the city who had been possessed by demons for a long time. This man did not wear clothes or live in a house but among the tombs.
Da Yesu ya sauka daga jirgin, sai ga wani mutum mai aljanu daga garin. Mutumin ya daɗe bai sa tufafi ba, kuma ba ya zama a gida. Yana zama a cikin kaburbura.
28 When he saw Jesus, he cried out, fell down before him, and said with a loud voice, “What do yoʋ have to do with me, Jesus, Son of the Most High God? I beg yoʋ, do not torment me.”
Da ya ga Yesu, sai mutumin ya ɗaga murya da ƙarfi, ya fāɗi a gabansa, yana ihu cewa, “Ina ruwanka da ni, Yesu, Ɗan Allah Mafi Ɗaukaka? Ina roƙonka, kada ka ba ni wahala!”
29 For Jesus had commanded the unclean spirit to come out of the man. Many times it had seized him, and he would be bound with chains and shackles and kept under guard, but he would break the chains and be driven by the demon into desolate places.
Gama Yesu ya riga ya umarci mugun ruhun ya fita daga mutumin. Sau da yawa mugun ruhun ya sha kamunsa. Ko da yake akan daure shi hannu da ƙafa, da sarƙa, a kuma yi gadinsa, amma yakan tsinke sarƙoƙinsa, aljanun kuma su kore shi zuwa wuraren kaɗaici, inda ba kowa.
30 Jesus then asked him, “What is yoʋr name?” He said, “Legion,” for many demons had entered him.
Yesu ya tambaye shi, “Mene ne sunanka?” Sai ya amsa, “Tuli,” gama aljanu masu ɗumbun yawa ne suna cikinsa.
31 And he begged Jesus not to command them to go away into the abyss. (Abyssos g12)
Suka yi ta roƙonsa kada yă umarce su su shiga ramin Abis. (Abyssos g12)
32 Now there was a herd of many pigs feeding there on the mountain. The demons begged Jesus to permit them to enter the pigs. So he gave them permission.
A wurin kuwa, akwai babban garken aladu da suke kiwo a gefen tudu. Aljanun suka roƙi Yesu ya bar su, su shiga cikin aladun, ya kuwa yardar musu.
33 Then the demons came out of the man and went into the pigs, and the herd rushed down the steep bank into the lake and were drowned.
Da aljanun suka fita daga cikin mutumin, sai suka shiga cikin aladun. Garken kuma ya gangara daga kan tudun zuwa cikin tafkin, kuma suka nutse.
34 When those who had been feeding the pigs saw what happened, they ran off and reported it in the city and in the countryside.
Da masu kiwon aladun suka ga abin da ya faru, sai suka ruga da gudu zuwa garin da kewaye suka kai labari.
35 So the people came out to see what had happened. When they came to Jesus, they found the man from whom the demons had gone out sitting at Jesus' feet, clothed and in his right mind, and they were afraid.
Mutanen kuma suka fito don su ga abin da ya faru. Da suka iso wurin Yesu, sai suka tarar da mutumin da aljanun suka fita daga cikinsa, yana zaune kusa da Yesu sanye da tufafi, kuma cikin hankalinsa, sai tsoro ya kama su.
36 Those who had seen it told them how the demon-possessed man had been delivered.
Waɗanda suka ga abin da faru, suka gaya wa mutanen yadda aka warkar da mai aljanun.
37 Then the entire multitude from the surrounding region of the Gadarenes asked Jesus to depart from them, for they were seized with great fear. So he got into the boat and left.
Sai dukan mutanen yankin Gerasenawa suka roƙi Yesu ya bar su, don sun tsorata sosai. Sai Yesu ya shiga jirgin ruwa ya tafi.
38 Now the man from whom the demons had gone out begged to go with him. But Jesus sent him away, saying,
Mutumin da aka fitar da aljanun daga cikinsa, ya roƙi Yesu don yă tafi tare da shi, amma Yesu ya sallame shi ya ce,
39 “Return to yoʋr house, and declare all that God has done for yoʋ.” So the man went away, proclaiming throughout the entire city all that Jesus had done for him.
“Koma gida, ka shaida babban alherin da Allah ya yi maka.” Sai mutumin ya tafi yana faɗin abin da Yesu ya yi masa a duk garin.
40 Now when Jesus returned, the crowd welcomed him, for they had all been waiting for him.
Da Yesu ya koma, taron suka marabce shi, don dā ma duk suna jiransa.
41 And behold, there came a man named Jairus, who was a ruler of the synagogue. He fell down at Jesus' feet and begged him to come to his house,
Sai wani mutum mai suna Yayirus, wani mai mulkin majami’a, ya zo ya fāɗi a gaban Yesu, yana roƙonsa ya zo gidansa,
42 because he had an only daughter, about twelve years old, and she was dying. As Jesus went on his way, the crowds were pressing in on him.
domin diyarsa ɗaya tak, wadda ta kai shekara goma sha biyu, tana bakin mutuwa. Da Yesu yake kan hanyarsa, taron mutane masu yawa suka yi ta matsa shi a kowane gefe.
43 Now there was a woman who had suffered from a flow of blood for twelve years, and even though she had spent her entire livelihood on physicians, she could not be healed by anyone.
A wurin kuwa, akwai wata mace wadda tana da ciwon zubar da jini, har na shekara goma sha biyu, amma babu wanda ya iya warkar da ita.
44 She came up behind Jesus and touched the fringe of his garment, and the flow of her blood stopped at once.
Sai ta zo ta bayansa, ta taɓa bakin rigarsa. Nan da nan, zubar da jininta ya tsaya.
45 Then Jesus said, “Who touched me?” When everyone denied it, Peter and those who were with him said, “Master, the crowds are surrounding yoʋ and pressing against yoʋ, and yet yoʋ say, ‘Who touched me?’”
Yesu ya yi tambaya, “Wa ya taɓa ni?” Bayan kowa ya yi musu, sai Bitrus ya ce, “Ubangiji, ai, mutane da yawa suna matsinka ta kowane gefe.”
46 But Jesus said, “Someone touched me, for I know that power has gone out from me.”
Amma Yesu ya ce, “Wani ya taɓa ni, na san cewa iko ya fita daga wurina.”
47 When the woman saw that she could not escape notice, she came trembling and fell down before him, and in the presence of all the people she told him the reason why she had touched him, and how she had been healed at once.
Sai macen, da ta ga ba halin ɓoyewa, sai ta fita, jikinta na rawa, ta fāɗi a gabansa. A gaban dukan mutanen, ta faɗi dalilin da ya sa ta taɓa shi, da yadda ta warke nan take.
48 Then Jesus said to her, “Take courage, daughter; yoʋr faith has healed yoʋ. Go in peace.”
Sai Yesu ya ce mata, “Diyata, bangaskiyarki ta warkar da ke. Ki sauka lafiya.”
49 While he was still speaking, someone came from the ruler of the synagogue's house and said to him, “Yoʋr daughter has died; do not trouble the teacher.”
Yayinda Yesu na cikin magana har yanzu, sai ga wani daga gidan Yayirus, mai mulkin majami’ar ya ce, “Kada ka ƙara damun malam, diyarka ta rasu.”
50 But when Jesus heard this, he said to him in response, “Do not be afraid; only believe, and she will be healed.”
Da Yesu ya ji wannan, sai ya ce wa Yayirus, “Kada ka ji tsoro, ka gaskata, za a kuma warkar da ita.”
51 When he came to the house, Jesus allowed no one to go in, except Peter, John, James, and the child's father and mother.
Da ya iso gidan Yayirus, sai ya hana kowa yă bi shi cikin ɗakin, sai dai Bitrus, da Yohanna, da Yaƙub, da kuma mahaifin da mahaifiyar.
52 Meanwhile, all the people were weeping and mourning for her, but Jesus said, “Do not weep; she is not dead but sleeping.”
Ana cikin haka, dukan mutanen kuma sai kuka da makoki suke ta yi, domin yarinyar. Sai Yesu ya ce, “Ka daina yin kuka, ba tă mutu ba, tana barci ne.”
53 And they began laughing at him, knowing that she was dead.
Sai suka yi masa dariya, da yake sun san cewa, ta mutu.
54 But Jesus put them all outside, took hold of the girl's hand, and called out, “Child, arise!”
Amma Yesu ya kama ta a hannu ya ce, “Diyata, tashi.”
55 Her spirit returned, and she got up at once. Then he told them to give her something to eat.
Ruhunta ya dawo, kuma ta tashi, nan take. Yesu ya ce musu, su ba ta wani abu tă ci.
56 Her parents were amazed, but he ordered them not to tell anyone what had happened.
Iyayenta suka yi mamaki, amma ya ba su umarni kada su faɗa wa kowa abin da ya faru.

< Luke 8 >