< Luke 1 >

1 Since many have undertaken to compile an account of the events that have been fulfilled among us,
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 just as those who from the beginning were eyewitnesses and ministers of the word have delivered them to us,
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 it seemed good to me also, having carefully investigated all things from the beginning, to write an orderly account for yoʋ, most excellent Theophilus,
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 so that yoʋ may know the certainty of the things about which yoʋ have been instructed.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 In the days of Herod, the king of Judea, there was a priest named Zechariah who belonged to the division of Abijah. His wife was of the daughters of Aaron, and her name was Elizabeth.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 They were both righteous before God, walking blamelessly in all the commandments and regulations of the Lord.
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 But they had no children because Elizabeth was barren, and they were both advanced in their days.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 While Zechariah was serving as a priest before God when his division was on duty,
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 he was chosen by lot, according to the custom of the priesthood, to enter the temple of the Lord and burn incense.
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 At the hour of incense the whole multitude of the people was praying outside.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 Then an angel of the Lord appeared to Zechariah, standing at the right side of the altar of incense.
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 When Zechariah saw him, he was startled, and fear fell upon him.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 But the angel said to him, “Do not be afraid, Zechariah, for yoʋr prayer has been heard. Yoʋr wife Elizabeth will bear yoʋ a son, and yoʋ shall name him John.
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 Yoʋ will have joy and gladness, and many will rejoice at his birth,
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 for he will be great in the sight of the Lord. He must never drink any wine or strong drink, and he will be filled with the Holy Spirit, even from his mother's womb.
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 He will turn many of the sons of Israel to the Lord their God.
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 And he will go before the Lord in the spirit and power of Elijah, to turn the hearts of fathers back to their children, and the disobedient to the wisdom of the righteous, to make ready a people prepared for the Lord.”
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 Zechariah said to the angel, “How can I know this for certain? For I am an old man, and my wife is advanced in her days.”
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 The angel answered him, “I am Gabriel. I stand in the presence of God and was sent to speak to yoʋ and bring yoʋ this good news.
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 But behold, yoʋ will be silent and unable to speak until the day that these things take place, because yoʋ did not believe my words, which will be fulfilled at their appointed time.”
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 Meanwhile, the people were waiting for Zechariah and wondering about his delay in the temple.
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 When he came out, he was unable to speak to them, and they perceived that he had seen a vision in the temple, because he kept making signs to them and remained unable to speak.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 When the days of his service had come to an end, he returned to his home.
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 After those days his wife Elizabeth conceived and kept herself in seclusion for five months, saying,
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 “The Lord has done this for me. In these days he has looked upon me with favor and taken away my reproach among the people.”
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 In the sixth month the angel Gabriel was sent by God to a town of Galilee called Nazareth,
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 to a virgin betrothed to a man named Joseph, of the house of David. The virgin's name was Mary.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 The angel came to her and said, “Greetings, O favored one, the Lord is with yoʋ! Blessed are yoʋ among women!”
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 But when Mary saw him, she was greatly perplexed by his statement and began wondering what sort of greeting this might be.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 Then the angel said to her, “Do not be afraid, Mary, for yoʋ have found favor with God.
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 And behold, yoʋ will conceive in yoʋr womb and give birth to a son, and yoʋ shall name him Jesus.
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 He will be great and will be called the Son of the Most High, and the Lord God will give him the throne of his father David.
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 He will reign over the house of Jacob forever, and of his kingdom there will be no end.” (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 Mary said to the angel, “How will this be, since I am a virgin?”
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 The angel answered her, “The Holy Spirit will come upon yoʋ, and the power of the Most High will overshadow yoʋ; therefore the holy child that is to be born will be called the Son of God.
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 And behold, yoʋr relative Elizabeth has also conceived a son in her old age, and this is the sixth month for her who was called barren.
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 For nothing is impossible with God.”
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 Then Mary said, “Behold, I am the servant of the Lord; may it happen to me according to yoʋr word.” And the angel went away from her.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 In those days Mary arose and went with haste to the hill country, to a town of Judah,
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 where she entered the house of Zechariah and greeted Elizabeth.
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 When Elizabeth heard Mary's greeting, the baby leaped in her womb, and Elizabeth was filled with the Holy Spirit.
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 Then she exclaimed with a loud voice, “Blessed are yoʋ among women, and blessed is the fruit of yoʋr womb!
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 How has this happened to me that the mother of my Lord should come to me?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 For behold, when the sound of yoʋr greeting came into my ears, the baby in my womb leaped for joy.
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 Blessed is she who has believed, for what the Lord has spoken to her will be fulfilled.”
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 Then Mary said, “My soul magnifies the Lord,
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 and my spirit rejoices in God my Savior,
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 because he has looked favorably on the humble state of his servant. For behold, from now on all generations will call me blessed,
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 because the Mighty One has done great things for me; holy is his name.
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 From generation to generation his mercy is upon those who fear him.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 He has done a mighty deed with his arm; he has scattered the proud in the thoughts of their hearts.
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 He has brought down rulers from their thrones and exalted the lowly.
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 He has filled the hungry with good things, but the rich he has sent away empty.
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 He has helped his servant Israel, remembering his mercy,
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 just as he spoke to our fathers, to Abraham and to his offspring forever.” (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 And Mary remained with Elizabeth for about three months and then returned to her house.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 Now the time was fulfilled for Elizabeth to give birth, and she bore a son.
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 Then her neighbors and her relatives heard that the Lord had magnified his mercy with her, and they rejoiced with her.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 On the eighth day they came to circumcise the child, and they were going to give him the name of his father Zechariah.
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 But the child's mother responded, “No! He is to be called John.”
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 But they said to her, “There is no one among yoʋr relatives who has that name.”
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 Then they began making signs to the child's father to find out what he wanted to name him.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 So he asked for a tablet and wrote, “His name is John.” And they were all amazed.
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 At once Zechariah's mouth was opened and his tongue was released, and he began to speak, blessing God.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 Then fear came upon all who dwelt around them, and in the entire hill country of Judea all these things were being discussed.
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 All who heard about this laid it up in their hearts, saying, “What then will this child become?” And the hand of the Lord was with him.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 Then Zechariah, the child's father, was filled with the Holy Spirit and prophesied:
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 “Blessed be the Lord, the God of Israel, for he has visited his people and brought them redemption.
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 He has raised up for us a horn of salvation in the house of his servant David
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 (just as he spoke through the mouth of his holy prophets long ago), (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 salvation from our enemies and from the hand of all who hate us—
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 to deal mercifully with our fathers and to remember his holy covenant,
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 the oath he swore to Abraham our father, to grant us
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 that we, having been rescued from the hands of our enemies, might serve him without fear,
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 in holiness and righteousness before him all the days of our lives.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 And yoʋ, child, will be called a prophet of the Most High, for yoʋ will go before the presence of the Lord to prepare his ways,
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 to give his people knowledge of salvation through the remission of their sins,
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 through the tender mercy of our God, by which the sunrise has visited us from on high,
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 to give light to those who sit in darkness and in the shadow of death, to guide our feet into the way of peace.”
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 And the child grew and became strong in spirit, and he was in the wilderness until the day of his public appearance to Israel.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< Luke 1 >