< Luke 8 >

1 And after these things Jesus travelled about the cities and the villages, and proclaimed and announced the kingdom of God. And with him were his twelve disciples,
Bayan wannan sai Yesu ya zazzaga gari da ƙauye, yana wa’azin bisharar mulkin Allah. Sha Biyun nan kuwa suna tare da shi,
2 and those women who were healed of infirmities and of unclean spirits, Mary called Magdalena, out of whom went seven demons,
da kuma waɗansu mata waɗanda aka warkar da su daga cututtukansu, da kuma mugayen ruhohi. Cikinsu akwai Maryamu (wadda ake kira Magdalin) wadda aljanu bakwai suka fito daga cikinta.
3 and Joanna the wife of Chusa, Herod's steward, and Susanna, and many others, who ministered to them of their property.
Da Yowanna matar Kuza, manajan iyalin Hiridus; da Suzana; da waɗansu mata da yawa. Waɗannan mata suna taimaka musu cikin hidima, daga cikin abin da suke da shi na zaman gari.
4 And when a great multitude was assembled, and people came to him from all the cities, he said, in similitudes:
Yayinda taron mai girma na taruwa, mutane kuma daga garuruwa dabam-dabam suna zuwa wurin Yesu, sai ya ba da wannan misali ya ce,
5 A sower went out to sow his seed: and as he sowed, some fell by the side of the path, and was trodden upon, and a bird devoured it.
“Wani manomi ya fita domin ya shuka irinsa. Da yana watsa irin, sai waɗansu suka fāɗi a kan hanya, aka tattaka su, tsuntsayen sararin sama kuma suka cinye su.
6 And other fell upon a rock, and sprung up forthwith; but, as it lacked moisture, it dried up.
Waɗansu suka fāɗi a kan dutse, da suka tsira sai suka yanƙwane don babu ruwa a wurin.
7 And other fell among thorns, and the thorns sprung up with it, and choked it.
Waɗansu kuma suka fāɗi a cikin ƙaya. Da suka yi girma tare, sai ƙayan suka shaƙe su.
8 And other fell on good and fair ground, and sprung up, and bore fruits, a hundred for one. Having said these things, he cried: He that hath ears to hear, let him hear.
Waɗansu kuma har yanzu, suka fāɗi a ƙasa mai kyau, suka yi girma, suka ba da amfani riɓi ɗari-ɗari, fiye da abin da aka shuka.” Da faɗin haka sai ya ce, “Duk mai kunnen ji, yă ji.”
9 And his disciples asked him: what meaneth this similitude?
Almajiransa suka tambaye shi ma’anar wannan misali.
10 And he said to them: To you it is given, to know the mysteries of the kingdom of God; but to others, it is spoken in allegories; that, while seeing, they may not see, and while hearing, may not understand.
Sai ya ce, “Ku ne aka ba sanin asirin mulkin Allah, amma ga sauran mutane kam, ina magana da misalai, saboda, “‘ko da yake suna kallo, ba za su gani ba, ko da yake suna ji, ba za su gane ba.’
11 But this is the similitude: The seed is the word of God.
“Ga ma’anar misalin, irin, shi ne maganar Allah.
12 And those by the side of the path, are they that hear the word, and the enemy cometh and taketh the word out of their heart, that they may not believe and live.
Waɗanda suka fāɗi a kan hanya su ne mutanen da suka ji, amma Iblis, yakan zo ya ɗauke maganar daga zuciyarsu, don kada su gaskata, su sami ceto.
13 And those upon the rock, are they who, when they hear, receive the word with joy: but they have no root in them, and their faith is temporary, and in time of temptation they are stumbled.
Na kan dutse kuwa, su ne da jin maganar, sukan karɓa da murna, amma ba su da saiwa. Sukan gaskata na ɗan lokaci, amma lokacin gwaji, sai su ja da baya.
14 And that which fell among thorns, are those who hear the word, but are choked by cares, and by riches, and by worldly desires, and bear no fruits.
Irin da suka fāɗi a cikin ƙaya kuwa, su ne mutanen da suka ji, amma a kwana a tashi, tunanin kayan duniya, da neman arziki, da son jin daɗi, sukan hana su ba da’ya’ya.
15 And that on good ground, are those who, with a humble and good heart, hear the word, and retain it, and with patience bring forth fruits.
Amma irin da suka fāɗi a ƙasa mai kyau kuwa, su ne mutane masu kyakkyawar zuciya, mai kyau, da suka ji, suka riƙe, suka kuma jimre har suka ba da’ya’ya.”
16 No one lighteth a lamp, and covereth it with a vessel, or placeth it under a bed, but setteth it upon a light-stand, that all who come in, may see the light of it.
“Ba mai ƙuna fitila sa’an nan ya ɓoye ta a cikin tulu, ko kuma ya sa ta a ƙarƙashin gado ba. A maimakon haka, yakan sa ta a kan wurin ajiye fitila, saboda mutane masu shigowa su ga haske.
17 For there is nothing covered, that shall not be uncovered; nor concealed, that shall not be known and become manifest.
Ba abin da yake ɓoye da ba za a fallasa ba. Kuma ba abin da yake rufe, da ba za a sani ba, ko a fitar da shi a fili ba.
18 Take heed how ye hear: for to him that hath, shall be given; and from him that hath not, shall be taken even what he thinketh he hath.
Saboda haka, ku yi tunani da kyau yadda kuke saurara. Duk wanda yake da shi, za a ƙara masa, duk wanda ba shi da shi kuma, abin da yake tsammani yana da shi ma, za a karɓe daga gare shi.”
19 And his mother and his brothers came to him, and they could not speak with him, because of the multitude.
Sai uwar Yesu da’yan’uwansa suka zo, domin su gan shi, amma ba su iya zuwa kusa da shi ba, saboda taron.
20 And they say to him: Thy mother and thy brothers stand without, and wish to see thee.
Sai wani ya faɗa masa cewa, “Ga uwarka da’yan’uwanka suna tsaye a waje suna so su gan ka.”
21 And he answered and said: My mother and my brothers, are they who hear the word of God, and do it.
Ya amsa ya ce, “Mahaifiyata da’yan’uwana, su ne waɗanda suke jin maganar Allah, suna kuma aikata ta.”
22 And on a certain day Jesus embarked and sat in a ship, he and his disciples. And he said to them; Let us pass over to the other side of the sea.
Wata rana Yesu ya ce wa almajiransa, “Mu haye zuwa wancan gefen tafkin.” Sai suka shiga jirgin ruwa suka fara tafiya.
23 And while they were rowing, Jesus fell asleep. And there was a tempest of wind on the sea; and the ship was near to sinking.
Da suna cikin tafiya, sai barci ya kwashe shi. Sai wata babban iska ta taso kan tafkin, har ruwa ya fara shiga cikin jirgin. Suka shiga babban hatsari.
24 And they came and awaked him, and said to him: Our Rabbi, our Rabbi, we are perishing! And he arose, and rebuked the winds and the agitations of the water; and they ceased, and there was a calm.
Almajiran suka je suka tashe shi daga barci, suka ce, “Ubangiji, Ubangiji, za mu nutse!” Ya tashi ya kwaɓe iskar da kuma haukar ruwan. Sai ruwan da iskar suka natsu. Kome ya yi tsit.
25 And he said to them: Where is your faith? And they being in awe, wondered, and said one to another: Who is this, that commandeth even the winds, and the waves, and the sea; and they obey him?
Sai ya tambayi almajiransa, “Ina bangaskiyarku?” A cikin tsoro da mamaki, suka ce wa junansu, “Wane ne wannan? Yana ba da umarni ga iska da ruwa ma, kuma suna biyayya da shi?”
26 And they rowed on, and came to the country of the Gadarenes, which lieth over against Galilee.
Suka shiga jirgin ruwa zuwa yankin Gerasenawa da yake a hayin tafkin, daga wajen Galili.
27 And when he went out upon the land, there, met him a man of the city, in whom had been a demon for a long time; and he wore no clothing, and did not reside in a house, but among the tombs.
Da Yesu ya sauka daga jirgin, sai ga wani mutum mai aljanu daga garin. Mutumin ya daɗe bai sa tufafi ba, kuma ba ya zama a gida. Yana zama a cikin kaburbura.
28 And when he saw Jesus, he cried out, and fell down before him, and said, with a loud voice: What have we to do with thee? Jesus, thou Son of the exalted God. I entreat of thee, torment me not.
Da ya ga Yesu, sai mutumin ya ɗaga murya da ƙarfi, ya fāɗi a gabansa, yana ihu cewa, “Ina ruwanka da ni, Yesu, Ɗan Allah Mafi Ɗaukaka? Ina roƙonka, kada ka ba ni wahala!”
29 For Jesus had commanded the unclean spirit, to come out of the man: for, of a long time he had been held captive by him; and he had been bound with chains, and held in fetters; but he had burst the bonds, and had been driven by the demon into the desert.
Gama Yesu ya riga ya umarci mugun ruhun ya fita daga mutumin. Sau da yawa mugun ruhun ya sha kamunsa. Ko da yake akan daure shi hannu da ƙafa, da sarƙa, a kuma yi gadinsa, amma yakan tsinke sarƙoƙinsa, aljanun kuma su kore shi zuwa wuraren kaɗaici, inda ba kowa.
30 And Jesus demanded of him: What is thy name? And he said to him: Legion: because many demons had entered into him.
Yesu ya tambaye shi, “Mene ne sunanka?” Sai ya amsa, “Tuli,” gama aljanu masu ɗumbun yawa ne suna cikinsa.
31 And they besought him, not to command them to depart into the abyss. (Abyssos g12)
Suka yi ta roƙonsa kada yă umarce su su shiga ramin Abis. (Abyssos g12)
32 And there was a herd of many swine grazing on the mountain. And they besought him, that he would permit them to enter the swine. And he permitted them.
A wurin kuwa, akwai babban garken aladu da suke kiwo a gefen tudu. Aljanun suka roƙi Yesu ya bar su, su shiga cikin aladun, ya kuwa yardar musu.
33 And the demons went out of the man, and entered the swine; and the whole herd ran to a precipice, and plunged into the sea, and were strangled.
Da aljanun suka fita daga cikin mutumin, sai suka shiga cikin aladun. Garken kuma ya gangara daga kan tudun zuwa cikin tafkin, kuma suka nutse.
34 And when the herdmen saw what had occurred, they fled, and told it in the cities and the villages.
Da masu kiwon aladun suka ga abin da ya faru, sai suka ruga da gudu zuwa garin da kewaye suka kai labari.
35 And the men went out to see what was done. And they came to Jesus, and found the man, out of whom the demons had gone, now clothed, and modest, and sitting at the feet of Jesus; and they were awed.
Mutanen kuma suka fito don su ga abin da ya faru. Da suka iso wurin Yesu, sai suka tarar da mutumin da aljanun suka fita daga cikinsa, yana zaune kusa da Yesu sanye da tufafi, kuma cikin hankalinsa, sai tsoro ya kama su.
36 And they that saw it, related to them in what manner the demoniac was cured.
Waɗanda suka ga abin da faru, suka gaya wa mutanen yadda aka warkar da mai aljanun.
37 And the whole throng of the Gadarenes requested him, that he would depart from them: for great fear had seized them. And Jesus embarked in a ship, and retired from among them.
Sai dukan mutanen yankin Gerasenawa suka roƙi Yesu ya bar su, don sun tsorata sosai. Sai Yesu ya shiga jirgin ruwa ya tafi.
38 And the man, from whom the demons had gone out, requested that he might remain with him. But Jesus dismissed him, and said to him:
Mutumin da aka fitar da aljanun daga cikinsa, ya roƙi Yesu don yă tafi tare da shi, amma Yesu ya sallame shi ya ce,
39 Return to thy home, and relate what God hath done for thee. And he went away, and proclaimed through all the city what Jesus had done for him.
“Koma gida, ka shaida babban alherin da Allah ya yi maka.” Sai mutumin ya tafi yana faɗin abin da Yesu ya yi masa a duk garin.
40 And when Jesus returned, a great multitude received him; for all were looking for him.
Da Yesu ya koma, taron suka marabce shi, don dā ma duk suna jiransa.
41 And a man, whose name was Jairus, a chief of the synagogue, fell down at the feet of Jesus, and besought him to enter his house;
Sai wani mutum mai suna Yayirus, wani mai mulkin majami’a, ya zo ya fāɗi a gaban Yesu, yana roƙonsa ya zo gidansa,
42 for he had an only daughter, about twelve years old, and she was near dying. And as Jesus went with him, a great multitude pressed upon him.
domin diyarsa ɗaya tak, wadda ta kai shekara goma sha biyu, tana bakin mutuwa. Da Yesu yake kan hanyarsa, taron mutane masu yawa suka yi ta matsa shi a kowane gefe.
43 And a certain woman, whose blood had flowed twelve years, and who had expended all her property among physicians, and could not be cured by any one,
A wurin kuwa, akwai wata mace wadda tana da ciwon zubar da jini, har na shekara goma sha biyu, amma babu wanda ya iya warkar da ita.
44 came up behind him, and touched the border of his garment; and immediately the flow of her blood stopped.
Sai ta zo ta bayansa, ta taɓa bakin rigarsa. Nan da nan, zubar da jininta ya tsaya.
45 And Jesus said: Who touched me? And when all denied, Simon Cephas and those with him said to him: Our Rabbi, crowds press upon thee and sayest thou, Who touched me?
Yesu ya yi tambaya, “Wa ya taɓa ni?” Bayan kowa ya yi musu, sai Bitrus ya ce, “Ubangiji, ai, mutane da yawa suna matsinka ta kowane gefe.”
46 And he said: Some one touched me; for I perceive, that energy hath gone out from me.
Amma Yesu ya ce, “Wani ya taɓa ni, na san cewa iko ya fita daga wurina.”
47 And the woman, when she saw that she had not escaped his notice, came trembling, and fell down and worshipped him. And in the presence of all the people, she declared for what cause she had touched him, and that she was instantly healed.
Sai macen, da ta ga ba halin ɓoyewa, sai ta fita, jikinta na rawa, ta fāɗi a gabansa. A gaban dukan mutanen, ta faɗi dalilin da ya sa ta taɓa shi, da yadda ta warke nan take.
48 And Jesus said to her: Take courage, my daughter: Thy faith hath given thee life: Go in peace.
Sai Yesu ya ce mata, “Diyata, bangaskiyarki ta warkar da ke. Ki sauka lafiya.”
49 And while he was speaking, one came from the house of the chief of the synagogue, and said to him: Thy daughter is dead; trouble not the teacher.
Yayinda Yesu na cikin magana har yanzu, sai ga wani daga gidan Yayirus, mai mulkin majami’ar ya ce, “Kada ka ƙara damun malam, diyarka ta rasu.”
50 And Jesus heard it, and said to the father of the maid: Fear not; believe only, and she will live.
Da Yesu ya ji wannan, sai ya ce wa Yayirus, “Kada ka ji tsoro, ka gaskata, za a kuma warkar da ita.”
51 And Jesus came to the house; and he suffered none to go in with him, except Simon, and James, and John, and the father and mother of the maid.
Da ya iso gidan Yayirus, sai ya hana kowa yă bi shi cikin ɗakin, sai dai Bitrus, da Yohanna, da Yaƙub, da kuma mahaifin da mahaifiyar.
52 And all were weeping and wailing over her. And Jesus said: Weep not; for she is not dead, but sleepeth
Ana cikin haka, dukan mutanen kuma sai kuka da makoki suke ta yi, domin yarinyar. Sai Yesu ya ce, “Ka daina yin kuka, ba tă mutu ba, tana barci ne.”
53 And they derided him, knowing that she was dead.
Sai suka yi masa dariya, da yake sun san cewa, ta mutu.
54 And he put every one out, and took her by the hand, and called, and said: Maid, arise.
Amma Yesu ya kama ta a hannu ya ce, “Diyata, tashi.”
55 And her spirit returned, and she instantly arose. And he directed them to give her food.
Ruhunta ya dawo, kuma ta tashi, nan take. Yesu ya ce musu, su ba ta wani abu tă ci.
56 And her parents were astonished: and he charged them to tell no one what had occurred.
Iyayenta suka yi mamaki, amma ya ba su umarni kada su faɗa wa kowa abin da ya faru.

< Luke 8 >