< Luke 5 >

1 AND it was while the assembly gathered upon him to hear the word of Aloha, he stood upon the bank of the sea of Genesar;
Wata rana, Yesu yana tsaye a bakin Tafkin Gennesaret, mutane kuma suna ta matsawa kewaye da shi, domin su ji maganar Allah,
2 and he saw two vessels standing by the sea-side, and the fishermen who had gone up from them, and were washing their nets.
sai ya hangi jiragen ruwa biyu a bakin tafkin, waɗanda masu kamun kifi suka bari suna wankin abin kamun kifinsu.
3 And one of them was of Shemun Kipha; and Jeshu ascended, sat in it, and directed that they should take it a little from the land into the waters; and he sat, and taught the multitudes from the vessel.
Sai ya shiga ɗaya jirgin ruwan da yake na Siman, ya kuma roƙe shi yă tura shi kaɗan daga gaci. Sai ya zauna a jirgin ruwan, ya koyar da mutane daga ciki.
4 And when he was silent from his discourses, he said to Shemun, Lead into the deep, and cast forth your nets for a draught.
Da ya gama magana, sai ya ce wa Siman, “Ka tuƙa jirgin zuwa inda akwai zurfi, ka saukar da abin kamun kifinka ka kama kifi.”
5 Shemun answered and said to him, Rabi, the whole night we have laboured and nothing have we taken; but at thy word I throw the net.
Siman ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, duk dare mun yi ta fama ba mu kama kome ba, amma tun da ka ce haka, zan saki abin kamun kifin.”
6 And when they had this done, they enclosed great multitudes of fishes, and their net brake.
Da suka yi haka, sai suka kama kifi da yawa, har abin kamun kifinsu suka fara tsintsinkewa.
7 And they signed to their companions, who were in another vessel, to come and help them. And when they had come, they filled those two vessels, so that they were nigh to be swallowed up.
Sai suka kira abokansu a ɗaya jirgin, su zo su taimake su, suka kuwa zo. Suka cika jiragen biyu da kifi cif, har jiragen suka fara nutsewa.
8 But when Shemun Kipha saw, he fell before the feet of Jeshu and said to him, I pray from thee, my Lord, remove thee from me, for I am a man a sinner.
Da Siman Bitrus ya ga wannan, sai ya fāɗi a gaban Yesu ya ce, “Rabu da ni, Ubangiji. Ni mai zunubi ne!”
9 For amazement had seized him, and all who were with him, on account of the draught of fishes which they had taken.
Gama mamaki ya kama shi da abokansa duka, saboda yawan kifin da suka kama.
10 Even so also Jacub and Juchanon, sons of Zabdai, who were partners of Shemun. But Jeshu said, Fear not, from henceforth the sons of men shalt thou catch unto life.
Yaƙub da Yohanna,’ya’yan Zebedi, abokan aikin Siman su ma suka yi mamaki. Sai Yesu ya ce wa Siman, “Kada ka ji tsoro, daga yanzu za ka riƙa kama mutane ne.”
11 And they brought the vessels to land, and forsook every thing, and went after him.
Sai suka jawo jiragen ruwansu zuwa gaci, suka bar kome da kome, suka bi shi.
12 AND when Jeshu was in one of the cities, there came a certain man who was wholly filled with leprosy; he saw Jeshu, and fell upon his face, and prayed of him, and said to him, My Lord, if thou art willing, thou canst make me clean.
Yayinda Yesu yake ɗaya daga cikin garuruwan nan, sai ga wani mutum wanda kuturta ta ci ƙarfinsa. Da ganin Yesu, sai ya fāɗi da fuskarsa a ƙasa, ya roƙe shi ya ce, “Ubangiji, in ka yarda, kana iya ka tsabtacce ni.”
13 And Jeshu extended his hand, touched him, and said to him, I am willing; be clean. And in an instant his leprosy went from him.
Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin ya ce, “Na yarda, ka zama da tsabta!” Nan da nan, sai kuturtar ta rabu da shi.
14 And he commanded him, Tell no man, but go show thyself to the priests, and offer the oblation for thy cleansing, as Musha ordained for their testimony.
Sai Yesu ya umarce shi ya ce, “Kada ka gaya wa kowa, amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, ka kuma miƙa hadayu da Musa ya umarta, saboda tsarkakewarka ta zama shaida a gare su.”
15 And the fame concerning him went forth the more, and much people were gathered together to hear him and to be healed from their diseases.
Duk da haka, labarinsa ya ƙara bazuwa sosai, har taron mutane suka dinga zuwa don jinsa, da kuma neman warkarwa daga cututtukansu.
16 And he passed away into the desert, and prayed.
Amma Yesu sau da yawa, yakan keɓe kansa zuwa wuraren da ba kowa, yă yi addu’a.
17 And it was on one of the days, while Jeshu was teaching, (certain) Pharishee and doctors of the law were sitting. And they had come from all the villages of Galila and of Jehud, and from Urishlem: and the power of the Lord was (there) to heal them.
Wata rana, da yake cikin koyarwa, waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki waɗanda suka zo daga kowane ƙauye a Galili, Yahudiya da Urushalima kuwa suna zaune. Ikon Ubangiji yana nan don yă warkar da masu ciwo.
18 And some brought on a couch a certain man a paralytic; and they sought to enter, that they might set him before him.
Sai ga waɗansu mutane suka kawo wani shanyayye a kan tabarma. Suka yi ƙoƙari su shigar da shi cikin gidan, domin su kwantar da shi a gaban Yesu.
19 And when they found not how to bring him in because of the multitude of people, they ascended to the house-top, and sent him with his couch from the roof into the midst before Jeshu.
Da suka ga babu hanyar da za su bi saboda taron, sai suka haura rufin, suka saukar da shi a kan tabarmarsa, ta bakin ramin da suka huda a rufin, suka ajiye shi a tsakiyar taron, a gaban Yesu.
20 And when Jeshu saw their faith, he said to the paralytic, Man, forgiven to thee are thy sins.
Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce, “Saurayi, an gafarta maka zunubanka.”
21 And the Sophree and Pharishee began to reason and to say, Who is this who speaketh blasphemy? Who can forgive sins but Aloha only?
Farisiyawa da malaman dokoki suka fara yin tunani a zukatansu, “Wane ne wannan mutum da yake saɓo haka? Wa zai iya gafarta zunubai, in ba Allah kaɗai ba?”
22 But Jeshu knew their reasoning, and said to them, What reason you in your hearts?
Yesu ya san abin da suke tunani, sai ya yi tambaya ya ce, “Don me kuke tunanin waɗannan abubuwa a zukatanku?
23 Which is easier, to say, Forgiven to thee are thy sins; or to say, Arise, walk?
Wanne ya fi sauƙi, a ce, ‘An gafarta maka zunubanka,’ ko kuma a ce, ‘Tashi, ka yi tafiya’?
24 But that you may know that authority hath the Son of man in the earth to forgive sins, -he saith to the paralytic, -To thee I say, Arise, take up thy couch, and go to thine house.
Amma domin ku san cewa Ɗan Mutum yana da iko a duniya ya gafarta zunubai.” Sai ya ce wa shanyayyen, “Na ce maka, tashi, ɗauki tabarmarka ka tafi gida.”
25 And immediately he arose before them, and took up his couch, and went to his house, glorifying Aloha.
Nan da nan, ya tashi tsaye a gabansu, ya ɗauki tabarmar da yake kwance a kai, ya tafi gida, yana yabon Allah.
26 And amazement held every man; and they glorified Aloha, and were filled with fear, saying, We have seen today wonders.
Kowa ya yi mamaki, ya kuma yabi Allah. Suka cika da tsoro, suna cewa, “Mun ga abubuwan banmamaki yau.”
27 After these things Jeshu went forth, and saw a tribute-taker, whose name was Levi, sitting at the house of tribute. And he said to him, Come after me:
Bayan wannan, sai Yesu ya fita, ya ga wani mai karɓar haraji, mai suna Lawi, yana zaune a wurin da ake karɓar haraji. Yesu ya ce masa, “Bi ni.”
28 and he left every thing, and arose, and went after him.
Sai Lawi ya tashi, ya bar kome da kome, ya bi shi.
29 And Levi made in his house a great feast; and there was a large company of tribute-takers, and of others that reclined with them.
Sai Lawi ya shirya wa Yesu wani babban liyafa a gidansa. Wani babban taron na masu karɓar haraji, tare da waɗansu suna cin abinci tare da su.
30 And the Sophree and Pharishee murmured, saying to his disciples, Why with tribute-takers and sinners eat you and drink?
Amma Farisiyawa da malaman dokokin da suke a ƙungiyarsu, suka yi wa almajiransa gunaguni, suna cewa, “Don me kuke ci, kuke sha tare da masu karɓar haraji da masu zunubi?”
31 Jeshu answered and said to them, The whole do not require the physician, but they who are grievously ill.
Yesu ya amsa musu ya ce, “Ai, masu lafiya ba sa bukatar likita, sai dai marasa lafiya.
32 I am not come to call the just, but the sinners, to repentance.
Ban zo don in kira masu adalci ba, sai dai masu zunubi zuwa ga tuba.”
33 But they say to him, Why do the disciples of Juchanon constantly fast, and pray also as the Pharishee, but thine eat and drink?
Suka ce masa, “Almajiran Yohanna sukan yi azumi da addu’a, haka ma almajiran Farisiyawa, amma naka sai ci da sha.”
34 But he said to them, How can you make the sons of the chamber fast, while the bridegroom is with them?
Yesu ya amsa ya ce, “Za ku iya sa abokan ango yin azumi yayinda yake tare da su?
35 But the days will come when the bridegroom will be taken up from them: then shall they fast in those days.
Amma lokaci yana zuwa, da za a ɗauke ango daga gare su. A waɗancan kwanakin ne za su yi azumi.”
36 He spake to them a parable: No man cutteth a piece from a new material, and fasteneth it upon an old garment; lest he rend the new, without completing the old with the piece that is new.
Sai ya faɗa musu wannan misali ya ce, “Ba wanda yakan yage ƙyalle daga sabuwar riga ya yi wa tsohuwar riga faci. In ya yi haka, zai yage sabuwar rigar, kuma facin daga sabuwar ba zai dace da tsohuwar rigar ba.
37 And no man poureth new wine into old bottles; lest the new wine burst forth, and the wine be shed, and the bottles perish.
Kuma ba wanda yakan zuba sabon ruwan inabi a cikin tsofaffin salkuna. In ya yi haka, sabon ruwan inabi zai farfashe salkunan, ruwan inabin yă zube, salkunan kuma su lalace.
38 But they pour new wine into new bottles, and both are preserved.
A’a, sai dai a zuba sabon ruwan inabi a sababbin salkuna.
39 And no man, drinking old wine, immediately asketh new: for he saith, The old is softer.
Kuma ba wanda yakan so shan sabon ruwan inabi bayan ya sha tsohon, don yakan ce, ‘Ai, tsohon ya fi kyau.’”

< Luke 5 >