< Luke 1 >

1 BECAUSE many have willed to record histories of those transactions of which we are persuaded, according to that which they have delivered to us,
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 (they) who from the first were eye-witnesses and ministers of his doctrine;
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 it appeared also to me, that having been intimately near to them all, I should record every thing in its order for thee, illustrious Theophile,
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 that thou mayest know the truth of those doctrines in which thou hast been instructed.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 THERE was in the days of Herodes, king of the Jihudoyee, a certain priest whose name was Zakaria, of the service of the house of Abia, and his wife (was) of the daughters of Aharun; her name was Elishaba.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 And they were both just before Aloha, and walked in all his commandments, and in the righteousness of the Lord, without blame.
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 But they had no son because Elishaba was barren, and both had become many in their days.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 But it was while he was acting-as-priest in the order of his ministry before Aloha,
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 according to the custom of the priesthood he came to set on incense, and entered into the temple of the Lord.
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 And all the congregation of the people were praying without at the time of incense.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 And there appeared to him, to Zakaria, the angel of the Lord, standing on the right hand of the altar of incense.
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 And Zakaria trembled when he saw him, and fear fell upon him.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 And the angel said to him, Fear not, Zakaria, for thy prayer is heard, and thy wife Elishaba shall bear thee a son, and thou shalt call his name Juchanon.
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 And to thee shall be joy and exultation, and many shall rejoice in his birth:
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 for he shall be great before the Lord, and wine and strong liquor shall he not drink, and with the Spirit of Holiness shall he be filled, from the womb of his mother.
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 And many of the sons of Isroel shall he convert to the Lord their Aloha.
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 And he shall go before him in the spirit and the power of Elia the prophet, to turn the hearts of the fathers unto the children, and those who believe not to the knowledge of the righteous, and to prepare for the Lord a perfect people.
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 And Zakaria said to the angel, How shall I know this? for I am old, and my wife many in her days.
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 And the angel answered and said to him, I am Gabriel, I stand before Aloha, and I have been sent to speak with thee and to announce to thee these things.
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 From henceforth thou shalt be dumb, and shalt not be able to speak, till the day when these things shall be done, because thou hast not believed these words, which shall be fulfilled in their time.
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 But the people were standing, and expecting Zakaria. and were wondering at his delay in the temple.
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 But when Zakaria had come forth, he could not speak to them; and he made them understand that he had seen a vision in the temple, and signing he signed to them, and remained dumb.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 And when the days of his service were fulfilled, he came to his house.
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 And it was after those days Elishaba his wife conceived, and she secluded herself five months.
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 And she said, These things hath the Lord done for me in the days of my desolation, to take away my reproach from among the children of men.
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 BUT in the sixth month Gabriel the angel was sent from before Aloha to Galila, to a city whose name (is) Natsrath,
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 unto a Virgin espoused to a man whose name was Jauseph, of the house of David, and the name of the Virgin was Mariam.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 And the angel entered to her, and said to her, Peace to thee, full of grace! our Lord is with thee, thou blessed among women!
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 But she, when she saw, was troubled at his words, and reasoned what this salutation was.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 And the angel said to her, Fear not, Mariam, for thou hast found favour with Aloha.
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 For, behold, thou shalt conceive, and shalt bring forth a son, and thou shalt call his name Jeshu.
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 He will be great, and the Son of the Most High shall he be called, and Aloha the Lord shall give unto him the throne of David his father.
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 And he shall reign over the house of Jakub for ever, and of his kingdom there shall be no end. (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 And Mariam said to the angel, How shall this be, because a man is not known to me?
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 The angel answered and said to her, The Spirit of Holiness shall come, and the Power of the Most High shall shadow over thee; on account of this He who (shall be) born from thee is the Holy, and the Son of Aloha shall be called.
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 And behold, Elishaba thy kinswoman, she also beareth a son in her old age, and this is the sixth month to her, -to her who is called the barren.
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 For nothing is difficult to Aloha.
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 And Mariam said, Behold, I am the handmaid of the Lord, be it unto me as thou hast said. And the angel went from her.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 AND Mariam arose in those days, and went with haste to the mountain to a city of Jehud;
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 and she entered into the house of Zakaria, and saluted Elishaba.
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 And it was that when Elishaba heard the salutation of Mariam, the infant leaped in her womb. And she was filled with the Spirit of Holiness;
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 and she cried with a loud voice, and said unto Mariam, Blessed art thou among women, And blessed is the fruit of thy womb!
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 Whence unto me is this, That the mother of my Lord should come to me?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 For, lo, as fell the voice of thy salutation on my ears, For great Joy leaped the infant in my womb.
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 And happy is she who hath believed, For there is a fulfilment of those things which have been spoken to her from the Lord.
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 And Mariam said: My soul doth magnify the Lord,
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 And my spirit rejoiceth in Aloha my Saviour,
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 Who hath looked upon the lowliness of his handmaid: For, behold, from now all generations shall give blessedness to me.
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 Because he hath done for me great things, he who is mighty, And holy is his name.
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 And his grace is for ages and generations Upon those who fear him.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 He hath wrought victory with his arm; He hath scattered the proud in the thoughts of their hearts.
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 He hath overturned the mighty from their thrones, And hath exalted the humble.
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 The hungry he hath satisfied with good things, And the rich he hath sent away empty.
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 He hath helped Isroel his servant, And hath remembered his mercy;
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 As he spake with our fathers, With Abraham and with his seed for ever. (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 And Mariam stayed with Elishaba three months, and returned to her house.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 BUT to Elishaba had come the time that she should give birth, and she gave birth to a son.
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 And her neighbours and the sons of her family heard that Aloha had magnified his grace upon her; and they rejoiced with her.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 And it was the eighth day, and they came to circumcise the child; and they called him by the name of his father, Zakaria.
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 And his mother answered and said to them, Not so; but he shall be called Juchanon.
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 And they said to her, No man in thy kindred is called by this name.
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 And they signed to his father (to show) how he willed they should call him.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 And he requested a tablet, and wrote, and said, Juchanan is his name. And every man wondered.
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 And immediately his mouth and his tongue were opened, and he spake, and blessed Aloha.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 And there was fear upon all around them; and in all the hill country of Jehud were these things spoken.
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 And all who heard reasoned in their hearts, and said, What is this child to be? And the hand of the Lord was with him.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 And Zakaria his father was filled with the Spirit of Holiness, and he prophesied, and said:
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 Blessed be the Lord, the Aloha of Israel; For he hath visited his people, and wrought for him redemption,
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 And hath raised up for us the horn of redemption In the house of David his servant;
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 As he spake by the mouth of his holy prophets, Who have been from of old, (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 That we should be delivered from our adversaries, And from the hand of all who hate us;
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 To perform his grace with our fathers, And to remember his holy covenant;
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 The oath which he sware to Abraham our father, -
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 That to us he would grant That, being delivered from the hand of our adversaries, Without fear we might serve before him
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 All our days in righteousness.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 And thou, child, the Prophet of the Most High Shalt thou be called; For thou shalt go before the face of the Lord, And thou shalt prepare his way;
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 To give the knowledge of salvation to his people In the forgiveness of their sins,
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 Through the compassions of the grace of our Aloha; Whereby the morn-splendour shall visit us from on high,
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 To illumine those who sit in darkness and the shadow of death. And to direct our feet into the way of peace.
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 And the child grew, and was strong in the spirit, and was in the desert till the day of his manifestation unto Isroel.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< Luke 1 >