< 2 Kings 6 >

1 and to say son: child [the] prophet to(wards) Elisha behold please [the] place which we to dwell there to/for face your narrow from us
Sai ƙungiyar annabawa suka ce wa Elisha, “Duba, wurin da muke taruwa ya kāsa mana.
2 to go: went please till [the] Jordan and to take: take from there man: anyone beam one and to make to/for us there place to/for to dwell there and to say to go: went
Bari mu je Urdun, inda kowannenmu zai saro itace; mu gina inda za mu zauna.” Sai ya ce musu, “Ku je.”
3 and to say [the] one be willing please and to go: went with servant/slave your and to say I to go: went
Sai ɗayansu ya ce, “Ba za ka zo tare da bayinka ba?” Sai Elisha ya ce “Zan zo.”
4 and to go: went with them and to come (in): come [the] Jordan [to] and to cut [the] tree
Ya kuma tafi tare da su. Suka tafi Urdun suka fara saran itatuwa.
5 and to be [the] one to fall: fell(trees) [the] beam and [obj] [the] iron to fall: fell(trees) to(wards) [the] water and to cry and to say alas! lord my and he/she/it to ask
Yayinda ɗayansu yake cikin saran itace, sai kan gatarin ya fāɗi a ruwa, sai ya ce, “Kash, ranka yă daɗe, kayan aro ne fa!”
6 and to say man [the] God where? to fall: fall and to see: see him [obj] [the] place and to shear tree: stick and to throw there [to] and to flow [the] iron
Sai mutumin Allah ya ce, “Daidai ina ya fāɗa?” Da ya nuna masa wurin, sai Elisha ya yanka ɗan sanda ya jefa a wurin, ya sa kan gatarin ya taso sama.
7 and to say to exalt to/for you and to send: reach hand his and to take: take him
Sai ya ce masa, “Ka ɗauko.” Sai mutumin ya miƙa hannu ya ɗauka.
8 and king Syria to be to fight in/on/with Israel and to advise to(wards) servant/slave his to/for to say to(wards) place someone someone encampment my
To, fa, sarkin Aram yana yaƙi da Isra’ila. Bayan ya tattauna da hafsoshinsa, sai ya ce, “Zan kafa sansanina a wurin kaza da kaza.”
9 and to send: depart man [the] God to(wards) king Israel to/for to say to keep: careful from to pass [the] place [the] this for there Syria descended
Sai mutumin Allah ya aika wa sarkin Isra’ila cewa, “Ka yi hankali da wuce wuri kaza, domin Arameyawa za su gangara can.”
10 and to send: depart king Israel to(wards) [the] place which to say to/for him man [the] God (and to warn him *QK) and to keep: guard there not one and not two
Saboda haka sarkin Isra’ila ya lura da inda mutumin Allah ya ambata. Sau da sau Elisha yakan yi wa sarki kashedi, don haka ya riƙa taka yi tsantsan a wuraren nan.
11 and to rage heart king Syria upon [the] word: because [the] this and to call: call to to(wards) servant/slave his and to say to(wards) them not to tell to/for me who? from which/that to/for us to(wards) king Israel
Wannan ya husata sarkin Aram. Ya kira hafsoshinsa ya tambaye su ya ce, “Ku faɗa mini, wane ne a cikinmu yake gefen sarkin Isra’ila?”
12 and to say one from servant/slave his not lord my [the] king for Elisha [the] prophet which in/on/with Israel to tell to/for king Israel [obj] [the] word which to speak: speak in/on/with chamber bed your
Sai ɗaya daga cikin hafsoshinsa ya ce, “Babu waninmu, ranka yă daɗe; Elisha, annabin da yake a Isra’ila ne, yake faɗa wa sarkin Isra’ila dukan zancen da ka yi a ɗakinka.”
13 and to say to go: went and to see: see where? he/she/it and to send: depart and to take: take him and to tell to/for him to/for to say behold in/on/with Dothan
Sai sarki ya ba da umarni ya ce, “Ku je ku tabbatar da inda yake don in aika mutane a kamo shi.” Sai ya sami rahoto cewa, “Yana a Dotan.”
14 and to send: depart there [to] horse and chariot and strength: soldiers heavy and to come (in): come night and to surround upon [the] city
Sai ya aika da dawakai da kekunan yaƙi da babban rukunin soja zuwa can. Suka bi dare, suka kewaye birnin.
15 and to rise to minister man [the] God to/for to arise: rise and to come out: come and behold strength: soldiers to turn: surround [obj] [the] city and horse and chariot and to say youth his to(wards) him alas! lord my how? to make: do
Sa’ad da bawan mutumin Allah ya farka ya kuma fita kashegari da sassafe, sai ga mayaƙa tare da dawakai da kekunan yaƙi sun kewaye birni. Sai bawan ya ce, “Ranka yă daɗe! Me za mu yi?”
16 and to say not to fear for many which with us from whence with them
Sai annabin ya ce, “Kada ka ji tsoro, waɗanda suke tare da mu sun fi waɗanda suke tare da su.”
17 and to pray Elisha and to say LORD to open please [obj] eye his and to see: see and to open LORD [obj] eye [the] youth and to see: see and behold [the] mountain: mount to fill horse and chariot fire around Elisha
Sa’an nan Elisha ya yi addu’a ya ce, “Ya Ubangiji, ka buɗe idanunsa yă gani!” Sai Ubangiji ya buɗe idanun bawan, ya duba, ya ga tuddai cike da dawakai da keken yaƙin wuta kewaye da Elisha.
18 and to go down to(wards) him and to pray Elisha to(wards) LORD and to say to smite please [obj] [the] nation [the] this in/on/with blindness and to smite them in/on/with blindness like/as word Elisha
Yayinda abokan gāba suka gangaro wajensa, sai Elisha ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce, “Ka sa mutanen nan su zama makafi.” Sai Ubangiji ya buge su da makanta kamar yadda Elisha ya roƙa.
19 and to say to(wards) them Elisha not this [the] way: road and not this [the] city to go: follow after me and to go: take [obj] you to(wards) [the] man which to seek [emph?] and to go: take [obj] them Samaria [to]
Elisha ya ce musu, “Wannan ba ita ce hanyar ba, ba kuma gari ke nan ba, ku bi ni, zan kuwa kai ku wurin mutumin da kuke nema!” Sai ya kai su Samariya.
20 and to be like/as to come (in): come they Samaria and to say Elisha LORD to open [obj] eye these and to see: see and to open LORD [obj] eye their and to see: see and behold in/on/with midst Samaria
Bayan suka shiga birnin, sai Elisha ya ce, “Ubangiji, ka buɗe idanun mutanen nan don su gani.” Sa’an nan Ubangiji ya buɗe idanunsu suka ga kansu a tsakiyar Samariya.
21 and to say king Israel to(wards) Elisha like/as to see: see he [obj] them to smite to smite father my
Da sarkin Isra’ila ya gan su, sai ya tambayi Elisha ya ce, “In kashe su ne, mahaifina? In kashe su?”
22 and to say not to smite which to take captive in/on/with sword your and in/on/with bow your you(m. s.) to smite to set: make food: bread and water to/for face: before their and to eat and to drink and to go: went to(wards) lord their
Elisha ya ce, “Kada ka kashe su. Za ka kashe mutanen da ka kame da takobi ko bakanka? Ka ba su abinci da ruwa su ci, su sha, sa’an nan su koma wurin maigidansu.”
23 and to feed to/for them feast great: large and to eat and to drink and to send: depart them and to go: went to(wards) lord their and not to add: again still band Syria to/for to come (in): come in/on/with land: country/planet Israel
Saboda haka aka shirya musu babban liyafa, bayan sun ci, suka kuma sha, sai ya tura su zuwa wurin maigidansu. Ta haka’yan harin Aram suka daina kai hari a yankin Isra’ila.
24 and to be after so and to gather Ben-hadad Ben-hadad king Syria [obj] all camp his and to ascend: rise and to confine upon Samaria
Bayan wani lokaci, Ben-Hadad sarkin Aram ya tattara dukan rundunarsa, ya je ya kewaye Samariya da yaƙi.
25 and to be famine great: large in/on/with Samaria and behold to confine upon her till to be head donkey in/on/with eighty silver: money and fourth [the] kab (quano *QK) in/on/with five silver: money
Aka yi babban yunwa a cikin birnin. Saboda daɗewar wannan kewayewar da aka yi wa birnin, sai yunwa ta ɓarke a birnin, har ana sayar da kan jaki a kan shekel tamanin, kashin kurciya kuma a kan shekel biyar.
26 and to be king Israel to pass upon [the] wall and woman to cry to(wards) him to/for to say to save [emph?] lord my [the] king
Yayinda sarkin Isra’ila yake wucewa kusa da katanga, sai wata mace ta yi masa kuka ta ce, “Ka taimake ni, ranka yă daɗe, sarki!”
27 and to say not to save you LORD from where? to save you from [the] threshing floor or from [the] wine
Sai sarki ya amsa ya ce, “In Ubangiji bai taimake ki ba, me zan iya yi? Ina da hatsi ko ruwan inabin da zan ba ki ne?”
28 and to say to/for her [the] king what? to/for you and to say [the] woman [the] this to say to(wards) me to give: give [obj] son: child your and to eat him [the] day and [obj] son: child my to eat tomorrow
Sa’an nan ya tambaye ta ya ce, “Me ya faru?” Sai ta amsa ta ce, “Wannan mace ta ce mini, ‘Kawo ɗanki mu ci yau, gobe kuwa mu ci ɗana.’
29 and to boil [obj] son: child my and to eat him and to say to(wards) her in/on/with day [the] another to give: give [obj] son: child your and to eat him and to hide [obj] son: child her
Saboda haka muka dafa ɗana muka ci. Kashegari na ce mata, ‘Kawo ɗanki mu ci,’ amma ta ɓoye shi.”
30 and to be like/as to hear: hear [the] king [obj] word [the] woman and to tear [obj] garment his and he/she/it to pass upon [the] wall and to see: see [the] people and behold [the] sackcloth upon flesh his from house: inside
Da sarki ya ji maganar macen sai ya yage rigunansa. Sa’ad da sarki yake wucewa a kan katangar birnin, sai mutane suka gan yana saye da rigar makoki a ciki.
31 and to say thus to make: do to/for me God and thus to add if to stand: stand head Elisha son: child Shaphat upon him [the] day: today
Ya ce, “Bari Allah yă yi mini hukunci mai tsanani har ma fiye da haka, idan ban cire kan Elisha ɗan Shafat yau ba!”
32 and Elisha to dwell in/on/with house: home his and [the] old: elder to dwell with him and to send: depart man from to/for face: before his in/on/with before to come (in): come [the] messenger to(wards) him and he/she/it to say to(wards) [the] old: elder to see: behold! for to send: depart son: warrior [the] to murder [the] this to/for to turn aside: remove [obj] head my to see: behold! like/as to come (in): come [the] messenger to shut [the] door and to oppress [obj] him in/on/with door not voice: sound foot lord his after him
To, Elisha yana zaune a cikin gidansa, dattawa kuwa suna zaune tare da shi. Sai sarki ya aiki ɗan aika yă ci gaba, amma kafin ɗan aikan yă isa, Elisha ya ce wa dattawan, “Kun gani ko? Wannan mai kisa ya aiko a cire mini kai! To, idan ɗan aikan ya iso, sai ku rufe ƙofar da ƙarfi, ku bar shi a waje. Ba da jimawa ba, maigidansa zai bi bayansa?”
33 still he to speak: speak with them and behold [the] messenger to go down to(wards) him and to say behold this [the] distress: harm from with LORD what? to wait: wait to/for LORD still
Yana magana da su ke nan, sai ga ɗan aikan ya gangaro wajensa. Sarki kuma ya ce, “Wannan bala’in daga wurin Ubangiji ya fito. Don me zan sa zuciya ga Ubangiji kuma?”

< 2 Kings 6 >