< 2 Chronicles 20 >

1 and to be after so to come (in): come son: descendant/people Moab and son: descendant/people Ammon and with them from [the] Meunite upon Jehoshaphat to/for battle
Bayan wannan, Mowabawa da Ammonawa tare da waɗansu Meyunawa suka zo su yaƙi Yehoshafat.
2 and to come (in): come and to tell to/for Jehoshaphat to/for to say to come (in): come upon you crowd many from side: beyond to/for sea from Edom and behold they in/on/with Hazazon-tamar Hazazon-tamar he/she/it Engedi Engedi
Sai waɗansu mutane suka zo suka faɗa wa Yehoshafat, “Ga babban runduna tana zuwa a kanka daga Edom, daga ƙetaren Teku, daga Aram. Ta ma kai Hazazon Tamar” (wato, En Gedi).
3 and to fear and to give: put Jehoshaphat [obj] face his to/for to seek to/for LORD and to call: call out fast upon all Judah
A firgice, Yehoshafat ya yanke shawara yă nemi nufin Ubangiji, ya kuma yi shelar azumi a dukan Yahuda.
4 and to gather Judah to/for to seek from LORD also from all city Judah to come (in): come to/for to seek [obj] LORD
Mutanen Yahuda suka taru gaba ɗaya don su nemi taimako daga wurin Ubangiji, tabbatacce suka fito daga kowane garin Yahuda don su neme shi.
5 and to stand: stand Jehoshaphat in/on/with assembly Judah and Jerusalem in/on/with house: temple LORD to/for face: before [the] court [the] new
Sa’an nan Yehoshafat ya miƙe tsaye a taron Yahuda da Urushalima a haikalin Ubangiji a sabon filin
6 and to say LORD God father our not you(m. s.) he/she/it God in/on/with heaven and you(m. s.) to rule in/on/with all kingdom [the] nation and in/on/with hand: power your strength and might and nothing with you to/for to stand
ya ce, “Ya Ubangiji Allah na kakanninmu, ba kai ne Allah wanda yake sama ba? Kana mulki a bisa dukan mulkokin ƙasashe. Iko da girma suna a hannunka, kuma ba wanda zai iya tsayayya da kai.
7 not you(m. s.) God our to possess: take [obj] to dwell [the] land: country/planet [the] this from to/for face: before people your Israel and to give: give her to/for seed: children Abraham to love: friend you to/for forever: enduring
Ya Allahnmu, ba kai ba ne ka kore mazaunan wannan ƙasa a gaban mutanenka Isra’ila ka kuma ba da ita har abada ga zuriyar Ibrahim abokinka?
8 and to dwell in/on/with her and to build to/for you in/on/with her sanctuary to/for name your to/for to say
Sun yi zama a cikinta suka kuma yi gina wuri mai tsarki a cikinta domin Sunanka cewa,
9 if to come (in): come upon us distress: harm sword judgment and pestilence and famine to stand: stand to/for face: before [the] house: home [the] this and to/for face: before your for name your in/on/with house: home [the] this and to cry out to(wards) you from distress our and to hear: hear and to save
‘In masifa ta zo mana, ko takobin hukunci, ko annoba ko yunwa, za mu tsaya a gabanka a gaban wannan haikalin da yake ɗauke da Sunanka, mu kuma yi kuka gare ka cikin azaba, za ka kuwa ji mu, ka cece mu.’
10 and now behold son: descendant/people Ammon and Moab and mountain: mount (Mount) Seir which not to give: allow to/for Israel to/for to come (in): come in/on/with them in/on/with to come (in): come they from land: country/planet Egypt for to turn aside: turn aside from upon them and not to destroy them
“Yanzu kuma ga mutanen Ammon, da na Mowab, da na Dutsen Seyir, waɗanda ka hana Isra’ilawa su kai musu yaƙi sa’ad da suka fito daga ƙasar Masar, su ne mutanen da Isra’ila suka ƙyale, ba su hallaka su ba.
11 and behold they(masc.) to wean upon us to/for to come (in): come to/for to drive out: drive out us from possession your which to possess: possess us
Yau ga yadda suke so su biya mu. Su suke so su kore mu daga ƙasar da ka ba mu gādo.
12 God our not to judge in/on/with them for nothing in/on/with us strength to/for face: before [the] crowd [the] many [the] this [the] to come (in): come upon us and we not to know what? to make: do for upon you eye our
Ya Allahnmu, ba za ka hukunta su ba? Gama ba mu da ƙarfin fuskantar wannan babbar rundunar da take so ta yaƙe mu. Ba mu san abin da za mu yi ba, mu dai mun zuba maka ido.”
13 and all Judah to stand: stand to/for face: before LORD also child their woman: wife their and son: child their
Dukan mazan Yahuda, tare da matansu da yaransu da ƙananansu, suka tsaya a gaban Ubangiji.
14 and Jahaziel son: descendant/people Zechariah son: descendant/people Benaiah son: descendant/people Jeiel son: descendant/people Mattaniah [the] Levi from son: descendant/people Asaph to be upon him spirit LORD in/on/with midst [the] assembly
Sa’an nan Ruhun Ubangiji ya sauko a kan Yahaziyel ɗan Zakariya, ɗan Benahiya, ɗan Yehiyel, ɗan Mattaniya, wani Balawe kuma zuriyar Asaf, yayinda yake tsaye a cikin taron.
15 and to say to listen all Judah and to dwell Jerusalem and [the] king Jehoshaphat thus to say LORD to/for you you(m. p.) not to fear and not to to be dismayed from face: because [the] crowd [the] many [the] this for not to/for you [the] battle for to/for God
Ya ce, “Saurara, Sarki Yehoshafat da dukan waɗanda suke zama a Yahuda da Urushalima! Ga abin da Ubangiji ya ce muku, ‘Kada ku ji tsoro ko ku fid da zuciya saboda wannan babbar runduna. Gama yaƙin ba naku ba ne, amma na Allah.
16 tomorrow to go down upon them look! they to ascend: rise in/on/with ascent [the] Ziz and to find [obj] them in/on/with end [the] torrent: valley face: east wilderness Jeruel
Gobe ku fito ku gangara ku yaƙe su. Za su yi ta haurawa ta Mashigin Ziz, ku kuwa za ku same su a ƙarshen kwari a Hamadan Yeruwel.
17 not to/for you to/for to fight in/on/with this to stand to stand: stand and to see: see [obj] salvation LORD with you Judah and Jerusalem not to fear and not to to be dismayed tomorrow to come out: come to/for face: before their and LORD with you
Ba lalle ba ne ku yi wannan yaƙi. Ku dai, ku ja dāgā, ku tsaya kurum ku ga nasarar da Ubangiji zai ba ku, ya Yahuda da Urushalima. Kada ku ji tsoro; kada ku karai. Ku fito don ku fuskance su gobe, Ubangiji kuwa zai kasance tare ku.’”
18 and to bow Jehoshaphat face land: soil [to] and all Judah and to dwell Jerusalem to fall: fall to/for face: before LORD to/for to bow to/for LORD
Yehoshafat ya rusuna da fuskarsa har ƙasa, dukan mutanen Yahuda da Urushalima suka fāɗi rubda ciki suka yi sujada a gaban Ubangiji.
19 and to arise: rise [the] Levi from son: descendant/people [the] Kohathite and from son: descendant/people [the] Korahite to/for to boast: praise to/for LORD God Israel in/on/with voice great: large to/for above [to]
Sa’an nan waɗansu Lawiyawa daga Kohatawa da Korayawa suka tashi tsaye suka yabe Ubangiji, Allah na Isra’ila, da babbar murya sosai.
20 and to rise in/on/with morning and to come out: come to/for wilderness Tekoa and in/on/with to come out: come they to stand: stand Jehoshaphat and to say to hear: hear me Judah and to dwell Jerusalem be faithful in/on/with LORD God your and be faithful be faithful in/on/with prophet his and to prosper
Da sassafe suka tashi suka nufi Hamadan Tekowa. Yayinda suka kama hanya, Yehoshafat ya tsaya ya ce, “Ku saurare ni, Yahuda da mutanen Urushalima! Ku amince da Ubangiji Allahnku za a kuwa kafa ku; ku amince da annabawansa za ku kuwa yi nasara.”
21 and to advise to(wards) [the] people and to stand: appoint to sing to/for LORD and to boast: praise to/for adornment holiness in/on/with to come out: come to/for face: before [the] to arm and to say to give thanks to/for LORD for to/for forever: enduring kindness his
Bayan suka yi shawara tare da shugabanni, sai ya zaɓi mutanen da za su ja gaban sojoji suna waƙa ga Ubangiji suna yabonsa saboda tsarkinsa suna cewa, “Ku yi godiya ga Ubangiji, gama ƙaunarsa dawwammamiya ce har abada.”
22 and in/on/with time to profane/begin: begin in/on/with cry and praise to give: put LORD to ambush upon son: descendant/people Ammon Moab and mountain: mount (Mount) Seir [the] to come (in): come to/for Judah and to strike
Da suka fara waƙa, suna kuma yabo, sai Ubangiji ya kai hari a kan mutanen Ammon da Mowab da Dutsen Seyir, waɗanda suka kawo hari a Yahuda, aka kuwa ci su da yaƙi.
23 and to stand: rise son: descendant/people Ammon and Moab upon to dwell mountain: mount (Mount) Seir to/for to devote/destroy and to/for to destroy and like/as to end: finish they in/on/with to dwell (Mount) Seir to help man: anyone in/on/with neighbor his to/for destruction
Mutanen Ammon da Mowab suka tasar wa mazaunan Dutsen Seyir, suka hallaka su ƙaƙaf. Sa’ad da suka karkashe mazaunan Seyir sai suka fāɗa wa juna, suka yi ta hallaka juna.
24 and Judah to come (in): come upon [the] lookout to/for wilderness and to turn to(wards) [the] crowd and look! they corpse to fall: fall land: soil [to] and nothing survivor
Sa’ad da mutanen Yahuda suka zo wurin da yake fuskantar hamada, suka duba ta wajen babban rundunar, sai suka ga gawawwaki birjik a ƙasa; babu wani wanda ya kuɓuta.
25 and to come (in): come Jehoshaphat and people his to/for to plunder [obj] spoil their and to find in/on/with them to/for abundance and property and corpse and article/utensil precious thing and to rescue to/for them to/for nothing burden and to be day three to plunder [obj] [the] spoil for many he/she/it
Sa’ad da Yehoshafat da jama’arsa suka je kwasar ganima, sai suka sami shanu masu yawan gaske, da kayayyaki, da tufafi, da abubuwa masu daraja, waɗanda suka yi ta kwasa har suka gaji. Kwana uku suka yi suna kwasar ganimar saboda yawanta.
26 and in/on/with day: today [the] fourth to gather to/for Valley (of Beracah) Beracah (Valley) for there to bless [obj] LORD upon so to call: call by [obj] name [the] place [the] he/she/it Valley (of Beracah) Beracah (Valley) till [the] day: today
A rana ta huɗu sai suka taru a Kwarin Beraka, inda suka yabi Ubangiji. Wannan ne ya sa ake kiransa Kwarin Beraka har wa yau.
27 and to return: return all man Judah and Jerusalem and Jehoshaphat in/on/with head: leader their to/for to return: return to(wards) Jerusalem in/on/with joy for to rejoice them LORD from enemy their
Sa’an nan Yehoshafat ya jagoranci dukan mutanen Yahuda da Urushalima suka dawo da farin ciki zuwa Urushalima, gama Ubangiji ya ba su dalilin farin ciki a kan abokan gābansu.
28 and to come (in): come Jerusalem in/on/with harp and in/on/with lyre and in/on/with trumpet to(wards) house: temple LORD
Suka shiga Urushalima suka shiga haikalin Ubangiji da kiɗin molaye da sarewa da kuma garayu.
29 and to be dread God upon all kingdom [the] land: country/planet in/on/with to hear: hear they for to fight LORD with enemy Israel
Tsoron Allah ya kama dukan mulkokin ƙasashe sa’ad da suka ji yadda Ubangiji ya yi yaƙi a kan abokan gāban Isra’ila.
30 and to quiet royalty Jehoshaphat and to rest to/for him God his from around
Mulkin Yehoshafat kuwa ya zauna lafiya, gama Allahnsa ya ba shi hutu a kowane gefe.
31 and to reign Jehoshaphat upon Judah son: aged thirty and five year in/on/with to reign he and twenty and five year to reign in/on/with Jerusalem and name mother his Azubah daughter Shilhi
Ta haka Yehoshafat ya yi mulki a bisa Yahuda. Yana da shekara talatin da biyar sa’ad da ya zama sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara ashirin da biyar. Sunan mahaifiyarsa Azuba ce,’yar Shilhi.
32 and to go: walk in/on/with way: conduct father his Asa and not to turn aside: turn aside from her to/for to make: do [the] upright in/on/with eye: seeing LORD
Ya yi tafiya a hanyoyin mahaifinsa Asa bai kuwa kauce daga gare su ba; ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji.
33 surely [the] high place not to turn aside: remove and still [the] people not to establish: establish heart their to/for God father their
Duk da haka ba a kawar da masujadai kan tudu ba, domin har yanzu mutanen ba su tsayar da zukatansu ga Allahn kakanninsu ba.
34 and remainder word: deed Jehoshaphat [the] first and [the] last look! they to write in/on/with word: deed Jehu son: child Hanani which to ascend: establish upon scroll: book king Israel
Sauran ayyukan mulkin Yehoshafat, daga farko zuwa ƙarshe, an rubuta su a tarihin Yehu ɗan Hanani, waɗanda aka rubuta a littafin sarakunan Isra’ila.
35 and after so to unite Jehoshaphat king Judah with Ahaziah king Israel he/she/it be wicked to/for to make: do
Daga baya, Yehoshafat sarkin Yahuda ya haɗa kai da Ahaziya sarkin Isra’ila, wanda yake da laifin mugunta.
36 and to unite him with him to/for to make fleet to/for to go: went Tarshish and to make fleet in/on/with Ezion-geber Ezion-geber
Ya yarda da shi su gina jiragen ruwan kasuwanci. Bayan aka gina waɗannan a Eziyon Geber,
37 and to prophesy Eliezer son: child Dodavahu from Mareshah upon Jehoshaphat to/for to say like/as to unite you with Ahaziah to break through LORD [obj] deed: work your and to break fleet and not to restrain to/for to go: went to(wards) Tarshish
Eliyezer ɗan Dodabahu na Maresha ya yi annabci a kan Yehoshafat cewa, “Domin ka haɗa kai da Ahaziya, Ubangiji zai hallaka abin da ka yi.” Jiragen ruwan kuwa suka farfashe, ba a kuwa iya sa su je kasuwanci ba.

< 2 Chronicles 20 >