< Romans 4 >

1 What then will we say to have discovered Abraham the (ancestor *N+KO) of us according to [the] flesh?
To, me za mu ce Ibrahim kakan kakanninmu ya gani game da wannan batu?
2 If for Abraham by works was justified, he has ground of boasting but not toward God.
In fa da gaske ne Ibrahim ya sami kuɓuta ta wurin ayyuka, yana da abin da zai yin taƙama da shi ke nan, amma ba a gaban Allah ba.
3 What for the Scripture says? Believed then Abraham in God, and it was reckoned to him for righteousness.
Me Nassin ya ce? “Ibrahim ya gaskata Allah, aka kuma lissafta wannan adalci ne a gare shi.”
4 To the [one] now working the reward not is reckoned according to grace but according to debt;
To, sa’ad da mutum ya yi aiki, ba a lissafta ladan aikinsa a matsayin kyauta, sai dai a matsayin hakkinsa.
5 To the [one] however not working, believing however on the [One] justifying the ungodly, is reckoned the faith of him for righteousness.
Amma fa, game da mutumin da ba ya aiki sai dai dogara ga Allah wanda yake kuɓutar da masu mugunta, akan lissafta bangaskiyarsa a matsayin adalci ne.
6 just as also David declares the blessedness of the man to whom God credits righteousness apart from works:
Dawuda ya faɗi haka sa’ad da ya yi magana game da albarkar da aka yi wa mutumin da Allah ya lissafta adalci a gare shi, ba don yă yi ayyuka ba.
7 Blessed [are] they of whom are forgiven the lawless deeds and of whom are covered the sins;
“Masu albarka ne waɗanda aka gafarta laifofinsu, waɗanda aka kuma rufe zunubansu.
8 blessed [is] [the] man (of whom *N+kO) certainly not may reckon [the] Lord sin.
Mai albarka ne mutumin da Ubangiji ba zai taɓa lissafta zunubansa ba.”
9 [Is] the blessing then this on the circumcision or also on the uncircumcision? We are saying for (that: *k) was credited to Abraham the faith as righteousness.
Shin, wannan albarkar a kan masu kaciya ne kawai, ko kuwa har da marasa kaciya ma? Mun sha faɗi cewa an lissafta bangaskiyar Ibrahim adalci ne a gare shi.
10 How then was it credited? In circumcision being or in uncircumcision? Not in circumcision but in uncircumcision;
A kan wane hali ne aka lissafta masa? Bayan da aka yi masa kaciya ne, ko kuwa kafin kaciyar? Ba bayan an yi masa kaciya ba ne, amma kafin a yi masa kaciya!
11 And [the] sign he received of circumcision, a seal of the righteousness of the faith that [he had] [while] in the uncircumcision; for the to be him father of all those believing in uncircumcision, for to be credited also to them the righteousness,
Ya kuma karɓi alamar kaciya, hatimin adalcin da yake da shi ta wurin bangaskiya tun yana marar kaciya. Saboda haka fa, ya zama mahaifin dukan waɗanda suka gaskata domin su ma a lasafta su masu adalci ne, ba tare da an yi musu kaciya ba.
12 and father of circumcision to those not of circumcision only but also to those walking in the steps during (the *k) uncircumcision (of the *k) faith of the father of us Abraham.
Ya kuma zama mahaifin masu kaciya waɗanda ba kaciya kaɗai suke da ita ba amma har ma suna bin gurbin bangaskiyar da mahaifinmu Ibrahim yake da ita kafin aka yi masa kaciya.
13 Not for through [the] Law [was] the promise to Abraham or to the descendants of him that heir he being (of the *k) world but through [the] righteousness of faith.
Ba ta wurin doka ce Ibrahim da zuriyarsa suka sami alkawarin cewa zai zama magājin duniya ba, amma sai dai ta wurin adalcin da yake zuwa ta wurin bangaskiya.
14 If for those of [the] Law [are] heirs, has been made void faith and has been nullified the promise;
Gama da a ce masu kiyaye doka ne magāda, ai, da bangaskiya ba ta da amfani, alkawarin kuma ya zama banza,
15 For law wrath brings; where (now *N+kO) no there is law, neither [is] transgression.
domin doka tana jawo fushi ne. Kuma inda babu doka babu keta umarni ke nan.
16 Therefore it [is] of faith, that [it may be] according to grace, for to be sure the promise to all the seed, not to that of the law only but also to that of [the] faith of Abraham, who is [the] father of all of us —
Saboda haka, alkawari yakan zo ta wurin bangaskiya ne, domin yă zama ta wurin alheri, don a tabbatar wa dukan zuriyar Ibrahim ba kawai ga waɗanda suke na doka ba amma har ma ga waɗanda suke na bangaskiyar Ibrahim. Shi ne kuwa mahaifinmu duka.
17 even as it has been written that A father of many nations I have made you, before whom he believed God, who is giving life to the dead and calling the [things] not [into] being as existing;
Kamar yadda yake a rubuce cewa, “Na mai da kai uban al’ummai masu yawa.” Shi ubanmu ne a gaban Allah, wanda a cikinsa ya gaskata, Allahn da yake ba da rai ga matattu, yake kuma kiran abubuwan da ba su kasance ba su zama kamar sun kasance.
18 who against hope in hope believed for to become him [the] father of many nations according to that spoken; So will be the offspring of you;
Saɓanin dukan bege, Ibrahim cikin bege ya gaskata, haka kuwa ya zama uban al’ummai masu yawa, kamar yadda aka riga aka faɗa masa cewa, “Haka zuriyarka za tă zama.”
19 And not having become weak in the faith (not *K) he considered his own body already expired, a hundred years old about being, and the lifelessness of the womb of Sarah,
Ba tare da ya bar bangaskiyarsa ta yi rauni ba, ya fuskanci gaskiyan nan mai cewa jikinsa mai tsufa matacce ne, da yake yana da shekara wajen ɗari, mahaifar Saratu kuma matacciya ce.
20 About however the promise of God not he did waver through unbelief, but was strengthened in faith, having given glory to God
Duk da haka bai yi shakka ta wurin rashin bangaskiya game da alkawarin Allah ba, sai ma ya ƙara ƙarfafa ga bangaskiyarsa, ya kuma ɗaukaka Allah,
21 and having been fully assured that what He has promised able He is also to do;
yana kuma da cikakken tabbaci cewa Allah yana da iko yă cika abin da ya yi alkawari.
22 Therefore also it was credited to him unto righteousness.
Shi ya sa, “aka lissafta adalci a gare shi.”
23 Not it was written now on account of him alone that it was credited to him,
Kalmomin nan, “aka lissafta a gare shi” ba a rubuta su saboda shi kaɗai ba ne,
24 but also on account of us to whom it is about to be credited, to those believing on the [One] having raised Jesus the Lord of us out from [the] dead,
amma saboda mu ma, mu da Allah zai lissafta adalci, mu da muka ba da gaskiya gare shi da ya tashe Yesu Ubangijinmu daga matattu.
25 who was delivered over for the trespasses of us and was raised for the justification of us.
An miƙa shi ga mutuwa saboda zunubanmu, aka kuma tashe shi zuwa rai saboda Allah zai same mu marasa laifi.

< Romans 4 >