< Matthew 8 >

1 (When was coming down *N+kO) now (He *N+kO) from the mountain followed Him crowds great.
Da ya sauko daga dutsen, sai taron mutane mai yawan gaske suka bi shi.
2 And behold a leper (having come near *N+kO) was worshipping Him saying; Lord, if You shall be willing, You are able me to cleanse.
Wani mutum mai kuturta ya zo ya durƙusa a gabansa ya ce, “Ubangiji, in kana so, kana iya tsabtacce ni.”
3 And having stretched out the hand He touched of him (Jesus *K) saying; I am willing, do be cleansed. And immediately was cleansed his leprosy.
Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin. Ya ce, “Ina so, ka tsabtacce!” Nan da nan aka warkar da shi daga kuturtarsa.
4 And says to him Jesus; do see that to no one may you tell, But do go yourself do show to the priest and do offer the gift that commanded Moses for a testimony to them.
Sai Yesu ya ce masa, “Ka lura kada ka gaya wa kowa. Sai dai ka tafi, ka nuna kanka ga firist ka kuma yi bayarwar da Musa ya umarta, a matsayin shaida gare su.”
5 (When was entering *N+kO) now (He *n+o) (Jesus *k) into Capernaum came to Him a centurion imploring Him
Da Yesu ya shiga Kafarnahum, sai wani jarumi ya zo wurinsa, yana neman taimako.
6 and saying; Lord, the servant of mine has been laid in the house paralyzed grievously being tormented.
Ya ce, “Ubangiji, bawana yana kwance a gida shanyayye, yana kuma shan azaba ƙwarai.”
7 And He says to him (Jesus: *ko) I myself having come will heal him.
Yesu ya ce masa, “Zan je in warkar da shi.”
8 And answering (now *o) the centurion was saying; Lord, not I am worthy that my under the roof You may come, but only do speak (a word, *N+kO) and will be healed the servant of mine.
Jarumin ya amsa, “Ubangiji, ban cancanci in sa ka zo gidana ba, ka dai yi magana kawai, bawana zai warke.
9 Also for I myself a man am under authority (appointed *O) having under myself soldiers and I say to this [one]; do go, and he goes, and to another; do come, and he comes, and to the servant of mine; do enact this, and he enacts [it].
Gama ni kaina mutum ne a ƙarƙashin iko, da kuma sojoji a ƙarƙashina. Nakan ce wa wannan, ‘Je ka,’ sai yă tafi; wancan kuma, ‘Zo nan,’ sai yă zo. Nakan ce wa bawana, ‘Yi wannan,’ sai kuwa yă yi.”
10 Having heard now Jesus marveled and He said to those following; Amen I say to you; (such *no) (no [one] *N+kO) so great faith in Israel have I found.
Da Yesu ya ji wannan, sai ya yi mamaki ya kuma ce wa waɗanda suke binsa, “Gaskiya nake gaya muku, ban taɓa samun wani a Isra’ila da bangaskiya mai girma haka ba.
11 I say now to you that many from east and west will come and they will recline with Abraham and Isaac and Jacob in the kingdom of the heavens.
Ina kuma gaya muku da yawa za su zo daga gabas da kuma yamma, su ɗauki wuraren zamansu a biki tare da Ibrahim, Ishaku, da Yaƙub a cikin mulkin sama.
12 the however sons of the kingdom will be cast out into the darkness the outer; there will be the weeping and the gnashing of the teeth.
Amma za a jefar da’ya’yan mulki waje, zuwa cikin baƙin duhu, inda za a yi kuka da cizon haƙora.”
13 And said Jesus to the centurion; do go, (and *ko) as you have believed it should be [done] to you. And was healed the servant of him in the hour that.
Sa’an nan Yesu ya ce wa jarumin, “Je ka! Za a yi bisa ga bangaskiyarka.” A daidai wannan lokaci bawansa kuwa ya warke.
14 And having come Jesus to the house of Peter He saw the mother-in-law of him lain down and fevering
Da Yesu ya zo cikin gidan Bitrus, sai ya ga surukar Bitrus tana kwance a gado tana da zazzaɓi.
15 And He touched the hand of her, and left her the fever. and she arose and was ministering (to him. *N+KO)
Ya taɓa hannunta sai zazzaɓin ya sake ta, ta kuwa tashi ta fara yin masa hidima.
16 When evening now having come they brought to Him being demonised many, and He cast out the spirits by a word, and all those sick being He healed,
Da yamma ta yi, aka kawo masa masu aljanu da yawa, ya kuwa fitar da ruhohin ta wurin magana, ya kuma warkar da dukan marasa lafiya.
17 so that it may be fulfilled that having been spoken through Isaiah the prophet saying; Himself the infirmities of us He took and [our] diseases bore.
Wannan ya faru ne domin a cika abin da aka faɗa ta bakin annabi Ishaya cewa, “Ya ɗebi rashin lafiyarmu, ya kuma ɗauki cututtukanmu.”
18 Having seen now Jesus (great *KO) (crowd *N+kO) around Him He commanded to depart to the other side.
Da Yesu ya ga taron mutane kewaye da shi, sai ya ba da umarni a ƙetare zuwa ɗayan hayin tafkin.
19 And having come to [Him] one scribe said to Him; Teacher, I will follow You wherever if You shall go.
Sai wani malamin dokoki ya zo wurinsa ya ce, “Malam, zan bi ka duk inda za ka.”
20 And says to him Jesus; Foxes holes have and the birds of the air nests, but the Son of Man no has [place] where the head He may lay.
Sai Yesu ya amsa ya ce, “Yanyawa suna da ramummuka, tsuntsayen sararin sama suna da sheƙuna, amma Ɗan Mutum ba shi da wurin da zai sa kansa.”
21 Another now of the disciples of Him said to Him; Lord, do allow me first to go and to bury the father of mine.
Sai wani almajiri ya ce masa, “Ubangiji, da farko bari in je in binne mahaifina.”
22 But Jesus (speaks *N+kO) to him; do follow Me, and do leave the dead to bury their own dead.
Amma Yesu ya ce masa, “Ka bi ni, ka bar matattu su binne matattunsu.”
23 And having climbed He into the boat followed Him the disciples of Him.
Sai ya shiga jirgin ruwa, almajiransa kuwa suka bi shi.
24 And behold a storm great arose in the sea so that the boat being swamped by the waves; He Himself however was sleeping.
Ba zato ba tsammani, sai wani babban hadari ya taso a tafkin, har raƙuman ruwan suka sha kan jirgin. Amma Yesu yana barci.
25 And having come to [Him] (the disciples of Him *k) they awoke Him saying; Lord, do save (us *k) we are perishing!
Almajiran suka je suka tashe shi, suna cewa, “Ubangiji, ka cece mu! Za mu nutse!”
26 And He says to them; Why fearful are you, O [you] of little faith? Then having arisen He rebuked the winds and the sea, and there was a calm great.
Ya amsa ya ce, “Ku masu ƙarancin bangaskiya, me ya sa kuke tsoro haka?” Sa’an nan ya tashi ya tsawata wa iskar da kuma raƙuman ruwan, sai wuri ya yi tsit gaba ɗaya.
27 And the men marveled saying; What kind [of man] is this that even the winds and the sea Him obey
Mutanen suka yi mamaki suka ce, “Wane irin mutum ne wannan? Har iska da raƙuman ruwa suna masa biyayya!”
28 And (when was coming He *N+kO) to the other side to the region of the (Gadarenes *N+KO) met Him two being demonised out of the tombs coming forth, violent extremely, so that not to be able anyone to pass through the way that.
Da ya isa ɗayan gefen a yankin Gadarenawa (ko kuwa Gerasenawa), sai ga mutum biyu masu aljanu suna fitowa daga kaburbura suka tarye shi. Su abin tsoro ne ƙwarai, har ba mai iya bin wannan hanya.
29 And behold they cried out saying; What to us and to you (Jesus *k) Son of God? Are You come here before [the] time to torment us?
Suka yi ihu suka ce, “Me ya haɗa ka da mu, Ɗan Allah?” Ka zo ne nan don ka ji mana kafin lokaci yă yi?
30 There was now far off from them a herd of pigs many feeding.
Nesa kaɗan da su kuwa akwai babban garken aladu da yake kiwo.
31 And the demons were begging Him saying; If You cast out us, (do allow *K) (do send away *N+KO) (us *N+kO) into the herd of pigs.
Aljanun suka roƙi Yesu suka ce, “In ka fitar da mu, tura mu cikin garken aladun nan.”
32 And He said to them; do go. And having gone out they went away into (herd *k) (pigs, *N+kO) and behold rushed all the herd (of the of pigs *k) down the steep bank into the sea, and perished in the waters.
Ya ce musu, “Ku tafi!” Sai suka fita suka shiga cikin aladun, dukan garken kuwa ya gangara a guje daga kan tudun zuwa cikin tafkin aladun kuma suka mutu a cikin ruwa.
33 Those now feeding [them] fled, and having gone away into the city they related everything including the [matter] of those being demonised.
Masu kiwon aladun suka ruga, suka je cikin gari suka ba da labarin dukan wannan, haɗe da abin da ya faru da mutanen nan masu aljanu.
34 And behold all the city went out to (meet *N+kO) Jesus, And having seen Him they begged [Him] that He may depart from the region of them.
Sai dukan garin suka fito don su taryi Yesu. Da suka kuwa gan shi, sai suka roƙe shi yă bar musu yanki.

< Matthew 8 >