< Luke 5 >

1 It came to pass then in the crowd pressing on Him (also *N+KO) to hear the word of God and He himself was already standing by the lake of Gennesaret
Ya zama sa'adda mutane sun taru a wurin Yesu suna sauraron maganar Allah, yana kuma yana tsaye a bakin tabkin Janisarata.
2 and He saw two boats already lying by the lake. but the fishermen from them having gone out (were washing *N+kO) the nets.
Ya ga jiragen ruwa biyu tsaye a bakin tabkin. Masu kamun kifin kuwa sun fita daga cikin jiragen suna wanke tarunsu.
3 Having climbed then into one of the boats which was (of the *k) Simon’s, He asked him from the land to put off a little. (and *ko) Having sat down (then *no) from the boat He was teaching the crowds.
Yesu ya shiga daya daga cikn jiragen wanda shike na Bitrus ne, sai ya umarce shi ya dan zakuda da jirgin daga bakin tabkin kadan zuwa cikin ruwa. Sai ya zauna ya kuma koya wa mutane daga cikin jirgin.
4 When then He left off speaking He said to Simon; do put off into the deep and do lower the nets of you for a catch.
Da ya gama magana, ya ce wa Siman, “Zakuda jirgin zuwa wuri mai zurfi sa'annan ka zuba tarunka domin kamu.”
5 And answering Simon said (to him: *ko) Master, through whole night having toiled no [thing] have we taken, at however the declaration of You I will let down (the *N+kO) (nets. *N+KO)
Siman ya amsa ya ce, “Ubangiji, mun yi aiki dukan dare bamu kama komai ba, amma bisa ga maganarka, zan jefa tarun.”
6 And this having done they enclosed a multitude of fishes great; were breaking now (the *N+kO) (nets *N+KO) of them.
Da sun yi haka, suka kama kifaye da yawan gaske, har tarunsu suna yagewa.
7 And they beckoned to the partners (to the *k) in the other boat having come to help them. and they came and filled both the boats so that [were] sinking they.
Sai suka roki abokan aikinsu da ke a dayan jirgin su zo su taimake su. Suka zo sun cika jiragen biyu da kifaye, har suka fara nutsewa.
8 Having seen now Simon Peter fell at the knees of Jesus saying; do depart from me, for a man sinful am I, Lord.
Amma Siman Bitrus, da ya ga haka, ya russuna a gaban Yesu, yana cewa, “Ka rabu da ni Ubangiji, gama ni mai zunubi ne.”
9 Amazement for laid hold on him and on all those with him at the catch of the fish (which *N+kO) they had taken,
Domin ya yi mamaki, da dukan wadanda suke tare da shi, sabili da yawan kifaye da suka kama.
10 likewise now also James and John [the] sons of Zebedee, who were partners with Simon. And said to Simon Jesus; Not do fear; from now on men you will be catching.
Wannan ya hada da Yakubu da Yahaya 'ya'yan Zabadi abokan aikin Siman. Sai Yesu ya ce wa Siman, “Kada ka ji tsoro, domin daga yanzu, za ka kama mutane.”
11 And having brought the boats to the land, having left (all [things] *N+kO) they followed Him.
Da sun kawo jiragensu waje kan kasa, suka bar komai suka kuma bi shi.
12 And it came to pass in being Him in one of the cities that behold a man full of leprosy; (and *ko) having seen (then *no) Jesus, having fallen upon [his] face begged Him saying; Lord, if You shall be willing, You are able me to cleanse.
Sa'adda yana daya daga cikin biranen, wani mutum dauke da kuturta yana nan wurin. Da ya ga Yesu, ya fadi bisa fuskarsa kasa yana rokansa, yana cewa, “Ubangji, idan ka yarda, za ka iya tsarkake ni.”
13 And having stretched out the hand He touched him (saying; *N+kO) I am willing, do be cleansed. And immediately the leprosy departed from him.
Yesu ya mika hanunsa ya taba shi, yana cewa, “Na yarda. Ka tsarkaka.” Sai nan da nan, kuturtar ta rabu da shi.
14 And He himself ordered him no one to tell But having gone do show yourself to the priest and do offer for the cleansing of you even as commanded Moses for a testimony to them.
Ya umarce shi kada ya gaya wa kowa, amma ya ce ma sa, “Tafi ka nuna kanka ga firist sa'annan ka mika hadaya domin tsarkakewarka, kamar yadda Musa ya umarta, a matsayin shaida a garesu.”
15 Was spread abroad now still more the report concerning Him; and were coming crowds great to hear and to be healed (by him *K) from the sicknesses of them;
Amma labarinsa ya bazu nesa, taron mutane da yawa kuma suka zo wurinsa domin su ji shi, su kuma samu warkarwa daga cututtukansu.
16 He Himself now was withdrawing into the wilderness and praying.
Amma ya kan janye zuwa wuraren da babu kowa ya yi addu'a.
17 And it came to pass on one of the days that He himself was teaching; and there were sitting by Pharisees and teachers of the law who were already coming out of every village of Galilee and of Judea and of Jerusalem, And [the] power of [the] Lord was with to heal (Him. *N+KO)
Ya zama daya a cikin kwanakin da yake koyarwa, akwai Farisawa da malaman attaura da ke zaune a wurin wandanda suka zo daga kauyukan da suke kewaye da Galili da Yahudiya da kuma birnin Urushalima. Ikon Ubangiji yana tare da shi domin warkarwa.
18 And behold men carrying upon a mat a man who was paralyzed, and they were seeking him to bring in and to place him before Him.
A lokacin nan, wasu mutane suka zo dauke da wani mutum shanyayye a kan tabarma, suka kuma nemi yadda za su shigar da shi ciki, su kwantar da shi a gaban Yesu.
19 And not having found (through *k) what way they may bring in him on account of the crowd, having gone up on the housetop through the tiles they let down him with the mat into the midst before Jesus.
Ba su iya samun hanyar da za su shigar da shi ba saboda taron, sai suka hau saman gidan, suka saukar da shi daga rufin, a kan tabarman sa, zuwa tsakiyar mutanen, dai dai a gaban Yesu.
20 And having seen the faith of them He said (to him: *k) Man, have been forgiven you the sins of you.
Da ya ga bangaskiyarsu, Yesu ya ce, “Maigida, an gafarta zunubanka.”
21 And began to reason the scribes and the Pharisees saying; Who is this who speaks blasphemies? Who is able sins (to forgive *N+kO) only except [the] sole God?
Marubuta da Farisawa suka fara sukar wannan, suna cewa, “Wanene wannan da ke sabo? Wa zai iya gafarta zunubi, idan ba Allah kadai ba?”
22 Having known now Jesus the reasonings of them answering He said to them; Why reason you in the hearts of you?
Amma da Yesu ya fahimci abin da suke tunani, sai ya amsa ya ce masu, “Don me kuke sukar wannan a zuciyarku?
23 Which is easier, to say; Have been forgiven you the sins of you, or to say; (do arise *N+kO) and do walk?
Wanne ne ya fi sauki a ce, 'An yafe zunubanka' ko kuwa a ce, 'Tashi ka yi tafiya?”
24 That however you may know that the Son of Man authority has on the earth to forgive sins, He said to the [one] paralyzed; To you I say, (do arise *N+kO) and having taken up the mat of you, do go to the house of you.
Amma domin ku sani cewa Dan Mutum yana da yancin gafarta zunubai a duniya, na ce maka, 'Tashi, dauki tabarmanka, ka tafi gidanka.'”
25 And immediately having stood up before them, having taken up [that] on (which *N+kO) he was lying, he departed to the home of him glorifying God.
Nan take, ya tashi a gabansu ya dauki tabarma da yake kwance; sai ya koma gidansa, yana daukaka Allah.
26 And amazement seized all, and they were glorifying God and were filled with fear saying that We have seen remarkable things today.
Kowa yana ta mamaki kuma suka daukaka Allah. Suna cike da tsoro, suna cewa, “Yau mun ga abubuwan al'ajibi.”
27 And after these things He went forth and He saw a tax collector named Levi sitting at the tax booth and He said to him; do follow Me.
Bayan wadannan abubuwa sun faru, Yesu ya fito daga can sai ya ga wani mai karban haraji mai suna Lawi yana zama a wurin karban haraji. Ya ce masa, “Ka biyo ni.”
28 And having left (all [things] *N+kO) having arisen (he was following *N+kO) Him.
Sai Lawi ya bar komai, ya tashi, ya bi shi.
29 And made a banquet great Levi for Him in the house of him, and there was a multitude great of tax collectors and others who were with them reclining.
Lawi kuma ya shirya gagarumar liyafa a gidansa, kuma akwai masu karban haraji da yawa a nan, da wasu mutane da ke zama a gaban teburin liyafar suna cin abinci tare da su.
30 And were grumbling the Pharisees and the scribes of them at the disciples of Him saying; Because of why with the tax collectors and sinners do you eat and drink?
Amma Farisawa da Marubuta suka fara korafi ga almajiransa, suna cewa, “Don menene kuna ci da sha tare da masu karban haraji da mutane masu zunubi?”
31 And answering Jesus said to them; No need have those being well of a physician but those sick being.
Yesu ya amsa masu, “Masu lafiya basu bukatar likita, wadanda ke marasa lafiya kadai ke bukatar likita.
32 Not I have come to call righteous [ones] but sinners to repentance.
Ban zo domin kiran masu adalci ba, amma na zo ne domin kiran masu zunubi zuwa ga tuba.”
33 And they said to Him; (through why *KO) The disciples of John fast often and prayers make, likewise also those of the Pharisees, those however of You eat and drink.
Sun ce masa, “Almajiran Yahaya sukan yi azumi da addu'a, kuma almajiran Farisawa ma sukan yi haka. Amma almajiranka suna ci suna sha?”
34 And (Jesus *no) said to them; Not are you able the sons of the bridechamber in which [time] the bridegroom with them is, to make (to fast? *N+kO)
Yesu ya ce masu, “Akwai wanda zai sa abokan ango su yi azumi, a lokacin da shi ango yana tare da su?
35 Will come however days also when may be taken away from them the bridegroom, then they will fast in those days.
Amma kwanaki na zuwa wadanda za a dauke ango daga wurinsu, a kwanakin za su yi azumi.”
36 He was speaking now also a parable to them that No [one] a piece (of *no) a garment new (having torn *NO) puts [it] on a garment old; lest then except indeed also the new (will tear, *N+kO) and to the old not (it will match *N+kO) (the *no) piece of the new.
Sai Yesu ya sake fada masu wani misali. “Babu wanda zai yage kyalle daga sabuwar tufa, ya kuma yi amfani da ita ya dinka tsohuwar tufa. Idan ya yi hakannan, zai yage sabuwar tufar, kuma kyallen daga sabuwar tufar ba zai dace da kyallen tsohuwar tufar ba.
37 And no [one] puts wine new into wineskins old; lest then except indeed will burst the wine new the wineskins and it will be spilled out, and the wineskins will be destroyed;
Kuma, babu mutum da zai sa sabon ruwan inabi a cikin tsofafin salkuna. Idan ya yi haka, sabon ruwan inabin zai fasa salkunan, kuma ruwan inabin din zai zube, salkunan kuma za su lallace.
38 But wine new into wineskins fresh must be put (and both are preserved. *KO)
Amma dole ne a sa sabon ruwan inabi a sabobin salkuna.
39 And no [one] having drunk old [wine] (immediately *K) desires new, he says for; The old (good *N+kO) is.
Babu wanda zai yi marmarin sabon ruwan inabi bayan da ya sha tsohon, gama zai ce, “Tsohon ya fi sabon.”

< Luke 5 >