< Hebrews 10 >

1 A shadow for having the law of the coming good things, not themselves the form of the things, each year with the same sacrifices which they offer to the continuous never (is able *NK+o) those drawing near to perfect;
Domin shari'a hoto ce na kyawawan abubuwan da ke zuwa, ba ainihin siffar wadannan abubuwa ba. Wadanda ke gusowa kusa da Allah ba za su taba ingantuwa ta wurin hadayu da firistoci ke mikawa shekara da shekaru ba.
2 Otherwise not would they have ceased being offered because of none having any longer conscience of sins those serving once (cleansed! *N+KO)
In ba haka ba, ba sai a dena mika hadayun ba? Bisa ga wannan al'amari, inda sun tsarkaka sau daya tak da masu sujada ba su san menene zunubi ba.
3 But in these [there is] a reminder of sins every year;
Amma wadannan hadayun sun zama matuni ne na zunubi shekara biye da shekara.
4 Impossible [it is] indeed [for the] blood of bulls and of goats to take away sins.
Domin ba shi yiwuwa jinin bijimai da awakai su kawar da zunubai.
5 Therefore coming into the world He says: Sacrifice and offering not You have desired, a body however You have prepared me;
Yayin da Almasihu ya zo duniya, ya ce, “Ba hadayu da sadakoki kake marmari ba. Maimakon haka, ka shirya mini jiki domin hadaya.
6 Burnt offerings and [offerings] for sin not You have delighted in;
Baka murna domin sadakoki da hadayu na konawa domin zunubi.
7 Then I said; Behold I have come — in [the] scroll of [the] book it has been written of Me — to do, O God, the will of You.
Sai na ce, 'Duba, gani na zo in yi nufinka, kamar yadda aka rubuta akaina.'''
8 Above saying that (sacrifices *N+KO) and (offerings *N+KO) and burnt offerings and [offerings] for sin not You have desired nor You delighted in, which according to (the *k) Law are offered,
Da fari Yace ''ba hadayu, ko sadakoki, ko kuma hadaya ta konawa domin zunubi kake bukata ba. Ba ka kuwa jin dadinsu.'' Wadannan sune hadayun da ake bayarwa bisa ga shari'a.
9 then He has said; Behold I have come to do (of the God *K) the will of You. He takes away the first that the second He may establish;
Sa'annan sai ya ce ''gani na zo domin in aikata nufinka.” Ya kawar da hidimar farko domin ya kafa hidima ta biyu.
10 By that will sanctified we are through the offering of the body of Jesus Christ once for all.
A hidima ta biyu, an kebe mu ga Allah ta wurin nufinsa ta wurin hadayar jikin Yesu Almasihu bugu daya ba kari.
11 And every indeed priest has stood every day ministering and the same repeatedly offering sacrifices, which never are able to take away sins;
Haka, kowanne firist ya ke tsayawa kulliyomi domin ya yi hidima ga Allah. A kullum yana mika hadayu, iri daya, koda shike ba za su taba kawar da zunubai ba.
12 (This [One] *N+kO) however one for sins having offered sacrifice in perpetuity sat down at [the] right hand of God,
A ta wata hanya kuma, Almasihu ya mika hadaya sau daya tak domin zunubai har abada, ya zauna a hannun dama na Allah.
13 the henceforth awaiting until may be placed the enemies of Him [as] a footstool for the feet of Him.
Yana jiran har a maida makiyansa matashin sawayensa.
14 By one for offering He has perfected for all time those being sanctified.
Domin ta wurin hadaya guda dayan nan ya kammala har abada ga wadanda suka sadaukar da kansu ga Allah.
15 Bears witness now to us also the Spirit Holy; after for (to have said: *N+KO)
Kuma Ruhu mai Tsarki ya shaida mana. Abu na farko yace,
16 This [is] the covenant that I will make with them after the days those, says [the] Lord, putting [the] laws of Mine into [the] hearts of them and into (the mind *N+kO) of them I will inscribe them;
“Wannan shi ne alkawarin da zan yi da su a bayan kwanakin nan,' inji Ubangiji Zan sa dokokina a cikin zukatansu, kuma zan rubuta su a lamirinsu.
17 and The sins of them and the lawless acts of them certainly not (will I remember *N+kO) any more.
Ba zan sake tunawa da zunubansu da kurakuransu ba.''
18 Where now forgiveness of these [is], no longer no longer an offering for sin.
Yanzu fa duk in da aka sami gafara domin wadannan abubuwa, babu wata hadaya domin zunubi.
19 Having therefore, brothers, confidence for the entering to the Holy [Places] by the blood of Jesus,
Saboda haka, yan'uwa, ba mu da shakkar shigowa wurin nan mafi tsarki ta wurin jinin Yesu.
20 which He dedicated for us a way new and living through the veil, That is through the flesh of Him,
Wannan ita ce sabuwar rayayyar hanya da ya bude mana ta wurin labulen, wato ta wurin jikinsa.
21 and [having] a priest great over the house of God,
Saboda muna da babban firist a gidan Allah.
22 we may draw near with a sincere heart in full assurance of faith sprinkled clean [our] hearts from a conscience evil and (having ourselves washed *N+kO) [our] body with water pure.
Bari mu matso kusa da sahihiyar zuciya, da kuma cikakken gabagadi cikin bangaskiya, da zuciyarmu wadda aka tsarkake daga mummunan tunani, da kuma jikunanmu wankakku da ruwa mai tsabta.
23 We may hold fast to the confession of [our] hope firmly, faithful for [is] the [One] having promised,
Bari mu rike da karfi shaidar bangaskiyar begenmu, ba tare da raurawa ba, domin Allahn, da ya yi alkawari, mai aminci ne.
24 And we may think one another toward stirring up to love and to good works
Bari mu kuma yi lura yadda za mu iza juna ga kauna da ayyuka masu dacewa.
25 not forsaking the assembling together of ourselves even as [is the] custom with some, but encouraging [one another], and so much more as much as you see drawing near the Day.
Kada mu fasa zumunci da juna, kamar yadda wadansu sukan yi. A maimakon haka, bari mu karfafa juna a kulluyomin, kamar yada kuke ganin kusantowar ranan nan.
26 [If] willingly for sin we after [we are] to receive the knowledge of the truth no longer no longer for sins remains a sacrifice,
Saboda idan mun ci gaba da zunubin ganganci bayan mun rigaya mun sami wannan sanin gaskiyar, hadayar irin wannan zunubi bata samuwa.
27 terrifying however a certain expectation of judgment and of fire fury to devour being about the adversaries.
Maimakon haka, sai fargabar babban tsoron hukunci, da kuma wuta mai zafi, da zata cinye makiyan Allah.
28 Having set aside anyone [the] law of Moses without mercies on the basis of two or three witnesses he dies;
Dukkan wanda ya ki bin dokar Musa zai mutu ba tausayi ta wurin shaidu biyu ko uku.
29 How much think you worse will he deserve punishment the [one] the Son of God having trampled upon and the blood of the covenant ordinary having esteemed by which he was sanctified and the Spirit of grace having insulted?
Wanne irin hukunci kuke tsammani ya dace ga wadanda suka raina Dan Allah, duk wadanda suka maida jinin alkawarin nan kamar ba tsarkakakke ba, wanda ta wurin jinin nan ne aka kebe shi ga Allah- wadanda suka wulakantar da Ruhun alheri?
30 We know for the [One] having said; Mine [is] vengeance, I myself will repay (says Lord; *K) and again: Will judge [the] Lord the people of Him.
Domin mun san wanda yace, “Ramako nawa ne; Zan yi sakayya.'' Sa'annan kuma, “Ubangiji zai hukumta jama'arsa.”
31 [It is] a fearful thing to fall into [the] hands of God [the] living.
Abin tsoro ne a fada cikin hannuwan Allah mai rai!
32 do remember however the former days in which having been enlightened a great conflict you endured of sufferings,
Amma ku tuna da kwanakin baya, bayan da ku ka sami haske, yadda kuka jure babban fama cikin wahala.
33 this indeed by revilings both and by tribulations being made a spectacle, this however partners of those thus passing through [them] having become;
Aka kunyatar da ku a gaban jama'a, ta wurin ba'a da cin mutunci, kuna kuma dandana irin azabar da wadansu suka shiga ciki.
34 Both for with the (prisoners *N+KO) you sympathized and the plundering of the possessions of you with joy you accepted knowing to have (in *k) (yourselves *N+kO) (a better *NK+o) possession (in heavens *K) and abiding.
Domin kuna da tausayi ga wadanda suke kurkuku, da farin ciki, kun amince da kwace na dukiyarku da aka yi, kun mallaki madauwamiyar mallaka mafi kyau. Dominn kun ji tausayina sa'adda na ke a kurkuku.
35 Not may throw away therefore the boldness of you, which has a great reward.
Don haka kada ku yarda gabagadinku, wanda ke da babban sakamako.
36 Of endurance for You have need, so that the will of God having done you may receive the promise.
Domin kuna bukatar hakuri don ku sami abin da Allah ya alkawarta, bayan kun aikata nufinsa.
37 Yet for A little very while, the [One] who is coming will come and not will delay.
“Domin a dan karamin lokaci, mai zuwan nan zai zo ba zai yi jinkiri ba.
38 The one however righteous (of Mine *NO) by faith will live; and if he shall shrink back, not takes pleasure the soul of Mine in him.
Adalina kuwa zai rayu ta wurin bangaskiya. In kuwa ya ja da baya, ba zan yi farin ciki dashi ba.”
39 We ourselves however not are of [those] drawing back to destruction but of faith to [the] preserving [of the] soul.
Amma mu bama cikin wadanda suka ja da baya zuwa hallaka. Maimakon haka, muna cikin wadanda suke da bangaskiya domin kula da rayukanmu.

< Hebrews 10 >