< Hebrews 10 >

1 A shadow for having the law of the coming good things, not themselves the form of the things, each year with the same sacrifices which they offer to the continuous never (is able *NK+o) those drawing near to perfect;
Dokar, inuwa ce kawai ta kyawawan abubuwa masu zuwa, wannan inuwar ba ita ce ainihin abubuwan ba ne. Saboda haka ba za tă taɓa mai da masu matsowa kusa don yin sujada cikakku ta wurin irin hadayun da ake maimaitawa ba fasawa shekara-shekara ba.
2 Otherwise not would they have ceased being offered because of none having any longer conscience of sins those serving once (cleansed! *N+KO)
Da a ce za tă iya, da ba su daina miƙa hadayu ba? Ai, da an riga an tsabtacce masu yin sujada sau ɗaya tak, da kuma ba za su ƙara damuwa da zunubansu ba.
3 But in these [there is] a reminder of sins every year;
Amma waɗancan hadayu abin tunawa da zunubai ne na kowace shekara,
4 Impossible [it is] indeed [for the] blood of bulls and of goats to take away sins.
domin ba zai taɓa yiwuwa jinin bijimai da na awaki yă kawar da zunubai ba.
5 Therefore coming into the world He says: Sacrifice and offering not You have desired, a body however You have prepared me;
Saboda haka, sa’ad da Kiristi ya shigo duniya ya ce, “Hadaya da sadaka kam ba ka so, sai dai ka tanadar mini jiki;
6 Burnt offerings and [offerings] for sin not You have delighted in;
hadayun ƙonawa da kuma hadayun zunubi ba ka ji daɗin.
7 Then I said; Behold I have come — in [the] scroll of [the] book it has been written of Me — to do, O God, the will of You.
Sai na ce, ‘Ga ni nan, a rubuce yake cikin naɗaɗɗen littafi na zo in aikata nufinka, ya Allah.’”
8 Above saying that (sacrifices *N+KO) and (offerings *N+KO) and burnt offerings and [offerings] for sin not You have desired nor You delighted in, which according to (the *k) Law are offered,
Da farko ya ce, “Hadayu da sadakoki, hadayun ƙonawa da hadayun zunubi ba ka so, ba ka kuwa jin daɗinsu” (ko da yake doka ta bukaci a yi su).
9 then He has said; Behold I have come to do (of the God *K) the will of You. He takes away the first that the second He may establish;
Sa’an nan ya ce, “Ga ni nan, na zo in aikata nufinka.” Ya kawar da na farkon domin yă kafa na biyun.
10 By that will sanctified we are through the offering of the body of Jesus Christ once for all.
Kuma bisa ga wannan nufi, aka mai da mu masu tsarki ta wurin miƙa hadayar jikin Yesu Kiristi sau ɗaya tak.
11 And every indeed priest has stood every day ministering and the same repeatedly offering sacrifices, which never are able to take away sins;
Kowace rana kowane firist yakan tsaya yin hidimar ibadarsa; sau da sau yakan miƙa hadayu iri ɗaya, waɗanda ba za su taɓa kawar da zunubai ba.
12 (This [One] *N+kO) however one for sins having offered sacrifice in perpetuity sat down at [the] right hand of God,
Amma da Kiristi ya miƙa hadaya ɗaya ta dukan lokaci saboda zunubai, sai ya zauna a hannun dama na Allah.
13 the henceforth awaiting until may be placed the enemies of Him [as] a footstool for the feet of Him.
Tun daga lokacin nan yana jira a mai da abokan gābansa matashin ƙafafunsa,
14 By one for offering He has perfected for all time those being sanctified.
gama ta wurin hadayan nan guda ɗaya ya kammala har abada waɗanda ake tsarkake.
15 Bears witness now to us also the Spirit Holy; after for (to have said: *N+KO)
Ruhu Mai Tsarki ma ya yi mana shaida game da wannan. Da farko ya ce,
16 This [is] the covenant that I will make with them after the days those, says [the] Lord, putting [the] laws of Mine into [the] hearts of them and into (the mind *N+kO) of them I will inscribe them;
“Wannan shi ne alkawarin da zan yi da su bayan wannan lokaci, in ji Ubangiji. Zan sa dokokina a cikin zukatansu, in kuma rubuta su a kan zukatansu.”
17 and The sins of them and the lawless acts of them certainly not (will I remember *N+kO) any more.
Sai ya ƙara da cewa, “Zunubansu da kurakuransu ba zan ƙara tunawa da su ba.”
18 Where now forgiveness of these [is], no longer no longer an offering for sin.
In an gafarta zunubai, babu sauran bukatar miƙa hadaya.
19 Having therefore, brothers, confidence for the entering to the Holy [Places] by the blood of Jesus,
Saboda haka,’yan’uwa, da yake muna da wannan tabbaci na shiga Wuri Mafi Tsarki ta wurin jinin Yesu,
20 which He dedicated for us a way new and living through the veil, That is through the flesh of Him,
ta wurin sabuwa, rayayyiyar hanya kuma wadda aka buɗe mana ta labulen nan, wato, jikinsa,
21 and [having] a priest great over the house of God,
da yake kuma muna da babban firist mai mulkin gidan Allah,
22 we may draw near with a sincere heart in full assurance of faith sprinkled clean [our] hearts from a conscience evil and (having ourselves washed *N+kO) [our] body with water pure.
bari mu matso kusa da Allah da zuciya mai gaskiya da kuma cikakken tabbaci mai zuwa ta wurin bangaskiya. Bari mu bar zukatan da tsabta, lamirinmu babu mugunta, da kuma jikunanmu a wanke da ruwa.
23 We may hold fast to the confession of [our] hope firmly, faithful for [is] the [One] having promised,
Bari mu tsaya da ƙarfi a kan ga begen da muka ce namu ne, gama shi da ya yi alkawarin, mai aminci ne.
24 And we may think one another toward stirring up to love and to good works
Bari kuma mu yi tunani a kan yadda za mu gargaɗe juna ga ƙauna da kuma ayyuka nagari.
25 not forsaking the assembling together of ourselves even as [is the] custom with some, but encouraging [one another], and so much more as much as you see drawing near the Day.
Kada mu daina taruwa kamar yadda waɗansu suka saba, sai dai mu ƙarfafa juna, tun ba ma da kuka ga Ranan nan tana kusatowa ba.
26 [If] willingly for sin we after [we are] to receive the knowledge of the truth no longer no longer for sins remains a sacrifice,
Ba wata hadayar da za a yi don mutanen da suka yanke shawara su yi ci gaba da yin zunubi da gangan bayan sun sami sanin gaskiya.
27 terrifying however a certain expectation of judgment and of fire fury to devour being about the adversaries.
A maimakon haka za su kasance da babban fargabar hukunci da kuma ta ƙunar wuta wadda za tă cinye abokan gāban Allah.
28 Having set aside anyone [the] law of Moses without mercies on the basis of two or three witnesses he dies;
Duk wanda ya ƙi ya kiyaye dokar Musa akan kashe shi ba tausayi, a kan shaidar mutum biyu ko uku.
29 How much think you worse will he deserve punishment the [one] the Son of God having trampled upon and the blood of the covenant ordinary having esteemed by which he was sanctified and the Spirit of grace having insulted?
Wane irin hukunci mai tsanani ne kuke tsammani zai dace da mutumin da ya nuna rashin bangirma ga Ɗan Allah, wanda ya yi banza da jinin nan na alkawarin da ya tsarkake shi, wanda kuma ya zargi Ruhun alheri?
30 We know for the [One] having said; Mine [is] vengeance, I myself will repay (says Lord; *K) and again: Will judge [the] Lord the people of Him.
Gama mun san shi, wannan wanda ya ce, “Ramuwa tawa ce; zan rama,” da kuma, “Ubangiji zai yi wa mutanensa hukunci.”
31 [It is] a fearful thing to fall into [the] hands of God [the] living.
Abu mai matuƙar bantsoro ne a fāɗa cikin hannuwan Allah mai rai.
32 do remember however the former days in which having been enlightened a great conflict you endured of sufferings,
Ku tuna da kwanakin nan da suka wuce bayan kun sami haske, sa’ad da kuka tsaya daram a tsananin shan wahala.
33 this indeed by revilings both and by tribulations being made a spectacle, this however partners of those thus passing through [them] having become;
Wani lokaci a fili an tsananta muku aka kuma zage ku aka kuma tsananta muku; a wani lokaci kuma kuka tsaya tare da waɗanda aka yi musu haka.
34 Both for with the (prisoners *N+KO) you sympathized and the plundering of the possessions of you with joy you accepted knowing to have (in *k) (yourselves *N+kO) (a better *NK+o) possession (in heavens *K) and abiding.
Kuka ji tausayin waɗanda suke cikin kurkuku, da farin ciki kuma kuka yarda ku rabu da dukiyar da aka ƙwace muku, domin ku kanku kun san cewa kuna da madawwamiyar dukiya mafi kyau.
35 Not may throw away therefore the boldness of you, which has a great reward.
Saboda haka kada ku yar da tabbacinku; za a sāka muku a yalwace.
36 Of endurance for You have need, so that the will of God having done you may receive the promise.
Kuna bukata ku jimre don sa’ad da kuka aikata nufin Allah, za ku karɓi abin da ya yi alkawari.
37 Yet for A little very while, the [One] who is coming will come and not will delay.
Gama, “A cikin ɗan lokaci kaɗan, mai zuwan nan zai zo ba kuwa zai yi jinkiri ba.
38 The one however righteous (of Mine *NO) by faith will live; and if he shall shrink back, not takes pleasure the soul of Mine in him.
Amma, “Mai adalcina zai rayu ta wurin bangaskiya. In kuwa ya ja da baya, ba zan ji daɗinsa ba.”
39 We ourselves however not are of [those] drawing back to destruction but of faith to [the] preserving [of the] soul.
Amma mu ba na waɗanda suke ja da baya, su kuma hallaka ba ne, amma na waɗanda suka gaskata, suka kuma sami ceto ne.

< Hebrews 10 >