< Zechariah 2 >

1 Then lifted I up mine eyes and looked, and lo! a Man, —and, in his hand, a Measuring Line.
Sa’an nan na ɗaga kai sai na ga mutum a tsaye riƙe da ma’auni a hannunsa!
2 And I said, Whither art thou going? And he said unto me, To measure Jerusalem, to see what [should be] the breadth thereof, and what the length thereof.
Sai na yi tambaya, na ce, “Ina za ka?” Ya amsa mini ya ce, “Zan je in auna Urushalima, in ga yadda fāɗinta da tsawonta suke.”
3 And lo! the messenger who was talking with me, coming forward, —and another messenger, coming forward to meet him.
Sai mala’ikan da yake yi mini magana ya tafi, sai wani mala’ika ya zo ya same shi
4 So he said unto him, Run, speak unto this young man, saying: Like open villages, shall Jerusalem remain, for the multitude of men and cattle in her midst;
ya ce masa, “Yi gudu, gaya wa saurayin can cewa, ‘Urushalima za tă zama birni marar katanga domin mutane da dabbobi masu yawa ƙwarai za su kasance a cikinta.
5 And, I, will become to her, declareth Yahweh, A wall of fire round about, —and, a glory, will I become in her midst.
Ni da kaina ne zan zama katangar wuta kewaye da birnin, in kuma zama darajarta,’ in ji Ubangiji.
6 Ho! ho! flee ye, therefore, out of the land of the North, urgeth Yahweh. For, as the four winds of the heavens, have I spread you abroad, declareth Yahweh.
“Zo! Zo! Ku gudu daga ƙasar arewa,” in ji Ubangiji, “gama na warwatsa ku a kusurwoyi huɗu na sama,” in ji Ubangiji.
7 Ho! Zion, deliver thyself, —thou that dwellest with the daughter of Babylon. For,
“Zo, ya ke Sihiyona! Ku tsere, ku masu zama a cikin Diyar Babilon!”
8 Thus, saith Yahweh of hosts, For his own honour, hath he sent me unto the nations that are spoiling you, —Surely, he that toucheth you, toucheth the pupil of mine eye.
Gama ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Bayan ya ɗaukaka ni, ya kuma aiko ni ga ƙasashen da suka washe ku gama duk wanda ya taɓa ku ya taɓa ƙwayar idonsa ne.
9 For behold me! brandishing my hand over them, and they shall become a spoil unto their own slaves, —and ye shall know that, Yahweh of hosts, hath sent me.
Ba shakka zan tā da hannuna a kansu domin bayinsu su washe su. Sa’an nan za ku san cewa Ubangiji Maɗaukaki ne ya aiko ni.
10 Sing out and rejoice, O daughter of Zion, —For behold me! coming in, and I will make my habitation in thy midst, declareth Yahweh.
“Ki yi sowa ki yi murna, ya ke Diyar Sihiyona. Gama ina zuwa, zan zauna a cikinki,” in ji Ubangiji.
11 Then shall many nations, join themselves, unto Yahweh, in that day, and shall become my people, —and I will make my habitation in thy midst, so shalt thou know that, Yahweh of hosts, hath sent me unto thee.
“Ƙasashe da yawa za su haɗa kai da Ubangiji a ranan nan, za su kuma zama mutanena. Zan zauna a cikinku, za ku kuma san cewa Ubangiji Maɗaukaki ne ya aiko ni gare ku.
12 Thus will Yahweh inherit Judah, his portion, on the soil of the sanctuary, —and make choice, yet again, of Jerusalem.
Ubangiji zai gāji Yahuda a matsayin rabonsa a cikin ƙasa mai tsarki zai kuma sāke zaɓi Urushalima.
13 Hush! all flesh, before Yahweh, —For he hath roused himself up out of his holy dwelling.
Ku yi tsit a gaban Ubangiji, dukanku’yan adam, gama ya taso daga wurin zamansa mai tsarki.”

< Zechariah 2 >