< Psalms 71 >

1 In thee, O Yahweh, have I sought refuge, May I not be ashamed unto times age-abiding:
A gare ka, ya Ubangiji, na nemi mafaka; kada ka taɓa sa in sha kunya.
2 In thy righteousness, wilt thou rescue me, and deliver me, Incline unto me thine ear, and save me:
Ka kuɓutar da ni ka cece ni cikin adalcinka; ka juya kunnenka gare ni ka kuma cece ni.
3 Be thou unto me, a Rock to dwell in, a Place of Security, To save me, For, my mountain crag and my stronghold, thou art.
Ka zama dutsena da kagarata, inda kullum zan je. Ka ba da umarni a cece ni, gama kai ne dutsen ɓuyana da katangata.
4 Oh my God, deliver me, From the hand of the lawless one, From the clutch of the perverse and ruthless one;
Ka cece ni, ya Allahna, daga hannun mugaye, da kuma daga ikon mugaye da masu mugunta.
5 For, thou, art my hope, My Lord, Yahweh, My confidence from my youthful days:
Gama kai ne abin sa zuciyata, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ƙarfin zuciyata tun ina yaro.
6 Upon thee, have I stayed myself from birth, Thou art he that severed me, from the body of my mother, Of thee, shall be my praise—continually.
Daga haihuwa na dogara gare ka; kai ka kawo ni daga cikin mahaifiyata. Kullayaumi zan yabe ka.
7 A very wonder, have I been unto many, Seeing that, thou, hast been my strong refuge,
Na zama kamar abin sa zuciya ga yawanci, amma kai ne katangata mai ƙarfi.
8 My mouth shall be filled with, thy praise, All the day, with thy splendour.
Bakina ya cika da yabonka, ina furta darajarka dukan yini.
9 Do not cast me off in the time of old age, When my vigour faileth, do not forsake me;
Kada ka yar da ni sa’ad da na tsufa; kada ka yashe ni sa’ad da ƙarfina ya ƙare.
10 For mine enemies have spoken of me, And, they who watch for my life, have taken counsel together;
Gama abokan gābana suna magana a kaina; waɗanda suke jira su kashe ni suna haɗa baki tare.
11 Saying, God, hath forsaken him, Pursue and take him, For there is none to rescue.
Suna cewa, “Allah ya yashe shi; mu fafare shi mu kama shi, gama ba wanda zai kuɓutar da shi.”
12 O God, be not far from me, O my God, to help me, make haste!
Kada ka yi nisa da ni, ya Allah; zo da sauri, ya Allahna, ka taimake ni.
13 Let them be ashamed—be consumed, Who are assailing my life, —Let them be covered with reproach and confusion, Who are seeking my hurt.
Bari masu zagina su hallaka da kunya; bari waɗanda suke so su cutar da ni su sha ba’a da kuma kunya.
14 But, I, continually will hope, And will add to all thy praise;
Amma game da ni, kullayaumi zan kasance da sa zuciya; zan yabe ka sau da sau.
15 My mouth, shall relate thy righteousness, All the day, thy deliverance, For I know not the numbers.
Bakina zai ba da labarin adalcinka, zai yi maganar cetonka dukan yini, ko da yake ban san yawansa ba.
16 I will enter into the mighty doings of My Lord—Yahweh, I will make mention of thy righteousness—thine alone.
Zan zo in furta in kuma yi shelar ayyukanka masu girma, ya Ubangiji Mai Iko Duka; zan yi shelar adalcinka, naka kaɗai.
17 O God, thou hast taught me from my youthful days, And, hitherto, have I been wont to tell of thy wonders;
Tun ina yaro, ya Allah, ka koya mini har wa yau ina furta ayyukanka masu banmamaki.
18 Even now, therefore, that I am old and grayheaded, O God, do not forsake me, —Until I tell of thine arm unto a [new] generation, Unto every one that is to come, thy might;
Ko sa’ad da na tsufa da furfura, kada ka yashe ni, ya Allah, sai na furta ikonka ga tsara mai zuwa, ƙarfinka ga dukan waɗanda suke zuwa.
19 And, as for thy righteousness, O God, up on high, Wherein thou hast wrought great things, O God! who is like unto thee?
Adalcinka ya kai sararin sama, ya Allah, kai da ka yi manyan abubuwa. Wane ne kamar ka, ya Allah?
20 Thou who hast let us see many distresses and misfortunes, Wilt again bring us to life, And, out of the resounding depths of the earth, wilt again raise us up;
Ko da yake ka sa na ga wahaloli, masu yawa da kuma masu ɗaci, za ka sāke mayar mini da rai; daga zurfafan duniya za ka sāke tā da ni.
21 Thou wilt increase my greatness, And, on every side, wilt comfort me.
Za ka ƙara girmana ka sāke ta’azantar da ni.
22 I also, will praise thee by the aid of a harp, Thy faithfulness, O my God, —I will make music unto thee with a lyre, Thou holy one of Israel;
Zan yabe ka da garaya saboda amincinka, ya Allah; zan rera yabo gare ka da molo, Ya Mai Tsarki na Isra’ila.
23 My lips shall make a joyful noise, When I make music unto thee, And my soul which thou hast ransomed;
Leɓunana za su yi sowa don farin ciki sa’ad da na rera yabo gare ka, ni, wanda ka fansa.
24 Even my tongue, all the day, shall softly utter thy righteousness, For they have turned pale—for they have blushed, Who were seeking my hurt.
Harshena zai ba da labarin ayyukanka masu adalci dukan yini, gama waɗanda suka so su cutar da ni sun sha kunya suka kuma rikice.

< Psalms 71 >