< Psalms 18 >

1 To the chief Musician. Of the servant of Yahweh, of David, —who spake unto Yahweh the words of this song, —in the day when Yahweh had rescued him out of the hand of all his enemies, and out of the hand of Saul; and he said: — I will love thee, O Yahweh my strength!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Ya rera ta ga Ubangiji kalmomin wannan waƙa sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa da kuma daga hannun Shawulu, ya ce, Ina ƙaunarka, ya Ubangiji, ƙarfina.
2 Yahweh, was my mountain crag and my stronghold, and my deliverer: My GOD, was my rock, I sought refuge in him, My shield, and my horn of salvation, my high tower.
Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona; Allahna shi ne dutsena, a gare shi nake neman mafaka. Shi ne garkuwata da ƙahon cetona, mafakata.
3 As one worthy to be praised, called I on Yahweh, —And, from my foes, was I saved.
Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa kuɓuta daga abokan gābana.
4 The meshes of death encompassed me, The torrents of perdition, made me afraid;
Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni; rigyawan hallaka sun sha kaina.
5 The meshes of hades, had surrounded me, The snares of death, had confronted me, (Sheol h7585)
Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe kewaye da ni; tarkon mutuwa ya yi mini arangama. (Sheol h7585)
6 In my distress, called I on Yahweh, And, unto my God, made outcry for help, He heard, out of his temple, my voice, And my outcry for help came before him—entered into his ears!
Cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; Na yi kuka ga Allahna don taimako. A Haikalinsa ya ji muryata, Kukana na neman taimako ya kai kunnensa.
7 Then did the earth shake and quake, Even, the foundations of the mountains, were deeply moved, Yea they did shake, because he was angry.
Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, tussan duwatsu sun girgiza; sun yi rawa domin ya yi fushi.
8 There went up smoke in his nostrils, and, a fire out of his mouth, devoured, Live coals, were kindled from it:
Hayaƙi ya tashi daga kafan hancinsa; wuta mai ci daga bakinsa, garwashi wuta mai ci daga bakinsa.
9 Then he stretched out the heaven, and came down, —and, thick gloom, was under his feet;
Ya buɗe sammai ya sauko; baƙaƙen gizagizai suna a ƙarƙashin ƙafafunsa.
10 Then he rode on a cherub, and flew, and darted on the wings of the wind;
Ya hau kerubobi ya kuma yi firiya; ya yi shawagi a fikafikan iska.
11 Made darkness his hiding-place, Round about him—his pavilion, Darkness of waters, clouds of vapours.
Ya mai da duhu abin rufuwarsa, rumfa kewaye da shi, baƙaƙen gizagizan ruwan sama na sarari,
12 Out of the brightness before him, his clouds rolled along, hail, and live coals of fire.
daga cikin hasken kasancewarsa gizagizai suka yi gaba, da ƙanƙara da kuma walƙiya.
13 Then did Yahweh thunder in the heavens, and the Highest uttered his voice, —hail, and live coals of fire.
Ubangiji ya yi tsawa daga sama; muryar Mafi Ɗaukaka ya yi kāra.
14 And he sent forth his arrows and scattered them, yea, lightnings, he shot out, and confused them.
Ya harba kibiyoyinsa ya kuma watsar da abokan gāba, walƙiya mai girma ya fafare su.
15 Then appeared the channels of waters, were uncovered the foundations of the world, —At thy rebuke O Yahweh, at the blast of the breath of thy nostrils.
Kwarin teku sun bayyana tussan duniya sun bayyana a fili sa’ad da ka tsawata, ya Ubangiji, sa’ad da ka numfasa daga hancinka.
16 He sent from on high, he took me, —he drew me out of many waters.
Ya miƙa hannunsa daga sama ya kama ni; ya ja ni daga zurfin ruwaye.
17 He rescued me from my foe, in his might, and from them who hated me, because they were too strong for me:
Ya cece ni daga abokin gābana mai ƙarfi, daga abokan gābana, waɗanda suka fi ƙarfina.
18 They confronted me, in the day of my necessity, Then became Yahweh my stay:
Sun yi arangama da ni a ranar masifa, amma Ubangiji ya zama mai taimakona.
19 And brought me out, into a large place, he delivered me, because he delighted in me.
Ya fitar da ni zuwa wuri mai sarari; ya kuɓutar da ni, gama yana jin daɗina.
20 Yahweh rewarded me according to my righteousness, According to the cleanness of my hands, he repaid me;
Ubangiji ya yi haka da ni bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya ba ni lada.
21 For I had kept the ways of Yahweh, and not broken away from my God;
Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi mugunta ta wurin juyewa daga Allahna ba.
22 For, all his regulations, were before me, and, his statutes, did I not put from me:
Dukan dokokinsa suna a gābana; ban juye daga ƙa’idodinsa ba.
23 So became I blameless with him, and kept myself from mine iniquity.
Na kasance marar laifi a gabansa na kuma kiyaye kaina daga zunubi.
24 Yahweh therefore repaid me according to my righteousness, according to the pureness of my hands, before his eyes.
Ubangiji ya ba ni lada bisa ga adalcina, bisa ga tsabtan hannuwana a gabansa.
25 With the loving, thou didst show thyself loving, —With the blameless man, thou didst show thyself blameless;
Ga mai aminci ka nuna kanka mai aminci, ga marar laifi ka nuna kanka marar laifi,
26 With the pure, thou didst show thyself pure, But, with the perverse, thou didst show thyself ready to contend.
ga mai tsabta ka nuna kanka mai tsabta, amma ga karkatacce, ka nuna kanka mai wayo.
27 For, as for thee, an oppressed people, thou didst save, but, looks that were lofty, layedst thou low;
Kakan cece mai sauƙinkai amma kakan ƙasƙantar da masu girman kai.
28 For, thou, didst light up my lamp, Yahweh my God, enlightened my darkness;
Kai Ya Ubangiji, ka sa fitilata ta yi ta ci; Allahna ya mai da duhu ya zama haske.
29 For, by thee, I ran through a troop, and, by my God, I leapt over a wall.
Da taimakonka zan iya fāɗa wa runduna; tare da Allahna zan iya rinjayi katanga.
30 As for GOD, blameless is his way, The speech of Yahweh hath been proved, A shield, he is to all who seek refuge in him.
Game da Allah kuwa, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji marar kuskure ne. Shi garkuwa ne ga dukan waɗanda suke neman mafaka a gare shi.
31 For who is a GOD, save Yahweh? And who is a Rock, save our God?
Gama wane ne Allah in ba Ubangiji ba? Wane ne kuwa Dutse in ba Allahnmu ba?
32 The GOD who girded me with strength, and set forth, as blameless, my way:
Allah ne ya ƙarfafa ni da ƙarfi ya kuma sa hanyarta ta zama cikakkiya.
33 Planting my feet like hinds’ [feet], yea, on my high places, he caused me to stand:
Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsaya a kan ƙwanƙoli.
34 Teaching my hands to war, —so that a bow of bronze was bent by mine arms.
Ya horar da hannuwana don yaƙi; hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
35 Thus didst thou grant me, as a shield, thy salvation, —and, thy right hand, sustained me, and, thy condescension, made me great.
Ka ba ni garkuwar nasara, kuma hannunka na dama yana riƙe ni; ya sunkuya don ka mai da ni mai girma.
36 Thou didst widen my stepping-places under me, so that, mine ankles, faltered not.
Ka fadada hanyar da yake a ƙarƙashina, don kada ɗiɗɗigena yă juya.
37 I pursued my foes, and overtook them, and returned not, till they were consumed:
Na bi abokan gābana na kuma cim musu; ban juya ba sai da na hallaka su.
38 I crushed them, and they were unable to rise, They fell under my feet.
Na ragargaza su har ba za su iya tashi ba; sun fāɗi a ƙarƙashin ƙafafuna.
39 Thus didst thou gird me with strength, for the battle, Thou subduedst mine assailants under me.
Ka ƙarfafa ni da ƙarfi saboda yaƙi; ka sa abokan gābana suka rusuna mini.
40 As for my foes, thou didst give me their neck, and, as for them who hated me, I destroyed them.
Ka sa abokan gābana suka juya suka gudu, na kuma hallaka abokan gābana.
41 They cried out, but there was none to save, unto Yahweh, but he answered them not.
Sun nemi taimako, amma ba su sami wanda zai cece su ba, ga Ubangiji, amma bai amsa ba.
42 Then did I beat them in pieces, like dust on the face of the wind. Like the mire in the lanes, did I scatter them.
Na murƙushe su kamar ƙura mai laushi da iska ke kwashewa; na zubar da su kamar laka a tituna.
43 Thus didst thou rescue me from the contentions of a people, —didst appoint me to be the head of nations, A people I had not known, served me:
Ka cece ni daga harin mutane; ka mai da ni kan al’ummai. Mutanen da ban sani ba sun zama bayina,
44 At the hearing of the ear, they submitted to me, the sons of the foreigner, came cringing unto me:
da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya; baƙi suna rusuna a gabana.
45 The sons of the foreigner, lost heart, and came quaking out of their fortresses.
Duk sukan karai; suna zuwa da rawan jiki daga mafakansu.
46 Yahweh liveth and, blessed, be my Rock, yea, exalted, be the God of my salvation:
Ubangiji mai rai ne! Yabo ya tabbata ga Dutsena! Girma ya tabbata ga Allah Mai cetona!
47 The GOD, who hath avenged me, —and subjugated peoples under me:
Shi ne Allah mai sāka mini, wanda yake sa al’ummai a ƙarƙashina,
48 Who hath delivered me from my foes, —Yea, from mine assailants, hast thou set me on high, From the man of violence, hast thou rescued me.
wanda yakan cece ni daga abokan gābana. Ana girmama ka bisa abokan gābana; daga masu tā-da-na-zaune-tsaye ka kuɓutar da ni.
49 For this cause, will I praise thee among the nations, O Yahweh, and, to thy Name, will I sweep the strings: —
Saboda haka zan yabe ka a cikin al’ummai, ya Ubangiji; zan rera yabai ga sunanka.
50 Who hath made great the victories of his King, —and shown lovingkindness to his Anointed One, To David and to his Seed, Unto times age-abiding.
Yakan ba sarkinsa nasarori; yakan nuna alheri marar ƙarewa ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.

< Psalms 18 >