< Psalms 130 >

1 A Song of Ascents. Out of the depths, have I cried unto thee, O Yahweh.
Waƙar haurawa. Daga cikin zurfafa na yi kuka gare ka, ya Ubangiji;
2 O My Lord! hearken thou unto my voice, —Let thine ears be attentive to the voice of my supplications,
Ya Ubangiji, ka ji muryata. Bari kunnuwanka su saurara ga kukata ta neman jinƙai.
3 If, iniquities, thou shouldest mark, O Yah, O My Lord, who could stand?
In kai, ya Ubangiji, za ka lissafta zunubai, Ya Ubangiji, wa zai tsaya?
4 But, with thee, is forgiveness, that thou mayest be revered.
Amma tare da kai akwai gafartawa, saboda haka ake tsoronka.
5 I have waited for Yahweh, My soul hath waited for his word;
Zan jira Ubangiji, raina zai jira, kuma a cikin maganarsa na sa zuciyata.
6 I have hoped, O my soul, for My Lord, more than they who watch for the morning, who watch for the morning.
Raina na jiran Ubangiji fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya, fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya.
7 Wait, O Israel, for Yahweh, —for, with Yahweh, is lovingkindness, and there aboundeth with him—redemption.
Ya Isra’ila, sa zuciya ga Ubangiji, gama tare da Ubangiji akwai ƙauna marar ƙarewa kuma tare da shi akwai cikakkiyar fansa.
8 He, therefore, will redeem Israel from all his iniquities.
Shi kansa zai fanshi Isra’ila daga dukan zunubansu.

< Psalms 130 >