< Psalms 108 >

1 A Song, a Melody: David’s. Fixed, is my heart, O God, I will sing and touch the strings, even mine honour.
Waƙa ce. Zabura ta Dawuda. Zuciyata tsayayyiya ce, ya Allah; zan rera in kuma yi kiɗi da dukan raina.
2 Awake, O harp and lyre, I will awaken the dawn!
Ku farka, garaya da molo! Zan farkar da rana.
3 I will thank thee among the peoples, O Yahweh, and will sing praise unto thee, among the tribes of men.
Zan yabe ka, ya Ubangiji, a cikin al’ummai; zan rera game da kai cikin mutane.
4 For, great, above the heavens, is thy lovingkindness, and, as far as the skies, thy faithfulness.
Gama ƙaunarka da girma take, bisa fiye da sammai; amincinka ya kai sarari.
5 Be thou exalted above the heavens, O God, And, above all the earth, be thy glory.
A ɗaukaka ka, ya Allah, a bisa sammai, bari kuma ɗaukakarka ta kasance a bisa dukan duniya.
6 To the end thy beloved ones may be delivered, Oh save thou with thy right hand and answer me!
Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.
7 God, hath spoken in his holiness, I will exult! I will apportion Shechem! And, the Vale of Succoth, will I measure out;
Allah ya yi magana daga wurinsa mai tsarki, “Ciki nasara zan raba Shekem in kuma auna Kwarin Sukkot.
8 Mine, is Gilead—mine, Manasseh, but, Ephraim, is the defence of my head, Judah, is my commander’s staff;
Gileyad nawa ne, Manasse nawa ne; Efraim shi hulan kwanona, Yahuda ne sandana na sarauta.
9 Moab, is my wash-bowl, Upon Edom, will I throw my shoe, Over Philistia, raise a shout of triumph.
Mowab shi ne kwanon wankina, a kan Edom zan jefa takalmina; a bisa Filistiya zan yi kirari cikin nasara.”
10 Who will conduct me to a fortified city? Who will lead me as far as Edom?
Wa zai kawo ni birni mai katanga? Wa zai jagorance ni zuwa Edom?
11 Hast not thou, O God, rejected us? and wilt not go forth, O God, with our hosts.
Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
12 Grant us help out of distress, for, vain, is the deliverance of man:
Ka ba mu taimako a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
13 In God, shall we do valiantly, He himself, therefore, shall tread down our adversaries.
Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattaka abokan gābanmu.

< Psalms 108 >