< Obadiah 1 >

1 The vision of Obadiah, —Thus, saith My Lord, Yahweh, concerning Edom—A rumour, have we heard from Yahweh, and, a herald, throughout the nations, hath been sent, Up! and let us rise against her to war.
Wahayin Obadiya. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce a kan Edom. Mun ji saƙo daga wurin Ubangiji cewa, An aiki jakada zuwa ga al’ummai yă faɗa musu cewa, “Ku tashi, mu tafi mu yi yaƙi da ita.”
2 Lo! small, have I made thee, among the nations—Despised art thou exceedingly!
“Duba, zan maishe ki ƙarama a cikin al’ummai; za a rena ki ƙwarai.
3 The insolence of thy heart, hath deceived thee, O thou that inhabitest the retreats of the crag, the height of his habitation, —that saith in his heart, Who shall bring me down to the ground?
Fariyar zuciyarki ta yaudare ki, ke da kike zama can bisa duwatsu kika kuma yi gidanki a kan ƙwanƙoli, ke da kike ce wa kanki, ‘Wa zai iya saukar da ni ƙasa?’
4 Though thou build high like an eagle, and though, among the stars, thou set thy nest, from thence, will I bring thee down, Declareth Yahweh.
Ko da yake kina firiya kamar gaggafa kin kuma yi sheƙarki a can cikin taurari, daga can zan saukar da ke,” in ji Ubangiji.
5 If, thieves, had come to thee, if robbers by night—how ruined thou art! Would they not have stolen what sufficed them? If, grape-gatherers, had come to thee, Would they not have left gleanings?
“In ɓarayi suka zo miki, in kuma’yan fashi suka shigo gidan da dare, kash, bala’i zai jira ki ba abin da suke so ne kawai za su sata ba? In kuma masu tsinka’ya’yan inabi suka zo miki, ba sukan bar’ya’yan inabi kaɗan ba?
6 How have the things of Esau been searched out! his treasures been sought up!
Amma za a washe Isuwa ƙaƙaf, a kuma yaye ɓoyayyiyar dukiyarsa!
7 Up to the boundary, have they sent thee—All thy covenant men, they have deceived thee, prevailed against thee—the men thou wast wont to salute, —The partakers of thy bread, have put a net under thee—No understanding in him!
Dukan waɗanda kike tarayya da su, za su kore ki zuwa iyaka; abokanki kuma za su yaudare ki, su kuma sha ƙarfinki; waɗanda suke cin abincinki, za su sa miki tarko, amma ba za ki gane ba.
8 Shall it not be, in that day, Demandeth Yahweh, —That I will destroy the wise men out of Edom, and understanding out of Mount Esau?
“A wannan rana,” in jin Ubangiji, “zan hallaka masu hikimar Edom, zan shafe mutane masu fahima a duwatsun Isuwa.
9 So shall thy mighty men, O Teman, be dismayed, —to the intent that every man, may be cut off, out of Mount Esau, by slaughter.
Jarumawanki, ya Teman, za su razana, za a kashe kowane mutum a duwatsun Isuwa.
10 For thy violence against thy brother Jacob, shall shame, cover thee, —so shalt thou be cut off, to times age-abiding.
Saboda halin kama-karyar da kika yi wa ɗan’uwanka Yaƙub, za ki sha kunya; za a hallaka ki har abada.
11 In the day when thou didst take thy stand over against him, in the day when foreigners took captive his forces, —and, aliens, entered his gates, and, over Jerusalem, cast lots, even thou, wast like one of them!
A ranan nan kin tsaya kawai kina zuba ido yayinda baƙi suke washe dukiyar ɗan’uwanki, baƙi kuma suka shiga ta ƙofofinsa suka jefa ƙuri’a don a rarraba Urushalima, kin tsaya kina kallo kamar ɗaya daga cikin abokan gābansa.
12 Do not, then, look with satisfaction upon the day of thy brother, upon the day of his calamity, Neither rejoice over the sons of Judah—in the day of their ruin, —nor enlarge thy mouth—in the day of distress:
Bai kamata ki rena ɗan’uwanki a ranar masifarsa ba, ko ki yi farin ciki a kan mutanen Yahuda a ranar hallakarsu, ko ki yi fariya sosai a ranar wahalarsu.
13 Do not enter into the gate of my people—in the day of their misfortune, Do not, thou also, look with satisfaction on his misery—in the day of his misfortune; neither do thou thrust [thy hands] on his substance—in the day of his misfortune;
Bai kamata ki bi ta ƙofofin mutanena a ranar bala’insu ba, ko ki rena su a cikin masifarsu a ranar bala’insu, ko ki ƙwace dukiyarsu a ranar bala’insu ba.
14 Neither do thou stand at the parting of the way, to cut off his fugitives, —neither do thou deliver up his survivors—in the day of distress.
Bai kamata ki tsaya a mararraba don ki kashe waɗanda suke ƙoƙarin tserewa ba, ko ki ba da waɗanda suka tsere ga hannun maƙiyansu a ranar wahalarsu ba.
15 For, near, is the day of Yahweh, upon all the nations, —Just as thou hast done, shall it be done to thee, Thy dealing, shall come back upon thine own head.
“Ranar Ubangiji ta yi kusa don dukan al’ummai. Kamar yadda kuka yi, haka za a yi muku; ayyukanku za su koma a kanku.
16 For, as ye have drunk on my holy mountain, all the nations shall drink continually, —Yea they shall drink and swallow down, and shall be, as though they had not been.
Kamar yadda kuka sha a kan tuduna mai tsarki, haka dukan al’ummai za su yi ta sha, za su sha, su kuma sha su zama sai ka ce ba su taɓa kasancewa ba.
17 But, in Mount Zion, shall be a delivered remnant which shall be holy, —and the house of Jacob shall possess their own possessions;
Amma a kan Dutsen Sihiyona za a sami ceto; Dutsen zai zama mai tsarki, gidan Yaƙub kuma zai mallaki gādonsa.
18 And the house of Jacob shall be a fire, and the house of Joseph a flame, with the house of Esau for stubble, So shall they kindle upon them, and devour them, —and there shall be no survivor to the house of Esau, for, Yahweh, hath spoken.
Gidan Yaƙub zai zama kamar wuta, gidan Yusuf kuma kamar harshen wuta; gidan Isuwa zai zama kamar tattaka, za a kuma sa masa wuta yă ƙone. Babu wanda zai tsira daga gidan Isuwa.” Ni Ubangiji na faɗa.
19 Then shall they of the South possess Mount Esau, and they of the Lowlands, the Philistines, and they [of the Mountain] shall possess the field of Ephraim, and the field of Samaria, —and Benjamin [shall possess] Gilead;
Mutane daga Negeb za su mamaye duwatsun Isuwa, mutane kuma daga gindin tuddai za su mallaki ƙasar Filistiyawa. Za su mamaye filayen Efraim da Samariya, Benyamin kuwa zai mallaki Gileyad.
20 And, they of the captivity of this force pertaining to the sons of Israel, [shall possess] that of the Canaanites, up to Zarephath, and, they of the captivity of Jerusalem who are in Sepharad, shall possess the cities of the South.
Wannan ƙungiyar Isra’ilawan da aka kwashe zuwa bauta da suke a Kan’ana za su mallaki ƙasar har zuwa Zarefat; waɗannan da aka kwashe zuwa bauta daga Urushalima da suke a Sefarad za su mallaki garuruwan Negeb.
21 And saviours shall come up in Mount Zion, to judge the mountain of Esau, —So shall the kingdom, belong unto Yahweh.
Masu kawo ceto za su haura zuwa Dutsen Sihiyona don su yi mulkin duwatsun Isuwa. Ubangiji ne zai yi mulki.

< Obadiah 1 >