< Nehemiah 10 >

1 Now, upon the sealed writings, were, —Nehemiah the governor, son of Hacaliah, and Zedekiah;
Waɗanda suka buga hatimin su ne, Nehemiya ɗan Hakaliya, wanda yake gwamna. Zedekiya
2 Seraiah, Azariah, Jeremiah;
da Serahiya, da Azariya, da Irmiya,
3 Pashhur, Amariah, Malchijah;
da Fashhur, da Amariya, da Malkiya,
4 Hattush, Shebaniah, Malluch;
da Hattush, da Shebaniya, da Malluk,
5 Harim, Meremoth, Obadiah;
da Harim, da Meremot, da Obadiya,
6 Daniel, Ginnethon, Baruch;
da Daniyel, da Ginneton, da Baruk,
7 Meshullam, Abijah, Mijamin;
da Meshullam, da Abiya, da Miyamin,
8 Maaziah, Bilgai, Shemaiah, —these, were, the priests.
da Ma’aziya, da Bilgai, da kuma Shemahiya. Waɗannan su ne Firistocin.
9 And, the Levites, —Jeshua, son of Azaniah, Binnui, of the sons of Henadad, Kadmiel;
Lawiyawan kuwa su ne, Yeshuwa ɗan Azaniya, da Binnuyi ɗan Henadad, da Kadmiyel,
10 and, their brethren, —Shebaniah, Hodiah, Kelita, Pelaiah, Hanan;
’yan’uwansu kuwa su ne, Shebaniya, da Hodiya, da Kelita, da Felahiya, da Hanan,
11 Mica, Rehob, Hashabiah;
da Mika, da Rehob, da Hashabiya,
12 Zaccur, Sherebiah, Shebaniah;
da Zakkur, da Sherebiya, da Shebaniya,
13 Hodiah, Bani, Beninu.
da Hodiya, da Bani da kuma Beninu.
14 The heads of the people, —Parosh, Pahath-moab, Elam, Zattu, Bani;
Shugabannin mutane su ne, Farosh, da Fahat-Mowab, da Elam, da Zattu, da Bani,
15 Bunni, Azgad, Bebai;
da Bunni, da Azgad, da Bebai,
16 Adonijah, Bigvai, Adin;
da Adoniya, da Bigwai, da Adin,
17 Ater, Hezekiah, Azzur;
da Ater, da Hezekiya, da Azzur,
18 Hodiah, Hashum, Bezai;
da Hodiya, da Hashum, da Bezai,
19 Hariph, Anathoth, Nobai;
da Harif, da Anatot, da Nebai,
20 Magpiash, Meshullam, Hezir;
da Magfiyash, da Meshullam, da Hezir,
21 Meshezabel, Zadok, Jaddua;
da Meshezabel, da Zadok, da Yadduwa
22 Pelatiah, Hanan, Anaiah;
da Felatiya, da Hanan, da Anahiya,
23 Hoshea, Hananiah, Hasshub;
da Hosheya, da Hananiya, da Hasshub,
24 Hallohesh, Pilha, Shobek;
da Hallohesh, da Filha, da Shobek,
25 Rehum, Hashabnah, Maaseiah;
da Rehum, da Hashabna, da Ma’asehiya
26 and Ahiah, Hanan, Anan;
da Ahiya, da Hanan, da Anan,
27 Malluch, Harim, Baanah.
da Malluk, da Harim da kuma Ba’ana.
28 And, the rest of the people—the priests, the Levites, the doorkeepers, the singers, the Nethinim, and all who had separated themselves from the peoples of the lands unto the law of God, their wives, their sons and their daughters, —every one having knowledge and understanding,
“Sauran mutane, wato, firistoci, Lawiyawa, matsaran ƙofofi, mawaƙa, ma’aikatan haikali da dukan waɗanda suka ware kansu daga maƙwabta saboda Dokar Allah, tare da matansu da dukan’ya’yansu maza da mata waɗanda za su iya fahimta,
29 were holding fast unto their distinguished brethren, and were entering into a curse and into an oath, to walk in the law of God, which was given through Moses the servant of God, —and to observe and do, all the commandments of Yahweh our Lord, and his regulations, and his statutes;
dukan waɗannan yanzu suka sadu da manyan gari’yan’uwansu, suka rantse, cewa la’ana ta same su idan ba su kiyaye Dokar Allah da aka bayar ta wurin Musa bawan Allah su kuma mai da hankali ga yin biyayya da dukan umarnai, ƙa’idodi da farillan Ubangiji shugabanmu ba.
30 and that we would not give our daughters unto the peoples of the land, —and, their daughters, would we not take for our sons;
“Mun yi alkawari ba za mu ba da’ya’yanmu mata aure ga mutanen da suke kewaye da mu ba, ba kuwa za mu auri’ya’yansu mata wa’ya’yanmu maza ba.
31 and, if the peoples of the land should be bringing in wares, or any corn on the sabbath day, to sell, we would not buy of them on the sabbath, or on a holy day, —and that we would remit the seventh year, and the loan of every hand.
“Sa’ad da maƙwabta suka kawo kayayyaki ko hatsi don su sayar a ranar Asabbaci, ba za mu saya daga gare su a ranar Asabbaci ko a rana mai tsarki ba. Kowace shekarar Asabbaci ba za mu nome ƙasa ba kuma za mu yafe kowane irin bashi.
32 And we laid on ourselves charges, appointing for ourselves the third of a shekel, yearly, —for the service of the house of our God:
“Mun ɗauka hakkin bin umarnai na ba da kashi ɗaya bisa uku na shekel kowace shekara don hidimar gidan Allahnmu.
33 for the bread to set in array, and the continual meal-offering, and for the continual ascending-sacrifice, of the sabbaths, of the new moons, for the appointed feasts, and for things hallowed, and for victims bearing sin, to put a propitiatory-covering over Israel, —and for all the work of the house of our God.
Za mu tanada burodin da ake ajiye a kan tebur; za mu ba da hadayun hatsi da hadayun ƙonawa na kullum; za mu ba da hadayun Asabbatai, da na bukukkuwan Sabon Wata da na bukukkuwan da aka ƙayyade; za mu ba da hadayu masu tsarki; za mu ba da hadayun zunubi don a yi kafara domin Isra’ila; mu kuma ba da abubuwan da ake bukata dukan domin ayyukan gidan Allahnmu.
34 Also, lots, did we cast, concerning the offering of wood among the priests, the Levites, and the people, to bring it unto the house of our God, by our ancestral houses, at times arranged, year by year, —to burn upon the altar of Yahweh our God, as it is written in the law.
“Mu, firistoci, da Lawiyawa da kuma mutane, mun jefa ƙuri’a don a san lokacin da kowane iyalinmu zai kawo sadakar itace don ƙonewa a gidan Allahnmu a ƙayyadaddun lokuta a bagaden Ubangiji Allahnmu, kamar yadda yake a rubuce a cikin Doka.
35 And that we would bring in the firstfruits of our ground, and the firstfruit of all fruit of all trees, year by year, —unto the house of Yahweh;
“Mun kuma ɗauka hakkin kawo nunan fari na hatsinmu da kuma na kowane itace mai ba da’ya’ya a gidan Ubangiji kowace shekara.
36 also that, the firstborn of our sons, and of our cattle, as it is written in the law, —and the firstlings of our herds and of our flocks, we would bring in unto the house of our God, unto the priests who should be in attendance in the house of our God;
“Kamar yadda yake a rubuce a cikin Doka, za mu kawo ɗan fari na’ya’yanmu maza da na garken shanunmu, da na tumakinmu, da kuma na awakinmu a gidan Allahnmu, don firistocin da suke aikin a can.
37 and, the first part of our meal and our heave-offerings and the fruit of all trees, new wine and oil, would we bring in unto the priests, into the chambers of the house of our God, and the tithe of our ground unto the Levites, —the Levites themselves, taking the tithes in all our cities of agriculture.
“Ban da haka ma, za mu kawo wa ɗakunan ajiyar gidan Allahnmu, abincinmu na farko daga ƙasa, na hadayun hatsinmu, na’ya’yan dukan itatuwanmu da kuma na sabon ruwan inabinmu da mai namu wa firistoci. Za mu kuma kawo zakkar hatsinmu wa Lawiyawa, gama Lawiyawa ne ke karɓan Zakka cikin dukan garuruwan da muke noma.
38 And the priest the son of Aaron should be with the Levites, when the Levites should take the tithes, —and the Levites, should bring up the tithe of the tithe, unto the house of our God, into the chambers pertaining unto the treasure-house.
Firist wanda yake daga zuriyar Haruna zai raka Lawiyawa sa’ad da suke karɓan zakka, Lawiyawan kuma za su kawo kashi ɗaya bisa goma na zakka zuwa gidan Allahnmu, su kawo a ɗakunan ajiya na baitulmali.
39 For, into the chambers, should the sons of Israel and the sons of Levi bring in the heave-offering of the corn, the new wine and the oil, since, there, are the utensils of the sanctuary, and the priests who are in attendance, and the doorkeepers, and the singers, —so would we not neglect the house of our God.
Mutanen Isra’ila haɗe da Lawiyawa, za su kawo sadakokinsu na hatsi, sabon ruwan inabi da mai a ɗakunan ajiya inda ake ajiyar kayayyakin wuri mai tsarki da kuma inda firistoci, matsaran ƙofofi da kuma mawaƙa suke zama. “Ba za mu ƙyale gidan Allahnmu ba.”

< Nehemiah 10 >