< Luke 5 >

1 And it came to pass, while the multitude was pressing upon him, and was hearing the word of God, that, he, was standing near the lake of Gennesaret;
Wata rana, Yesu yana tsaye a bakin Tafkin Gennesaret, mutane kuma suna ta matsawa kewaye da shi, domin su ji maganar Allah,
2 and he saw two boats placed near the lake, and, the fishers, having gone away, from them, were washing their nets.
sai ya hangi jiragen ruwa biyu a bakin tafkin, waɗanda masu kamun kifi suka bari suna wankin abin kamun kifinsu.
3 And, entering into one of the boats, which was Simon’s, he requested him, to put off from the land, a little; and, taking a seat, out of the boat, began he teaching the multitudes.
Sai ya shiga ɗaya jirgin ruwan da yake na Siman, ya kuma roƙe shi yă tura shi kaɗan daga gaci. Sai ya zauna a jirgin ruwan, ya koyar da mutane daga ciki.
4 And, when he ceased speaking, he said unto Simon—Put off into the deep, and let down your nets for a draught.
Da ya gama magana, sai ya ce wa Siman, “Ka tuƙa jirgin zuwa inda akwai zurfi, ka saukar da abin kamun kifinka ka kama kifi.”
5 And Simon, answering, said—Master! although through the whole night we toiled, we took, nothing; howbeit, at thy bidding, I will let down the nets.
Siman ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, duk dare mun yi ta fama ba mu kama kome ba, amma tun da ka ce haka, zan saki abin kamun kifin.”
6 And, when this they had done, they enclosed a very large number of fishes, and their nets began to break.
Da suka yi haka, sai suka kama kifi da yawa, har abin kamun kifinsu suka fara tsintsinkewa.
7 And they made signs to their partners in the other boat, to come and help them; and they came, and filled both the boats, —so that they began to sink.
Sai suka kira abokansu a ɗaya jirgin, su zo su taimake su, suka kuwa zo. Suka cika jiragen biyu da kifi cif, har jiragen suka fara nutsewa.
8 And Simon, beholding, fell down at the knees of Jesus, saying—Depart from me! Because, a sinful man, am I, O Lord!
Da Siman Bitrus ya ga wannan, sai ya fāɗi a gaban Yesu ya ce, “Rabu da ni, Ubangiji. Ni mai zunubi ne!”
9 For, amazement, overcame him, and all them who were with him, on account of the draught of the fishes which they had taken;
Gama mamaki ya kama shi da abokansa duka, saboda yawan kifin da suka kama.
10 likewise also, both James and John, sons of Zebedee, who were partners with Simon. And Jesus said unto Simon—Do not fear! henceforth, shall thou be taking, men, that they may, live.
Yaƙub da Yohanna,’ya’yan Zebedi, abokan aikin Siman su ma suka yi mamaki. Sai Yesu ya ce wa Siman, “Kada ka ji tsoro, daga yanzu za ka riƙa kama mutane ne.”
11 And, bringing the boats down on to the land, they left all, and followed him.
Sai suka jawo jiragen ruwansu zuwa gaci, suka bar kome da kome, suka bi shi.
12 And it came to pass, while he was in one of the cities, that lo! there was a man full of leprosy; and, seeing Jesus, he fell on his face, and entreated him, saying—Lord! if thou be willing, thou canst cleanse me.
Yayinda Yesu yake ɗaya daga cikin garuruwan nan, sai ga wani mutum wanda kuturta ta ci ƙarfinsa. Da ganin Yesu, sai ya fāɗi da fuskarsa a ƙasa, ya roƙe shi ya ce, “Ubangiji, in ka yarda, kana iya ka tsabtacce ni.”
13 And, stretching forth the hand, he touched him, saying—I am willing: Be cleansed! And, straightway, the leprosy departed from him.
Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin ya ce, “Na yarda, ka zama da tsabta!” Nan da nan, sai kuturtar ta rabu da shi.
14 And, he, charged him to tell, no one, —but, departing, Show thyself to the priest, and offer for thy cleansing, according as Moses enjoined, for a witness unto them.
Sai Yesu ya umarce shi ya ce, “Kada ka gaya wa kowa, amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, ka kuma miƙa hadayu da Musa ya umarta, saboda tsarkakewarka ta zama shaida a gare su.”
15 But the report concerning him the more went abroad, and many multitudes were coming together, to hear, and be getting cured from their infirmities;
Duk da haka, labarinsa ya ƙara bazuwa sosai, har taron mutane suka dinga zuwa don jinsa, da kuma neman warkarwa daga cututtukansu.
16 howbeit, he, was retiring in the deserts, and engaging in prayer.
Amma Yesu sau da yawa, yakan keɓe kansa zuwa wuraren da ba kowa, yă yi addu’a.
17 And it came to pass, on one of the days, that, he, was teaching, and there were sitting Pharisees and Teachers of the law, who had come out of every village of Galilee and Judaea and Jerusalem; and, the power of the Lord, was there, that he might heal.
Wata rana, da yake cikin koyarwa, waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki waɗanda suka zo daga kowane ƙauye a Galili, Yahudiya da Urushalima kuwa suna zaune. Ikon Ubangiji yana nan don yă warkar da masu ciwo.
18 And lo! men bearing, upon a couch, one who was paralyzed, and they were seeking to bring him in, and lay him before him.
Sai ga waɗansu mutane suka kawo wani shanyayye a kan tabarma. Suka yi ƙoƙari su shigar da shi cikin gidan, domin su kwantar da shi a gaban Yesu.
19 And, not finding by what means they might bring him in, because of the multitude, going up on the house-top, through the tiling, let they him down, with the little-couch, into the midst before Jesus.
Da suka ga babu hanyar da za su bi saboda taron, sai suka haura rufin, suka saukar da shi a kan tabarmarsa, ta bakin ramin da suka huda a rufin, suka ajiye shi a tsakiyar taron, a gaban Yesu.
20 And, beholding their faith, he said—O man! thy sins are forgiven thee.
Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce, “Saurayi, an gafarta maka zunubanka.”
21 And the Scribes and the Pharisees began to reason, saying—Who is this that speaketh profanities? Who can forgive, sins, save, God alone?
Farisiyawa da malaman dokoki suka fara yin tunani a zukatansu, “Wane ne wannan mutum da yake saɓo haka? Wa zai iya gafarta zunubai, in ba Allah kaɗai ba?”
22 And Jesus, taking note of their reasonings, answering, said unto them—Why are ye reasoning in your hearts?
Yesu ya san abin da suke tunani, sai ya yi tambaya ya ce, “Don me kuke tunanin waɗannan abubuwa a zukatanku?
23 Which is easier, To say—Thy sins are forgiven thee; or to say—Arise and be walking?
Wanne ya fi sauƙi, a ce, ‘An gafarta maka zunubanka,’ ko kuma a ce, ‘Tashi, ka yi tafiya’?
24 But, that ye may know that, the Son of Man, hath, authority, upon the earth to forgive sins—he said to the paralyzed man—To thee, I say, Arise, and, taking up thy couch, be going thy way unto thy house.
Amma domin ku san cewa Ɗan Mutum yana da iko a duniya ya gafarta zunubai.” Sai ya ce wa shanyayyen, “Na ce maka, tashi, ɗauki tabarmarka ka tafi gida.”
25 And, instantly arising before them, he took up that whereon he had been lying, and departed unto his house, glorifying God.
Nan da nan, ya tashi tsaye a gabansu, ya ɗauki tabarmar da yake kwance a kai, ya tafi gida, yana yabon Allah.
26 And, astonishment, seized one and all, and they began glorifying God, and were filled with fear, saying—We have seen unaccountable things, to-day!
Kowa ya yi mamaki, ya kuma yabi Allah. Suka cika da tsoro, suna cewa, “Mun ga abubuwan banmamaki yau.”
27 And, after these things, he went forth, and looked upon a tax-collector, by name Levi, —presiding over the tax-office; and he said to him—Be following me!
Bayan wannan, sai Yesu ya fita, ya ga wani mai karɓar haraji, mai suna Lawi, yana zaune a wurin da ake karɓar haraji. Yesu ya ce masa, “Bi ni.”
28 And, forsaking all, he arose, and was following him.
Sai Lawi ya tashi, ya bar kome da kome, ya bi shi.
29 And Levi made a great reception for him, in his house, and there was a great multitude of tax-collectors, and others, —who were with them reclining.
Sai Lawi ya shirya wa Yesu wani babban liyafa a gidansa. Wani babban taron na masu karɓar haraji, tare da waɗansu suna cin abinci tare da su.
30 And the Pharisees and their Scribes began murmuring unto his disciples, saying—Wherefore, with the tax-collectors and sinners, are ye eating and drinking?
Amma Farisiyawa da malaman dokokin da suke a ƙungiyarsu, suka yi wa almajiransa gunaguni, suna cewa, “Don me kuke ci, kuke sha tare da masu karɓar haraji da masu zunubi?”
31 And, answering, Jesus said unto them—No need, have, the whole, of a physician, but, they who are sick.
Yesu ya amsa musu ya ce, “Ai, masu lafiya ba sa bukatar likita, sai dai marasa lafiya.
32 I have not come to call, righteous, men, but, sinners, unto repentance.
Ban zo don in kira masu adalci ba, sai dai masu zunubi zuwa ga tuba.”
33 But, they, said unto him—The disciples of John, do fast much, and, supplications, do make, —likewise also the disciples of the Pharisees; but, thine, do eat and drink!
Suka ce masa, “Almajiran Yohanna sukan yi azumi da addu’a, haka ma almajiran Farisiyawa, amma naka sai ci da sha.”
34 Jesus, however, said unto them—Can, ye make, the sons of the bridechamber, fast, while the bridegroom is with them?
Yesu ya amsa ya ce, “Za ku iya sa abokan ango yin azumi yayinda yake tare da su?
35 But there will come days, even when the bridegroom shall be taken from them, then, will they fast, in those days.
Amma lokaci yana zuwa, da za a ɗauke ango daga gare su. A waɗancan kwanakin ne za su yi azumi.”
36 Moreover, he went on to speak, a parable also, unto them—No one, rending a patch from a new mantle, patcheth it upon an old mantle; otherwise, at least, both, the new, he will rend, and, with the old, the patch which is from the new, will not agree.
Sai ya faɗa musu wannan misali ya ce, “Ba wanda yakan yage ƙyalle daga sabuwar riga ya yi wa tsohuwar riga faci. In ya yi haka, zai yage sabuwar rigar, kuma facin daga sabuwar ba zai dace da tsohuwar rigar ba.
37 And, no one, poureth new wine into old skins; otherwise, at least, the new wine, will burst the skins, and will, itself, be poured out, and the skins be destroyed.
Kuma ba wanda yakan zuba sabon ruwan inabi a cikin tsofaffin salkuna. In ya yi haka, sabon ruwan inabi zai farfashe salkunan, ruwan inabin yă zube, salkunan kuma su lalace.
38 But, new wine, into unused skins, must be poured.
A’a, sai dai a zuba sabon ruwan inabi a sababbin salkuna.
39 [No one, having drunk old, desireth new; for he saith, The old, is, mellow.]
Kuma ba wanda yakan so shan sabon ruwan inabi bayan ya sha tsohon, don yakan ce, ‘Ai, tsohon ya fi kyau.’”

< Luke 5 >