< Luke 1 >

1 Seeing, indeed, that, many, had taken in hand to re-arrange for themselves a narrative, concerning the facts which have been fully confirmed amongst us, —
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 according as they who from the beginning became eye-witnesses and attendants of the Word delivered them unto us,
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 it seemed good, even to me, having closely traced from the outset all things accurately, to write unto thee, in order, most excellent Theophilus:
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 that, as touching the matters which thou hadst been taught by word of mouth, thou mightest obtain full knowledge, of the certainty.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 It came to pass, in the days of Herod, king of Judaea, that there was a certain priest, by name Zachariah, of the daily course of Abia; and that he had a wife of the daughters of Aaron, and, her name, was Elizabeth.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 Now they were both righteous before God, walking in all the commandments and righteous appointments of the Lord, blameless;
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 and they had no child, inasmuch as Elizabeth was barren, and, both, had become, advanced in their days.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 But it came to pass, as he was doing priestly service in the order of his daily course, before God,
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 according to the custom of his priesthood, it fell to his lot to offer incense, entering into the Temple of the Lord;
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 and, all the throng of the people, was praying outside, at the hour of the incense offering.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 And there appeared unto him a messenger of the Lord, standing on the right hand of the altar of incense;
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 and Zachariah was troubled when he beheld, and, fear, fell upon him.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 But the messenger said unto him—Do not fear, Zachariah! Inasmuch as thy supplication hath been hearkened to, —and, thy wife Elizabeth, shall bring forth a son to thee, and thou shalt call his name, John;
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 And there shall be joy to thee and exulting, and, many, over his birth, shall rejoice;
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 For he shall be great before the Lord, and, wine and strong drink, in nowise may he drink, and, with Holy Spirit, shall he be filled, already, from his mother’s womb;
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 And, many of the Sons of Israel, shall he turn towards the Lord their God;
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 And, he, shall go before him, in the spirit and power of Elijah, —To turn the hearts of fathers unto children, and the unyielding, into the prudence of the righteous, and to prepare, for the Lord, a people made ready.
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 And Zachariah said unto the messenger—Whereby, shall I know this? for, I, am, aged, and, my wife, advanced in her days.
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 And the messenger, answering, said unto him—I, am Gabriel, —he that standeth near before God; and have been sent forth to speak unto thee, and to deliver the joyful message unto thee, as touching these things.
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 And lo! thou shalt be silent, and not able to speak until the day when these things shall come to pass; because thou didst not believe in my words, —the which shall be fulfilled for their season.
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 And the people were expecting Zachariah, and began to marvel that he should tarry in the Temple;
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 and when he came forth he was not able to speak unto them, and they perceived that, a vision, he had seen in the Temple, —and, he, continued making signs unto them, and remained dumb.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 And it came to pass, when the days of his public ministration were fulfilled, that he departed unto his house.
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 And, after these days, Elizabeth his wife conceived, and she disguised herself five months, saying—
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 Thus, for me, hath the Lord wrought, —in the days in which he looked upon me, to take away my reproach among men.
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 Now, in the sixth month, was the messenger Gabriel sent forth from God, into a city of Galilee, the name of which was Nazareth, —
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 unto a virgin, betrothed to a man whose name was Joseph, of the house of David; and, the name of the virgin, was, Mary;
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 and entering in unto her, he said—Joy to thee, favoured one! The Lord, be with thee!
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 And, she, at the word, was greatly troubled, and began to deliberate, of what kind, this salutation, might be.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 And the messenger said unto her—Do not fear, Mary, for thou hast found favour with God, —
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 And lo! thou shalt conceive in thy womb, and bring forth a son, and shalt call his name, Jesus:
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 the same, shall be great, and, Son of the Most High, shall be called, and the Lord God, will give unto him, the throne of David his father, —
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 And he shall reign over the house of Jacob, unto the ages, and, of his kingdom, there shall be, no end. (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 But Mary said unto the messenger—How, shall this thing be, seeing that, a man, I know not?
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 And answering, the messenger said unto her—The Holy Spirit, shall come upon thee, and, the power of the Most High, shall overshadow thee; wherefore, even that which is to be born, Holy, shall be called, Son of God.
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 And lo! Elizabeth thy kinswoman, even she, hath conceived a son in, her old-age; —and, this month, is, the sixth, to her, the so-called barren one;
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 Because no declaration from God, shall be void of power.
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 And Mary said—Lo! the handmaid of the Lord! Might it come to pass unto me, according to thy declaration. And the messenger departed from her.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 And Mary, arising, in these days, journeyed into the hill country with haste, into a city of Judah, —
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 and entered into the house of Zachariah, and saluted Elizabeth.
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 And it came to pass that, as Elizabeth heard the salutation of Mary, the babe leapt in her womb, and Elizabeth was filled with Holy Spirit, —
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 and lifted up her voice with loud exclamation, and said—Blessed, art thou among women, and, blessed, is the fruit of thy womb;
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 And, whence, to me is, this, That the mother of my Lord should come, unto me?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 For lo! as the sound of thy salutation came into mine ears, the babe in my womb, leapt in exultation.
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 And, happy, is she who hath believed, that there shall be a perfecting of the things which have been spoken to her from the Lord!
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 And Mary said—My soul doth magnify the Lord,
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 And my spirit hath exulted upon God my saviour;
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 Because he hath looked upon the humbling of his handmaid; for lo! from the present time, all the generations, will pronounce me happy.
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 Because he that is mighty hath done for me great things, and, holy, is his name;
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 And his mercy is unto generations and generations, to them who revere him;
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 He hath wrought strength with his arm, He hath scattered men arrogant in the intention of their heart;
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 He hath deposed potentates from thrones, and uplifted the lowly;
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 The hungry, hath he filled with good things, and, the wealthy, hath he sent empty away;
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 He hath laid hold of Israel his servant, to be mindful of mercies:
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 According as he spake unto our fathers, —To Abraham, and to his seed, —Unto times age-abiding. (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 And Mary abode with her about three months, and returned unto her house.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 And, to Elizabeth, was the time fulfilled, that she should be bringing forth, —and she gave birth to a son.
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 And her neighbours and kinsfolk heard, that the Lord had magnified his mercy with her, and they were rejoicing with her.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 And it came to pass, on the eighth day, that they came to circumcise the child, and were calling it, after the name of its father, Zachariah.
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 And his mother, answering, said—Nay! but he shall be called, John.
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 And they said unto her—There is, no one from among thy kindred, who is called by this name!
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 And they began making signs unto his father, as to what he might be wishing it to be called.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 And, asking for a small tablet, he wrote, saying—John, is his name! and they marvelled all.
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 And his mouth was opened instantly, and his tongue [loosed], and he began to speak, blessing, God.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 And fear came upon all the neighbours themselves; and, throughout all the hill-country of Judaea, were all these matters being much talked of;
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 and all who heard laid [them] up in their hearts, saying—What then shall his child be? for, even the hand of the Lord, was with him.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 And, Zachariah his father, was filled with Holy Spirit, and prophesied, saying: —
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 Blessed, be the Lord, the God of Israel! Because he hath visited and wrought redemption for his people,
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 And hath raised up a horn of salvation for us, In the house of David his servant:
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 According as he hath spoken by mouth of his holy ancient prophets, — (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 Of salvation from among our foes, and out of the hand of all them that hate us:
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 To perform mercy with our fathers, and to be mindful of his holy covenant, —
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 The oath which he sware unto Abraham our father, To grant us,
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 without fear, from the hand of enemies rescued, to be rendering divine service unto him,
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 in lovingkindness and righteousness before him, all our days.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 And, even thou, child, prophet of the Most High, shalt be called, —for thou shall march on before the Lord, to prepare his ways,
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 Giving a knowledge of salvation unto his people, by a remission of their sins.
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 Because of the yearning compassion of the mercy of our God, wherein shall visit us a day-dawn from on high, —
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 To shine on them who, in the darkness and shade of death, are sitting, to guide our feet into a way of peace.
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 And, the child, went on growing, and being strengthened in spirit, and was in the deserts, until the day he was pointed out unto Israel.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< Luke 1 >