< Leviticus 17 >

1 And Yahweh spake unto Moses saying: —
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Speak unto Aaron, and unto his sons and unto all the sons of Israel, and thou shalt say unto them, —This, is the thing which Yahweh hath commanded, saying:
“Yi magana da Haruna da’ya’yansa maza da kuma dukan Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji ya umarta.
3 What man soever, there be of the house of Israel, who slayeth an ox or lamb or goat, in the camp, —or who slayeth it outside the camp;
Duk mutumin Isra’ilan da ya yanka sa, ɗan rago ko akuya a sansani ko waje da shi
4 and, unto the entrance of the tent of meeting, bringeth it not in, to present it as an oblation unto Yahweh, before the habitation of Yahweh, blood, shall be imputed to that man—blood, hath he shed, therefore shall that man be cut off from the midst of his people:
a maimakon kawo shi a matsayin hadaya ga Ubangiji a gaban tabanakul na Ubangiji, za a ɗauki wannan mutum a matsayi mai laifin zub da jini, ya zub da jini, kuma dole a raba shi da mutanensa.
5 to the end that the sons of Israel may bring in their sacrifices which they are offering upon the face of the field, that they may bring them in unto Yahweh—unto the entrance of the tent of meeting, unto the priest, —and that so as peace-offerings unto Yahweh, they may offer them.
Wannan ya zama haka saboda Isra’ilawa su kawo wa Ubangiji hadayun da suke yi a filaye. Dole su kawo su ga firist, wato, ga Ubangiji, a ƙofar Tentin Sujada, su miƙa su a matsayin hadayun salama.
6 Then shall the priest dash the blood against the altar of Yahweh, at the entrance of the tent of meeting, —and shall make a perfume of the fat, as a satisfying odour unto Yahweh;
Firist zai yayyafa jinin a bagaden Ubangiji, a ƙofar Tentin Sujada, yă kuma ƙone kitsen kamar ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji.
7 so shall they no more offer their sacrifices unto demons after whom they are unchastely going away, —a statute age-abiding, shall this be to them unto their generations.
Kada kuma su ƙara yin hadayunsu ga gumaka masu siffar bunsurai waɗanda suka bauta wa. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla a gare su wa tsararraki masu zuwa.’
8 Wherefore, unto them, shalt thou say: What man soever, there may be of the house of Israel, or of the sojourners that sojourn in their midst, —who causeth to go up an ascending-offering, or a sacrifice;
“Faɗa musu, ‘Duk wani mutumin Isra’ila ko wani baƙon da yake zama a cikinsu wanda ya miƙa hadaya ta ƙonawa ko sadaka
9 and unto the entrance of the tent of meeting, doth not bring it in, to offer it unto Yahweh, then shall that man be cut off from among his kinsfolk.
kuma bai kawo shi a ƙofar Tentin Sujada don yă miƙa shi ga Ubangiji ba, dole a raba wannan mutum da mutanensa.
10 And, what man soever, there may be of the house of Israel, or of the sojourners that sojourn in their midst, that partaketh of any manner of blood, then will I set my face against the person that partaketh of the blood, and will cut him off from the midst of his people.
“‘Duk mutumin Isra’ila ko baƙon da yake zama a cikinsu wanda ya ci wani jini, zan yi gāba da wannan mutum wanda ya ci jinin, za a kuma raba shi da mutanensa.
11 For as for the life of the flesh, in the blood, it is, therefore have, I, given it unto you upon the altar, to put a propitiatory-covering over your lives, —for the blood, it is, which, by virtue of the life, maketh propitiation.
Gama ran halitta yana a cikin jinin, kuma na ba da shi gare ku don kafara a kan bagade, jini ne yake kafara saboda ran mutum.
12 For this cause, have I said unto the sons of Israel, Not a person from among you shall partake of blood, —Even the sojourner that sojourneth in your midst, shall not partake of blood.
Saboda haka na ce wa Isra’ilawa, “Babu waninku da zai ci jini, babu wani baƙon da yake zama a cikinku da zai ci jini.”
13 And, what man soever, there may be of the sons of Israel, or of the sojourners that sojourn in their midst, who taketh by hunting any wild-beast or bird that may be eaten, then shall he pour out the blood thereof, and cover it with dust;
“‘Duk wani mutumin Isra’ila ko baƙon da yake zama a cikinku wanda ya ji wa wani dabba ko tsuntsu wanda ake ci ciwo, dole yă tsiyaye jinin yă rufe shi da ƙasa,
14 for, as for the life of all flesh, the blood thereof, for the life thereof, standeth, therefore have I said unto the sons of Israel—Of the blood of no manner of flesh, shall ye partake, For, the life of all flesh is the blood thereof; whoso partaketh thereof, shall be cut off.
domin ran kowace halitta yana cikin jini. Shi ya sa na ce wa Isra’ilawa, “Kada ku ci jinin wani halitta, domin ran kowace halitta yana cikin jinin; duk wanda ya ci shi dole a fid da shi.”
15 And, in the case of any person who eateth that which died of itself or was torn in pieces, whether he be home-born, or a sojourner, then shall he wash his clothes, and bathe in water, and be unclean until the evening, and then be clean.
“‘Kowa, ko haifaffe ɗan ƙasa ko baƙo, da ya ci wani abin da aka sami a mace, ko naman jeji ya yayyage, dole yă wanke rigunansa, yă kuma yi wanka, zai kuma ƙazantu har yamma; sa’an nan zai tsarkake.
16 But, if he wash them not, and his flesh, he do not bathe, then shall he bear his iniquity.
Amma in bai wanke rigunansa ya kuma yi wanka ba, alhaki zai kasance a kansa.’”

< Leviticus 17 >