< Joshua 2 >

1 Then did Joshua son of Nun, send out from The Acacias, two men to spy out silently, saying, Go view the land, and Jericho. So they came, and entered the house of a harlot, whose name was Rahab, and lay there.
Sai Yoshuwa ɗan Nun ya aika’yan leƙen asiri guda biyu a ɓoye daga Shittim ya ce, “Ku je ku duba, ku ga yadda wurin yake, musamman Yeriko.” Sai suka je suka shiga gidan wata karuwa mai suna Rahab, suka sauka a can.
2 And it was told the king of Jericho, saying, —Lo! men, have come in hither to-night of the sons of Israel to search out the land.
Aka gaya wa sarkin Yeriko cewa, “Ji fa, waɗansu Isra’ilawa sun shigo nan da dare don su leƙi asirin ƙasar.”
3 So the king of Jericho sent unto Rahab, saying, —Bring forth the men that are come in unto thee who have entered thy house, for, to search out all the land, have they come.
Saboda haka sai sarki ya aika wannan saƙo zuwa ga Rahab, “Ki fito da mutanen da suka zo suka sauka a gidanki, gama sun zo su leƙi asirin ƙasar ne gaba ɗaya.”
4 And the woman took the two men and hid them, —and said: Even so, the men did come in unto me, but I knew not from whence they were;
Amma matar ta ɓoye mutanen nan biyu. Ta ce, “I, mutanen sun zo wurina, amma ban san daga ina suka zo ba,
5 and it came to pass, as the gate was about to be shut in the darkness, that, the men, went out, I know not whither the men went, —pursue them quickly for ye shall overtake them.
da yamma kuwa, kafin a rufe ƙofar gari sai mutanen suka tafi. Ban san hanyar da suka bi ba, ku yi sauri ku bi su. Mai yiwuwa ku same su.”
6 But, she, had taken them up to the roof, —and concealed them with the stalks of flax which she had laid in order for herself upon the roof.
(Amma ta kai su saman rufin ɗaki ta ɓoye su a ƙarƙashin karan rama da ta baza a rufin ɗaki.)
7 So, the men, pursued them by way of the Jordan unto the fords, —the gate being shut as soon as they who pursued them had gone forth.
Sai mutanen garin suka kama hanyar Urdun don su nemi’yan leƙen asirin, daga fitar su sai aka rufe ƙofar garin.
8 And, ere yet they slept, she, went up unto them, upon the roof;
Kafin’yan leƙen asirin su kwanta, sai ta tafi wurinsu a bisa rufin ɗakin
9 and said unto the men, I know that Yahweh hath given unto you the land, —and that the terror of you hath fallen upon us, and that all the inhabitants of the land, have melted away, from before you.
ta ce musu, “Na sani Ubangiji ya riga ya ba ku ƙasan nan, tsoronku kuma ya kama mu har zukatan mazaunan ƙasar duka sun narke saboda ku.
10 For we have heard how Yahweh, dried up, the waters of the Red Sea from before you, when ye came forth out of Egypt, —and what ye did unto the two kings of the Amorites who were over the Jordan unto Sihon and unto Og, whom ye devoted to destruction;
Mun ji yadda Ubangiji ya busar da ruwan Jan Teku domin ku lokacin da kuka fito daga ƙasar Masar, da kuma abin da kuka yi wa Sihon da Og, sarakunan nan biyu na Amoriyawa gabas da Urdun, waɗanda kuka hallaka su sarai.
11 and, when we heard, then did our heart melt, and there rose up no longer any spirit in any man because of you, —for, as for Yahweh your God, he, is God—in the heavens above, and upon the earth beneath.
Da muka ji labarin, duk sai zuciyar kowa ta narke, kowa ya karaya saboda ku, gama Ubangiji Allahnku shi ne Allah na sama da ƙasa.
12 Now, therefore I pray you, swear unto me by Yahweh, since I have dealt with you in lovingkindness, that, ye also, will deal with the house of my father in lovingkindness, and will give me a token of faithfulness,
Yanzu ina roƙonku ku rantse mini da Ubangiji cewa za ku yi wa iyalina alheri kamar yadda na yi muku alheri. Ku ba ni ƙwaƙƙwarar shaida cewa
13 and will save alive my father and my mother, and my brethren and my sisters, and all that they have, —and will deliver our souls from death.
za ku ceci rayukan mahaifina da mahaifiyata, da’yan’uwana maza da mata, da duk waɗanda suke nasu, za ku cece mu daga mutuwa.”
14 And the men said unto her, Our souls in your stead unto death, if ye utter not this our business, —so shall it be, when Yahweh shall give us the land, that we will deal with thee in lovingkindness and in faithfulness.
Mutanen suka tabbatar mata suka ce, “Ranmu a bakin ranki! In ba ki faɗa wa kowa abin da ya kawo mu ba, za mu yi miki alheri da aminci lokacin da Ubangiji ya ba mu ƙasar.”
15 And she let them down with a cord through the window, —for, her house, was within the wall of the rampart, and, within the rampart, she was dwelling.
Sai ta zura igiya ta taga suka bi, domin gidan da take yana haɗe da katangar birnin.
16 And she said unto them—To the mountain, get you, lest the pursuers, fall in, with you, —and hide yourselves there, three days until the pursuers return, and, afterwards, shall ye go your way.
Ta ce musu, “Ku tafi cikin tuddan ƙasar don kada mutanen sarki su same ku. Ku ɓuya a can na kwana uku, har sai masu nemanku su komo, sa’an nan ku kama hanyarku.”
17 And the men said unto her, —Free, will we be from this thine oath which thou hast made us swear:
Mutanen suka ce mata, “Rantsuwar da kika sa muka yi, ba za tă yi amfani ba
18 Lo! when we are coming into the land, this cord of crimson thread, must thou bind in the window by which thou didst let us down, and, thy father and thy mother and thy brethren and all the household of thy father, must thou gather together unto thee unto the house.
sai in kin ɗaura jan ƙyalle a tagar da kika zura mu, kuma sai in kin kawo mahaifinki da mahaifiyarki, da’yan’uwanki, da dukan iyalinki cikin gidanki.
19 And it shall be, whosoever shall go forth out of the doors of thy house into the street, his blood, shall be on his own head and, we, shall be free, —but, whosoever shall be with thee in the house, his blood, shall be on our heads, if a, hand, be upon him.
In wani ya fita kan hanya, alhakin jininsa yă kasance a kansa; ba ruwanmu. Amma in aka taɓa wani da yake cikin gidanki tare da ke, alhakin jininsa yana kanmu.
20 Or, if thou utter this our business, then shall we be free from this thine oath which thou hast made us swear.
In kika tone mana asiri, za mu karya alkawarin da kika sa muka yi.”
21 And she said—According to your words, so, shall it be. Thus sent she them away and they departed, —and she bound the crimson cord in the window.
Ta ce, “Na yarda! Bari yă zama yadda kuka ce.” Sai ta sallame su suka tafi. Ta kuwa ɗaura jan ƙyalle a tagar.
22 And they went and came into the mountain, and abode there three days, until the pursuers had returned, —so the pursuers, made search, throughout all the way, but found them not.
Sai suka tafi, suka shiga cikin tuddai, suka yi zamansu a can kwana uku har masu nemansu suka koma, gama masu nemansu suka yi ta nema ko’ina a hanyar, amma ba su sami kowa ba.
23 And the two men returned and came down out of the mountain, and crossed over and came unto Joshua, son of Nun, —and recounted to him all that had befallen them;
Sa’an nan mutanen nan biyu,’yan leƙen asiri suka sauka daga tuddai suka haye kogi zuwa wurin Yoshuwa ɗan Nun, suka gaya masa duk abin da ya faru da su.
24 and they said unto Joshua, Yahweh, hath delivered, into our hand all the land, —moreover also all the inhabitants of the land, have melted away, from before us.
Suka ce wa Yoshuwa, “Ba shakka Ubangiji ya ba mu ƙasan nan duka, tana hannunmu, mutane can duk sun narke da tsoro saboda mu.”

< Joshua 2 >