< John 16 >

1 These things, have I spoken unto you, that ye may not be caused to stumble:
“Na faɗa muku wannan duka, domin kada ku bauɗe.
2 Excommunicants from the synagogue, will they make you; Nay! there cometh an hour, that, every one who killeth you, shall think to be rendering, divine service, unto God!
Za su kore ku daga majami’a; lalle, lokaci yana zuwa da duk wanda ya kashe ku, zai ɗauka yana yin wa Allah hidima ne.
3 And, these things, will they do, because they got to know, neither the Father nor me.
Za su yi waɗannan abubuwa ne domin ba su san Uba ko ni ba.
4 But, these things, have I told you, —That, whensoever their hour shall come, ye may remember, that, thereof, I told you. These things, however, I told you not, from the beginning, because I was, with you;
Na faɗa muku wannan, domin in lokacin ya yi, ku tuna na gargaɗe ku. Ban faɗa muku wannan tun da fari ba domin ina tare da ku.
5 But, now, I go my way unto him that sent me, and, not one from among you, questioneth me—Whither goest thou?
“Yanzu zan tafi wurin wanda ya aiko ni, duk da haka ba waninku da ya tambaye ni, ‘Ina za ka?’
6 But, because, these things, I have told you, sorrow, hath filled your heart.
Saboda na faɗa waɗannan abubuwa ga shi kun cika da baƙin ciki.
7 But, I, the truth, am telling you—It is profitable for you, that, I, depart; for, if I should not depart, The Advocate, would in nowise come unto you, but, if I go, I will send him unto you.
Amma gaskiya nake gaya muku. Don amfaninku ne zan tafi. Sai ko na tafi, in ba haka ba Mai Taimakon nan ba zai zo muku ba. Amma in na tafi, zan aiko shi gare ku.
8 And, having come, He, will reprove the world—Concerning sin, and concerning righteousness, and concerning judgment:
Sa’ad da ya zo kuwa, zai kā da duniya a kan zunubi da adalci da kuma hukunci,
9 Concerning sin, indeed, because they are not believing on me;
a kan zunubi, domin mutane ba su gaskata da ni ba;
10 But, concerning righteousness, because, unto the Father, I go my way, and, no longer, do ye behold me;
a kan adalci, domin zan tafi wurin Uba, inda ba za ku ƙara ganina ba;
11 And, concerning judgment, because, the ruler of this world, hath been judged.
a kan hukunci kuma, domin an yanke hukunci a kan mai mulkin duniyan nan.
12 Yet many things, have I, unto you, to be saying, —but ye cannot bear them, just now;
“Ina da sauran abubuwa da yawa da zan faɗa muku, amma ba za ku iya ɗauka a yanzu ba.
13 Howbeit, as soon as, he, hath come—The Spirit of truth, he will guide you into all truth; for he will not speak from himself, but, whatsoever he heareth, he will speak, and, the coming things, will he announce unto you.
Amma sa’ad da shi, Ruhun gaskiya ya zo, zai bi da ku zuwa ga dukan gaskiya. Ba zai yi magana don kansa ba; zai faɗi abin da ya ji ne kaɗai, zai kuma faɗa muku abin da bai faru ba tukuna.
14 He, shall glorify me; for, of mine, shall he receive, and announce unto you.
Zai kawo ɗaukaka gare ni ta wurin ɗaukan abin da yake nawa, ya bayyana muku.
15 All things, whatsoever the Father hath, are, my own; therefore, said I—Of mine, shall he receive, and announce unto you.
Duk abin da yake na Uba nawa ne. Shi ya sa na ce, ‘Ruhun zai ɗauko daga abin da yake nawa, yă bayyana muku.’”
16 A little while, and, no longer, ye behold me; and, again a little while, and ye shall see me.
Yesu ya ci gaba da cewa, “Jim kaɗan, ba za ku ƙara ganina ba, sa’an nan bayan an jima kaɗan kuma, za ku gan ni.”
17 Some of his disciples, therefore, said one to another—What is this which he is saying to us: —A little while, and ye behold me not, and, again a little while, and ye shall see me; and—Because I go my way unto the Father?
A nan fa sai waɗansu almajiransa suka ce wa juna, “Me yake nufi da cewa, ‘Jim kaɗan ba za ku ƙara ganina ba, kuma bayan an jima kaɗan, za ku gan ni,’ da kuma, ‘Domin zan tafi wurin Uba’?”
18 They were saying, therefore—What is this which he saith: —A little while? We know not [what he is saying].
Suka yi ta tambaya, “Me yake nufi da ‘jim kaɗan’? Ba mu fahimci abin da yake faɗi ba.”
19 Jesus took note, that they were wishing to question him, and said unto them—Concerning this, are ye enquiring one with another, —because I said: —A little while, and ye behold me not, and, again, a little while, and ye shall see me?
Yesu ya gane suna so su tambaye shi game da wannan, sai ya ce musu, “Kuna tambayar juna game da abin da nake nufi da na ce, ‘Jim kaɗan ba za ku ƙara ganina ba, da kuma bayan an jima kaɗan, za ku gan ni’?
20 Verily, verily, I say unto you—Ye, shall weep and lament, but, the world, shall rejoice: Ye, shall be grieved, but, your grief, into joy, shall be turned.
Gaskiya nake gaya muku, za ku yi kuka da kuma gunji, yayinda duniya take murna. Za ku yi baƙin ciki, amma baƙin cikinku zai koma farin ciki.
21 A woman, as soon as she is about to bring forth, hath, grief, because her hour hath come; but, as soon as she hath given birth to the child, no longer, remembereth she the anguish, by reason of the joy, that a human being into the world hath been born.
Macen da za tă haihu takan yi naƙuda domin lokacinta ya yi; amma sa’ad da ta haihu, sai ta manta da wahalar domin farin ciki an haifi jariri a duniya.
22 And, ye, therefore, now, indeed have grief; but, again, will I see you, and your heart shall rejoice, —and, your joy, no one, shall force from you.
Haka ku ma, yanzu ne lokacin baƙin cikinku, amma zan sāke ganinku za ku kuma yi farin ciki, ba kuwa wanda zai ɗauke muku farin cikinku.
23 And, in that day, shall ye request me, nothing: —Verily, verily, I say unto you—Whatsoever ye shall ask the Father, He will give you, in my name.
A ranan nan, ba za ku sāke tambaya ta kome ba. Gaskiya nake gaya muku, Ubana zai ba ku kome da kuka roƙa cikin sunana.
24 Until even now, ye have asked nothing in my name: Be asking, and ye shall receive, —that, your joy, may be made full.
Har yanzu dai ba ku roƙi kome cikin sunana ba. Ku roƙa za ku kuwa samu, farin cikinku kuwa zai zama cikakke.
25 These things, in similitudes, have I spoken unto you: There cometh an hour, when, no longer in similitudes, will I speak unto you, but, openly, concerning the Father, will I tell you.
“Ko da yake ina magana da misalai, lokaci yana zuwa da ba zan ƙara yin magana da misalai ba, sai dai in faɗa muku a fili game da Ubana.
26 In that day, In my name, shall ye ask: —and I say not that, I, will request the Father for you;
A ranan nan, za ku roƙa a cikin sunana. Ban ce zan roƙi Uba a madadinku ba.
27 For, the Father himself, dearly loveth you, because, ye, have dearly loved me, and believed that, I, from the Father, came forth: —
Ai, shi Uban kansa yana ƙaunarku domin kun ƙaunace ni kun kuma gaskata cewa daga Allah na fito.
28 I came forth out of the Father, and have come into the world, —Again, I leave the world, and go, unto the Father.
Na fito daga wurin Uba, na kuma shigo duniya, yanzu kuwa zan bar duniya in koma wurin Uba.”
29 His disciples say—See! now, openly, art thou speaking, and, not a single similitude, art thou using:
Sai almajiran Yesu suka ce, “Haba, yanzu ne fa kake magana a sarari ba tare da misalai ba.
30 Now, we know, that thou knowest all things, and hast, no need, that one be questioning thee. Hereby, do we believe, that, from God, thou camest forth.
Yanzu mun gane cewa ka san kome ba sai wani ya tambaye ka ba. Wannan ya sa muka gaskata ka fito daga Allah.”
31 Jesus answered them—As yet, ye believe:
Yesu ya amsa ya ce, “A ƙarshe kun gaskata!
32 Lo! there cometh an hour, and hath come, that ye should be scattered, each, unto his own home; and, me, alone, should leave; —And yet I am not, alone, but, the Father, is, with me!
Amma lokaci na zuwa, har ma ya yi, da za a warwatsa ku, kowa yă koma gidansa. Za ku bar ni ni kaɗai. Duk da haka ba ni kaɗai ba ne, gama Ubana yana tare da ni.
33 These things, have I spoken unto you, that, in me, ye may have, peace: In the world, ye have, tribulation; but be taking courage, —I, have overcome the world.
“Na faɗa muku waɗannan abubuwa ne, domin a cikina ku sami salama. A duniyan nan za ku sha wahala. Amma ku yi ƙarfin hali! Na yi nasara a kan duniya.”

< John 16 >