< Joel 2 >

1 Blow ye a horn in Zion, sound an alarm in my holy mountain, let all the inhabitants of the land, tremble, —for coming is the day of Yahweh, for it is near!—
Ku busa ƙaho a cikin Sihiyona; ku yi karar amo a tsaunina mai tsarki. Bari dukan mazaunan ƙasar su yi rawan jiki, gama ranar Ubangiji tana zuwa. Tana gab da faruwa
2 A day of obscurity and deep gloom, a day of cloud, and thick darkness, as dusk, spread over the mountains, —a people, many and bold, like whom, hath not been from age-past times, and, after whom, shall not be again unto the years of generation after generation.
rana ce ta baƙin duhu ƙirin, ranar gizagizai ce baƙi ƙirin. Babbar rundunar mayaƙa mai ƙarfi tana zuwa kamar ketowar alfijir a kan duwatsu yadda ba a taɓa ganin irinta ba, ba kuwa za a ƙara ganin irinta ba har tsararraki masu zuwa.
3 Before him, hath a fire, devoured, and, after him, shall a flame, consume, —As the garden of Eden, is the land before him, but, after him, a desert most desolate, Moreover also, escape, giveth he none.
A gabansu wuta tana ci, a bayansu ga harshen wuta yana ci, A gabansu ƙasa ta yi kamar gonar Eden, a bayansu kuma jeji ne wofi, babu abin da ya kuɓuce musu.
4 As the appearance of horses, is his appearance, and, as war-horses, so, shall they run:
Suna da kamannin dawakai; suna gudu kamar dokin yaƙi.
5 Like the noise of chariots on the tops of the mountains, shall they rattle along, like the noise of a flame of fire, devouring dry straw, —like a people bold, arrayed for battle.
Da motsi kamar na kekunan yaƙi sun tsallake ƙwanƙolin duwatsu, kamar ƙarar harshen wuta mai cin tattaka, kamar runduna mai ƙarfi wadda ta ja dāgār yaƙi.
6 Because of him, shall peoples’, be in anguish, —all faces, have withdrawn their colour.
Da ganinsu, al’ummai sun kamu da azaba; kowace fuska ta yanƙwane.
7 Like heroes, shall they run, like men of war, shall they mount a wall, —and, every one—along his own road, shall they march along, and shall not change their paths;
Sukan auka kamar jarumawa; sukan hau katanga kamar sojoji. Kowa yana takawa bisa ga tsari, ba mai kaucewa.
8 Nor, against each other, shall they strike, Each—on his own highway, shall they march, —though, in among the weapons, they fall, they shall not stop.
Ba sa turin juna, kowane yakan miƙe gaba. Sukan kutsa cikin abokan gāba ba mai tsai da su.
9 Upon the city, shall they leap, on the wall, shall they run, up the houses, shall they climb, —through the windows, shall they enter, like a thief,
Sukan ruga cikin birni, suna gudu a kan katanga. Sukan hau gidaje, sukan shiga ta tagogi kamar ɓarayi.
10 Before him, hath quaked the earth, have trembled the heavens, —the sun and the moon, have become dark, and, the stars, have withdrawn their shining;
A gabansu duniya takan girgiza, sararin sama kuma yakan jijjigu, rana da wata su yi duhu, taurari kuma ba sa ba da haske.
11 And, Yahweh, hath uttered his voice, before his host, for great indeed is his camp, for bold is he who executeth his word, —for great is the day of Yahweh, and awful exceedingly, Who then shall endure it?
Ubangiji ya yi tsawa wa shugaban mayaƙansa; sojojinsa sun fi a ƙirge masu ƙarfi ne kuma su waɗanda suke biyayya da umarninsa. Ranar Ubangiji da girma take; mai banrazana. Wa zai iya jure mata?
12 Even now, therefore, urgeth Yahweh, Turn ye unto me, with all your heart, —and with fasting and with weeping, and with lamentation;
“Ko yanzu”, in ji Ubangiji, “Ku juyo gare ni da dukan zuciyarku, da azumi da kuka da makoki.”
13 And rend your heart, and not your garments, turn therefore, unto Yahweh your God, —for, gracious and full of compassion, is he, slow to anger, and abundant in loving- kindness, and will grieve over calamity.
Ku kyakkece zuciyarku ba rigunanku ba. Ku juyo ga Ubangiji Allahnku, gama shi mai alheri ne mai tausayi kuma mai jinkirin fushi da yawan ƙauna, yakan kuma janye daga aika da bala’i.
14 Who knoweth, he may turn and grieve, —and leave behind him, a blessing, a meal-offering and a drink-offering, to Yahweh your God?
Wa ya sani? Ko zai juya yă kuma ji tausayi yă sa mana albarka ta wurin hadaya ta gari da hadaya ta sha wa Ubangiji Allahnku.
15 Blow ye a horn, in Zion, —hallow a fast, call a solemn assembly:
A busa ƙaho a Sihiyona, a yi shelar azumi mai tsarki, a kira tsarkakan taro.
16 Gather the people, hallow a convocation, collect the elders, gather the children, and the sucklings of the breasts, —let the bridegroom, come forth, from his chamber, and the bride from her bower:
A tattara mutane; ku tsarkake taron; ku kawo dattawa wuri ɗaya; ku kuma tara yara, da waɗanda suke shan mama. Bari ango yă bar ɗakinsa amarya kuma lolokinta.
17 Between the porch and the altar, let the priests, weep, the attendants of Yahweh, —and let them say—Look with pity, O Yahweh, upon thy people, and do not deliver thine inheritance to reproach, that the nations, should mock them, Why should they say among the peoples, Where is their God?
Bari firistocin da suke yin hidima a gaban Ubangiji, su yi kuka tsakanin filin haikali da bagade. Bari su ce, “Ka cece mutanenka, ya Ubangiji. Kada ka bar gādonka yă zama abin dariya, da abin ba’a a cikin al’ummai. Me zai sa a ce a cikin mutane, ‘Ina Allahnsu yake?’”
18 And Yahweh became jealous for his land, —and took pity on his people;
Ta haka Ubangiji zai yi kishin ƙasarsa yă kuma ji tausayin mutanensa.
19 Then answered Yahweh, and said to his people: —Behold me! sending you the corn, and the new wine and the oil, so shall ye be satisfied therewith; and I will not make you, any more, a reproach among the nations.
Ubangiji zai amsa musu ya ce, “Ina aika da hatsi, sabon ruwan inabi, da mai, isashe da zai ƙosar da ku sosai; ba kuma zan ƙara maishe ku abin dariya ga al’ummai ba.
20 And, the Northerner, will I remove far from you, and drive him into a land parched and desolate, with, his face, toward the eastern sea, and, his rear, toward the hinder sea, —then shall come up his ill odour, yea his stench, shall ascend, because he hath shown himself great in doing.
“Zan kori sojojin arewa nesa da ku, in tura su cikin busasshiyar ƙasa marar amfani kuma, kuma da sawunsu na gaba zan tura su zuwa gabashin teku da kuma sawunsu na baya tura su zuwa yammanci a Bahar Rum. Warinsu kuma zai bazu; ɗoyinsu zai tashi.” Tabbatacce ya yi al’amura masu girma.
21 Be not thou afraid, O soil, —exult and rejoice, because Yahweh, hath shown himself great, in doing.
Kada ki ji tsoro, ya ƙasa; ki yi murna ki kuma yi farin ciki. Tabbatacce Ubangiji ya yi abubuwa masu girma.
22 Be not afraid, ye beasts of the field, for sprouted have the pastures of the wilderness, —for, the tree, hath borne its fruit, the fig-tree and the vine, have yielded their wealth.
Kada ku ji tsoro, ya ku namun jeji, gama wuraren kiwo sun yi kore shar. Itatuwa suna ba da’ya’yansu; itacen ɓaure da na inabi suna ba da amfaninsu.
23 Ye sons of Zion, then, exult and be glad in Yahweh your God, for he hath given you the seed-rain, in right manner, —Yea he hath caused to descend for you a down-pour, of seed-rain and of the harvest-rain in the first month;
Ku yi murna, ya ku mutanen Sihiyona, ku yi farin ciki cikin Ubangiji Allahnku, gama ya ba ku ruwan bazara cikin adalci. Yakan aika muku yayyafi a yalwace, na bazara da na kaka, kamar dā.
24 So shall the threshing-floors, be filled, with corn, —and the vats, overflow, with new wine and oil.
Masussukai za su cika da hatsi; randuna za su cika da sabon ruwan inabi da mai suna zuba.
25 Then will I make good to you the years which were eaten by the swarming locust, the grass locust, and the corn locust and the creeping locust, —even my great army, which I sent among you.
“Zan mayar muku da abin da fāra suka ci a waɗannan shekaru waɗanda ɗango da fāra masu gaigayewa, da kuma sauran fāra da tarin fāra babban mayaƙan da na aika don su fāɗa muku.
26 And ye shall eat and eat, and be satisfied, and shall praise the name of Yahweh your God, who hath dealt with you wondrously, —so shall my people, not be abashed, unto times age-abiding.
Za ku sami a wadace ku ci, har sai kun ƙoshi, za ku kuma yabi sunan Ubangiji Allahnku, wanda ya yi muku ayyukan banmamaki; mutanena ba za su ƙara shan kunya ba.
27 So shall ye know that, in the midst of Israel, I am, and that, I, Yahweh, am your God, and none else, —and my people, shall not be abashed, unto times age-abiding.
Sa’an nan za ku sani ina cikin Isra’ila, cewa ni ne Ubangiji Allahnku, babu wani kuma; mutanena ba za su ƙara shan kunya ba.
28 And it shall come to pass, afterwards, I will pour out my spirit upon all flesh, and your sons and your daughters, shall prophesy, —your old men, shall dream, dreams, your young men, shall see, visions;
“Daga baya kuma, zan zuba Ruhuna a bisan dukan mutane.’Ya’yanku maza da mata za su yi annabci, tsofaffinku za su yi mafarkai, matasanku za su ga wahayoyi.
29 Moreover also, upon the servants and upon the handmaids—in those days, will I pour out my spirit;
Har ma a bisan bayina, maza da mata, zan zuba Ruhuna a kwanakin nan.
30 And I will set forth wonders in the heavens, and in the earth, —blood, and fire, and columns of smoke:
Zan nuna abubuwan banmamaki a cikin sammai da kuma a kan duniya, za a ga jini da wuta da murtukewar hayaƙi.
31 The sun, shall be turned into darkness, and the moon into blood, —before the coming of the great and awful day of Yahweh.
Rana za tă duhunta wata kuma yă zama jini kafin isowar babbar ranan nan mai banrazana ta Ubangiji.
32 And it shall come to pass, whosoever, shall call on the name of Yahweh, shall be delivered, —For in Mount Zion, and in Jerusalem, shall be a delivered remnant, just as Yahweh hath said, and among the survivors, whom Yahweh doth call.
Amma dukan waɗanda suka nemi Ubangiji za su tsira. Kamar yadda Ubangiji ya ce, gama a Dutsen Sihiyona da Urushalima akwai ceto, a cikin waɗannan da Ubangiji ya kira.

< Joel 2 >