< Job 33 >

1 But, in very deed, hear, I pray thee, Job, my discourse, and, to all my words, give thou ear.
“Amma yanzu, Ayuba, ka saurari abin da zan ce; ka sa hankali ga kowane abin da zan faɗa.
2 Lo! I pray thee, I have opened my mouth, My tongue, with my palate, hath spoken,
Zan yi magana; kalmomina suna dab da fitowa daga bakina.
3 Mine utterances come straight from mine own heart, and, what I know, my lips have truly spoken;
Abin da zan faɗa gaskiya ne daga cikin zuciyata; bakina zai faɗi gaskiyar abin da na sani.
4 The spirit of GOD, hath made me, and, the inspiration of the Almighty, giveth me life.
Ruhun Allah ne ya yi ni; numfashin Maɗaukaki ya ba ni rai.
5 If thou art able to answer me, Set in order before me—take thy stand!
Ka amsa mini in za ka iya; ka yi shirin fuskanta ta.
6 Lo! I am like thyself toward GOD, From clay, have I been nipped off, even I!
Ni kamar ka nake a gaban Allah; ni ma daga ƙasa aka yi ni.
7 Lo! my terror, will not startle thee, nor, my hand, upon thee, be heavy.
Kada ka ji tsorona, ba abin da zai fi ƙarfinka.
8 But thou hast spoken in mine ears, and, the sound of words, I heard: —
“Amma ka faɗa na ji, na ji daidai abin da ka faɗa,
9 Pure am, I, without transgression, —Clean am, I, and have no iniquity;
‘ni mai tsarki ne marar zunubi; ina da tsabta kuma ba ni da laifi.
10 Lo! occasions of hostility, would he find against me, He counteth me an enemy to him;
Duk da haka Allah ya same ni da laifi; ya ɗauke ni maƙiyinsa,
11 He putteth—in the stocks—my feet, He watcheth all my paths.
ya daure ƙafafuna da sarƙa; yana tsaron duk inda na bi.’
12 Lo! in this, thou hast not been right—let me answer thee, For, GOD, is greater than, man.
“Amma na gaya maka, a nan ba ka yi daidai ba, gama Allah ya fi mutum girma.
13 Wherefore, against him, hast thou contended? For, with none of his reasons, will he respond.
Don me ka yi masa gunaguni cewa ba ya amsa tambayoyin mutum?
14 For, in one way, GOD may speak, —and, in a second way, one may not heed it: —
Gama Allah yana magana, yanzu ga wannan hanya, yanzu kuma ga wata hanya ko da yake ba lalle mutum yă lura ba.
15 In a dream, a vision of the night, when a deep sleep falleth upon men, in slumberings upon the bed,
A cikin mafarki, cikin wahayi da dare, sa’ad da barci mai zurfi ya fāɗo a kan mutane lokacin da suke cikin barci kan gadajensu,
16 Then, uncovereth he the ear of men, and, on their correction, affixeth a seal;
mai yiwuwa yă yi musu magana a cikin kunnuwansu yă razana su da gargaɗinsa,
17 To turn a son of earth from his deed, while yet, pride, from man he concealeth:
don a juyar da su daga abin da yake yi da ba daidai ba a kuma hana su daga girman kai,
18 He keepeth back his said from the pit, and his life from passing away by a weapon.
don a kāre su daga fāɗuwa cikin rami, a kāre su daga hallaka ta wurin takobi.
19 Or he is chastised with pain, upon his bed, and, the strife of his bones, is unceasing!
“Ko kuma mutum yă sha horo ta wurin kwanciya da ciwo da rashin jin daɗi cikin ƙasusuwansa,
20 So that his life maketh loathsome [his] food, and his soul, dainty meat;
yadda zai ji ƙyamar abinci, har yă ƙi son abinci mafi daɗi.
21 His flesh wasteth away out of sight, and bared are the bones once unseen;
Naman jikinsa ya lalace ba wani abu mai kyau a ciki kuma ƙasusuwansa da suke a rufe da tsoka yanzu duk sun fito.
22 So doth his soul draw near to the pit, and his life to the inflicters of death:
Ransa yana matsawa kusa da rami, ransa kuma kusa da’yan aikan mutuwa.
23 If there hath been near him a messenger who could interpret—one of a thousand, to declare to the son of earth His uprightness,
Duk da haka, in akwai mala’ika a gefensa kamar matsakanci, ɗaya daga cikin dubu, da zai gaya wa mutum abin da yake daidai gare shi,
24 Then hath he shewed him favour, and said, Set him free from going down to the pit, I have found a price of redemption!
yă yi masa alheri yă ce, ‘Kada ka bari yă fāɗa cikin rami, na samu fansa dominsa.’
25 His flesh hath been made fresher than a child’s, he hath returned to the days of his youth;
Sa’an nan fatar jikinsa za tă zama sabuwa kamar ta jariri; za tă zama kamar lokacin da yake matashi.
26 He made supplication unto GOD, who hath accepted him, and he hath beheld his face with a shout of triumph, Thus hath he given back to man his righteousness.
Ya yi addu’a ga Allah ya kuwa samu alheri a wurinsa, yana ganin fuskar Allah yana kuma yin sowa don murna; Allah ya mayar da shi ya zama mai adalci.
27 He sang before men, and said, I sinned, and, uprightness, I perverted, yet he requited me not;
Sa’an nan sai ya zo wurin, wurin mutane ya ce, ‘Na yi zunubi, na kauce wa abin da yake daidai, amma ban samu abin da ya kamata in samu ba.
28 He hath ransomed my soul from passing away into the pit, —and, my life, in the light, shall have vision.
Ya fanshi raina daga fāɗawa cikin rami, kuma zan rayu in ji daɗin hasken.’
29 Lo! a these things, doth GOD work, two ways, three, with a man;
“Allah ya yi wa mutum duk waɗannan, sau biyu, har ma sau uku.
30 To bring back his soul from the pit, to enlighten with the light of the living.
Ya juyo da ransa daga fāɗawa cikin rami, don hasken rai ya haskaka a kansa.
31 Mark well, O Job, and hearken to me, Be silent, and, I, will speak:
“Ka sa hankali da kyau, Ayuba, ka saurare ni; ka yi shiru zan yi magana.
32 If there is anything to say, reply to me, Speak, for I desire to justify thee;
In kana da abin da za ka ce, ka amsa mini; yi magana, domin ina so in’yantar da kai.
33 If not, do, thou, hearken unto me, Be silent, that I may teach thee wisdom.
Amma in ba haka ba, sai ka saurare ni; yi shiru, zan kuma koya maka hikima.”

< Job 33 >