< Job 17 >

1 My spirit, is broken, My days, are extinguished, Graves, are left me.
Na karaya, kwanakina sun kusa ƙarewa, kabari yana jirana.
2 Verily there are mockers, with me! And, on their insults, mine eye doth rest.
Ba shakka masu yi mini ba’a suna kewaye da ni; idanuna suna ganin tsokanar da suke yi mini.
3 Appoint it, I pray thee—be thou surety for me with thyself, Who is there that, on my side, can pledge himself?
“Ya Allah, ka ba ni abin da ka yi mini alkawari. Wane ne zai kāre ni?
4 For, their heart, hast thou kept back from understanding, On this account, thou wilt not exalt them.
Ka rufe zuciyarsu yadda ba za su iya ganewa ba, saboda haka ba za ka bari su yi nasara ba.
5 He that, for a share, denounceth friends, even, the eyes of his children, shall be dim.
In mutum ya juya wa abokansa baya don a ba shi wata lada’ya’yansa za su makance.
6 But he hath set me, as the byword of peoples, And, one to be spit on in the face, do I become.
“Allah ya sa na zama abin da kowa yake magana a kai wanda kowa yake tofa wa miyau a fuska.
7 Therefore hath mine eye become dim from vexation, and, my members, are like a shadow, all of them.
Idanuna ba sa gani sosai don baƙin ciki; jikina ya zama kamar inuwa kawai
8 Upright men shall be astounded over this, and, the innocent, against the impious, shall rouse themselves.
Mutanen da suke masu adalci wannan abu ya ba su tsoro; marasa laifi sun tayar wa marasa tsoron Allah.
9 That the righteous may hold on his way, and, the clean of hands, increase in strength.
Duk da haka, masu adalci za su ci gaba da tafiya a kan hanyarsu, waɗanda hannuwansu suke da tsabta kuma za su ƙara ƙarfi.
10 But indeed, as for them all, will ye bethink yourselves and enter into it, I pray you? Or shall I not find, among you, one who is wise?
“Amma ku zo dukanku, ku sāke gwadawa! Ba zan sami mutum ɗaya mai hikima ba a cikinku.
11 My days, are past, my purposes, are broken off, the possessions of my heart!
Kwanakina sun wuce, shirye-shiryena sun ɓaci haka kuma abubuwan da zuciyata take so.
12 Night for day, they appoint, Light, is near, by reason of darkness!
Mutanen nan sun juya rana ta zama dare. A tsakiyar duhu suka ce, ‘Haske yana kusa.’
13 If I wait for hades as my house, in darkness, have spread out my couch; (Sheol h7585)
In kabari ne begen da nake da shi kaɗai, in na shimfiɗa gadona a cikin duhu, (Sheol h7585)
14 To corruption, have exclaimed, My father, thou! My mother! and My sister! to the worm.
In na ce wa kabari, ‘Kai ne mahaifina,’ tsutsa kuma ke ce, ‘Mahaifiyata’ ko ‘’yar’uwata,’
15 Where then would be my hope? And, as for my blessedness, who should see it!
To, ina begena yake? Wane ne zai iya ganin wani bege domina?
16 With me to hades, would they go down, If, wholly—into the dust, is the descent! (Sheol h7585)
Ko begena zai tafi tare da ni zuwa kabari ne? Ko tare za a bizne mu cikin ƙura?” (Sheol h7585)

< Job 17 >