< Jeremiah 8 >

1 At that time, Declareth Yahweh, Shall they bring forth, The bones of the kings of Judah, and The bones of his princes, and The bones of the priests, and The bones of the prophets, and The bones of the inhabitants of Jerusalem, Out of their graves,
“‘A wancan lokaci, in ji Ubangiji, za a fitar da ƙasusuwan sarakuna da na shugabannin Yahuda, ƙasusuwan firistoci da na annabawa, da kuma ƙasusuwan mutanen Urushalima daga kaburbura.
2 And shall spread them out—To the sun, and To the moon, and To all the host of the heavens, Whom they have loved, And whom they have served, And after whom they have walked, And whom they have sought, And to whom they have bowed themselves down, —They shall not be gathered, Neither shall they be buried, As heaps of dung on the face of the ground, shall they be.
Za a shimfiɗa su a rana da wata da kuma dukan taurarin sammai, waɗanda suka ƙaunata suka kuma bauta wa, waɗanda suka bi suka nemi shawarar suka kuma yi wa sujada. Ba za a tattara su ko a binne su ba, amma za su zama kamar juji a jibge a ƙasa.
3 Then shall, death, be chosen rather than life, by all the remnant of them that remain, of this wicked family, —in all the places, whither I have driven them, Declareth Yahweh of hosts.
Duk inda na kore su zuwa, dukan waɗanda suka ragu na wannan muguwar al’umma za su gwammaci mutuwa da rai, in ji Ubangiji Maɗaukaki.’
4 Therefore shalt thou say unto them—Thus, saith Yahweh, Will men fall and not arise? Will one turn away, and not come back?
“Fada musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Sa’ad da mutane suka fāɗi, ba sa tashi ne? Sa’ad da mutum ya kauce, ba ya dawowa?
5 Wherefore hath this people of Jerusalem apostatized with an enduring apostacy, —Taken fast hold of deceit, Refused to come back?
To, me ya sa waɗannan mutane suka kauce? Me ya sa Urushalima kullum take kaucewa? Sun manne wa ƙarya; suka ƙi su dawo.
6 I hearkened and heard—Not aright, did they speak, —Not a man, repented him of his wickedness, saying, What have I done! They have every one, turned to their course again, Like a horse sweeping on through the battle.
Na saurara sosai, amma ba su faɗi wata maganar kirki ba. Ba wanda ya tuba daga muguntarsa, sai ma cewa yake, “Me na yi?” Kowa ta kai-ta-kai yake kamar dokin da ya kutsa kai a fagen fama.
7 Even the stork in the heavens knoweth her appointed times, And the turtle and the swallow and the crane, observe the season for coming; But my people know not the just sentence of Yahweh.
Ko shamuwa ta sararin sama ma takan san lokutan da aka tsara mata, kurciya, mashirare da kuma zalɓe sukan lura da lokacin ƙauransu. Amma mutanena ba su san abubuwan da Ubangiji yake bukata ba.
8 How can ye say, Wise, are, we, And the law of Yahweh, is with us? But indeed lo! falsely, hath dealt the false pen of the scribes!
“‘Yaya za ku ce, “Muna da hikima, gama muna da dokar Ubangiji,” alhali alƙalamin ƙarya na magatakarda ya yi ƙarya?
9 Ashamed are the wise, dismayed and captured! Lo! the word of Yahweh, have they rejected, And, what wisdom, have, they?
Za a kunyatar da masu hikima; za su yi fargaba a kuma kama su. Da yake sun ƙi maganar Ubangiji, wace irin hikima kuka ce kuke da ita?
10 Therefore, will I give—Their wives to others, Their fields to such as shall take possession of them, For from the least, even unto the greatest, Every one, is, wholly given to extortion: From the prophet even unto the priest, Every one, dealeth, falsely.
Saboda haka zan ba da matansu ga waɗansu gonakinsu kuma ga waɗansu da suka ci da yaƙi. Tun daga ƙarami har zuwa babba, kowannensu yana haɗamar cin muguwar riba; har da annabawa da firistoci ma, kowannensu yana ƙarya.
11 And so they have healed the grievous wound of the daughter of my people, slightly, —Saying, Peace! peace! when there was no peace!
Sukan ɗaura mikin mutanena sai ka ce mikin ba shi da matsala. Suna cewa, “Lafiya, Lafiya,” alhali kuwa ba lafiya.
12 Were they led to turn pale because an abominable thing, they had done? Nay! they did not, at all turn pale Nay! they did not so much as know how to exhibit shame! Therefore, shall they fall among them who are falling, In the time when they are punished, shall they be overthrown, Saith Yahweh:
Sukan ji kunyar halin banƙyamarsu kuwa? Sam, ba su da kunya ko kaɗan; ba su ma san yadda za su ji kunya ba. Saboda haka sukan fāɗi tare da fāɗaɗɗu; za su fāɗi sa’ad da aka hukunta su, in ji Ubangiji.
13 I will, surely remove, them, declareth Yahweh: There shall be no grapes on the vine Nor figs on the fig-tree, Even the leaf, hath faded, Though I have given them these things, they shall pass away from them.
“‘Zan ƙwace girbinsu, in ji Ubangiji. Ba a za sami inabi a kuringa ba. Ba za a sami’ya’ya a itacen ɓaure ba, ganyayensu kuwa za su bushe. Abin da na ba su za a ƙwace.’”
14 Why are, we, sitting still? Gather yourselves together and let us enter the defenced cities And let us be silent there, —For, Yahweh our God, hath put us to silence And made us drink poisoned water, Because we have sinned against Yahweh.
Me ya sa muke zama a nan? Mu tattaru! Mu gudu zuwa birane masu katanga mu mutu a can! Gama Ubangiji Allahnmu ya ƙaddara mana mutuwa ya kuma ba mu ruwan dafi mu sha, domin mun yi masa zunubi.
15 A waiting For prosperity, but no welfare, —For a time of healing, but lo! terror.
Mun sa zuciya ga salama amma ba lafiya, mun sa zuciya ga lokacin warkarwa amma sai ga razana.
16 From Dan, was heard the snorting of his horses At the sound of the neighing of his chargers, the whole land trembled, —Yea they came in and did sat up The land and the fulness thereof, The city, and them who were dwelling therein.
Daga Dan ana jin tirjin dawakan abokin gāba; da jin haniniyar ingarmunsu dukan ƙasar ta girgiza. Sun zo su cinye ƙasar da kome da yake cikinta, birni da dukan mazaunanta.
17 For behold me! sending among you serpents—vipers which there is no charming, —And they shall fatally bite you declareth Yahweh.
“Duba, zan aika macizai masu dafi a cikinku, kāsā, waɗanda ba su da maƙari, za su kuwa sassare ku,” in ji Ubangiji.
18 When I would have cheered myself against sorrow, Against me, mine own heart sickened: —
Ya mai ta’aziyyata a cikin baƙin ciki, zuciyata ta ɓaci ƙwarai.
19 Lo! the voice of the cry for help of the daughter of my people from a land far away, Is, Yahweh, not in Zion? Is, her King, not within her? Why, have they provoked me with their carved images, with their foreign vanities?
Ka saurari kukan mutanena daga ƙasa mai nisa suna cewa, “Ubangiji ba ya a Sihiyona ne? Sarkinta ba ya can ne kuma?” “Me ya sa suka tsokane ni da gumakansu har na yi fushi, da baƙin gumakansu marasa amfani?”
20 The harvest is passed, The fruit-gathering, is ended; And we are not saved!
“Girbi ya wuce, damuna ta ƙare, ba a kuwa cece mu ba.”
21 For the grievous injury of the daughter of my people, I am grievously injured, —I am enshrouded in gloom, Horror, hath seized me: —
Da yake an ragargazar da mutanena, an ragargaza ni ke nan; na yi kuka, tsoro ya kama ni.
22 Balsam, is there none, in Gilead? Is there no physician, there? Why hath not appeared the healing of the daughter of my people?
Ba magani ne a Gileyad? Ba likita ne a can? To, me ya sa ba warkarwa wa raunin mutanena?

< Jeremiah 8 >