< Jeremiah 47 >

1 So much of the word of Yahweh as came unto Jeremiah the prophet, Against the Philistines, —before Pharaoh smote Gaza:
Ga maganar Ubangiji da ta zo wa Irmiya annabi game da Filistiyawa kafin Fir’auna ya yaƙi Gaza.
2 Thus, saith Yahweh—Lo! waters rising from the North And they shall become a torrent overflowing, Which shall overflow The land and the fulness thereof, The city, and the dwellers therein, —Then shall men make outcry, And all the inhabitants of the land, howl.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Dubi yadda ruwaye suna tasowa a arewa; za su zama kogi mai rigyawa. Za su malala a ƙasa da kuma a kan kome da yake cikinta, garuruwa da waɗanda suke zaune a cikinsu. Mutane za su yi kuka; dukan mazaunan ƙasar za su yi kururuwa
3 Because of the sound of the tramping of the hoofs of his chargers, Because of the rushing of his chariots, the rumbling of his wheels Fathers shall not turn, to children, Because of the unnerving of their hands;
da jin motsin takawar kofatan dawakai, da jin surutun kekunan yaƙin abokin gāba da motsin ƙafafunsu. Ubanni ba za su juye don su taimaki’ya’yansu ba; hannuwansu za su yi laƙwas.
4 On account of the day that cometh to lay waste all the Philistines, To cut off from Tyre and Zidon every escaped one that could have helped, —For Yahweh is laying waste the Philistines, The remnant of the Coastland of Caphtor.
Gama rana ta zo da za a hallaka Filistiyawa a kuma datse dukan waɗanda suka ragu waɗanda za su iya taimakon Taya da Sidon. Ubangiji yana gab da hallaka Filistiyawa, raguwa daga bakin tekun Kaftor.
5 Baldness hath come, upon Gaza, Silenced is Ashkelon the remnant of their vale, —How long, wilt thou cut thyself?
Gaza za tă aske kanta cikin baƙin ciki; Ashkelon zai yi shiru. Ya raguwar da suke zama a fili, har yaushe za ku tsattsage kanku?
6 Ah! thou sword of Yahweh, How long, wilt thou not be quiet? Withdraw into thy scabbard, Rest thyself and be still.
“Za ku yi kuka kuna cewa, ‘Wayyo, takobin Ubangiji sai yaushe za ka huta? Ka koma kubenka; ka huta, ka yi shiru.’
7 How, can it be quiet, when, Yahweh, hath given it a charge, —against Ashkelon and against the shore of the sea? There, hath he appointed it!
Amma ta yaya zai huta sa’ad da Ubangiji ya umarta, sa’ad da ya umarta shi don yă faɗa wa Ashkelon da kuma bakin teku?”

< Jeremiah 47 >