< Jeremiah 21 >

1 The word which came unto Jeremiah from Yahweh, —when King Zedekiah sent unto him Pashhur, son of Malchiah, and Zephaniah, son of Maaseiah, the priest, saying:
Magana ta zo wa Irmiya daga Ubangiji sa’ad da Sarki Zedekiya ya aiki Fashhur ɗan Malkiya da firist Zefaniya ɗan Ma’asehiya gare shi. Suka ce masa,
2 Enquire for us I pray thee of Yahweh, in that, Nebuchadrezzar king of Babylon, maketh war against us, —Peradventure Yahweh will deal with us according to all his wonders, so that he go up from us.
“Yanzu ka roƙi mana Ubangiji saboda Nebukadnezzar sarkin Babilon yana kawo mana yaƙi. Wataƙila Ubangiji zai yi mana waɗansu abubuwa banmamaki kamar a lokacin baya don yă janye daga gare mu.”
3 Then said Jeremiah unto them, —Thus, shall ye say unto Zedekiah:
Amma Irmiya ya amsa musu ya ce, “Ku faɗa wa Zedekiya cewa,
4 Thus, saith Yahweh, God of Israel—Behold me! turning back the weapons of war that are in your hand, wherewith, ye, are fighting the king of Babylon and the Chaldeans, who are besieging you outside the wall, —and I will gather them into the midst of this city.
‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yake cewa ina shirin juya kayan yaƙin da suke a hannuwanka a kanka, waɗanda kake amfani don ka yaƙi sarki Babilon da kuma Babiloniyawa waɗanda suka kewaye katangar birnin, zan kuwa tsiba kayan yaƙinka a tsakiyar birnin nan.
5 And I myself, will fight against you, with a hand outstretched, and with an arm of strength, —and with anger and with wrath and with great indignation;
Ni da kaina zan yi yaƙi da kai da miƙaƙƙen hannu mai ƙarfi cikin fushi da hasala mai girma.
6 and I will smite the inhabitants of this city, both man and beast, —of a great pestilence, shall they die.
Zan kashe waɗanda suke zaune a wannan birni, mutane da dabbobi za su kuwa mutu da muguwar annoba.
7 And after that, Declareth Yahweh—Will I deliver Zedekiah king of Judah and his servants, and the people—even such as are left in this city from the pestilence from the sword and from the famine, —into the hand of Nebuchadrezzar king of Babylon, even into the hand of their enemies, and into the hand of them who are seeking their life, —and he will smite them with the edge of the sword, he will not have pity on them nor will he spare nor will he have compassion.
Bayan wannan, in ji Ubangiji, zan ba da Zedekiya sarkin Yahuda, fadawansa da kuma mutanen wannan birni waɗanda suka tsira daga annoba, takobi da kuma yunwa, ga Nebukadnezzar sarkin Babilon da kuma ga abokan gābansu waɗanda suke neman ransu. Zai kashe su da takobi; ba zai ji tausayinsu ko ya yi musu jinƙai ko ya yi juyayinsu ba.’
8 And unto this people, shalt thou say, Thus, saith Yahweh, —Behold me! setting before you the way, of life, and the way of death:
“Bugu da ƙari, ka faɗa wa mutanen cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ga shi na sa a gabanku hanyar rai da hanyar mutuwa.
9 He that remaineth in this city, shall die—by the sword or by the famine or by the pestilence, —Whereas, he that goeth forth and falleth unto the Chaldeans, who are besieging you, —then shall he live, and, his life, shall become to him, a spoil;
Duk wanda ya zauna a wannan birni zai mutu ta takobi, yunwa ko annoba. Amma duk wanda ya fita ya miƙa kansa ga Babiloniyawa waɗanda suka kewaye ku zai rayu; zai kuɓutar da ransa.
10 For I have set my face against this city, for calamity and not for blessing, Declareth Yahweh, —Into the hand of the king of Babylon, shall it be given up, and he will burn it with fire.
Na ƙudura in yi wa wannan birni lahani ba alheri ba, in ji Ubangiji. Za a ba da shi a hannuwan sarki Babilon, zai kuwa hallaka shi da wuta.’
11 Now, as to the house of the king of Judah, —hear ye the word of Yahweh: —
“Ban haka ma, ka faɗa wa gidan sarauta na Yahuda cewa, ‘Ku saurari maganar Ubangiji;
12 O house of David! Thus, saith Yahweh, Administer justice betimes, And deliver the robbed out of the hand of the oppressor, —Lest mine indignation come forth like fire And burn and there be none to quench it, Because of the wickedness of your doings:
Ya gidan Dawuda ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Ku yi gaskiya kowace safiya; ku kuɓuta daga hannun mai danniya wannan da aka yi wa fashi in ba haka ba hasalata za tă sauka ta kuma ci kamar wuta saboda muguntar da kuka aikata za tă ci babu wanda zai kashe ta.
13 Behold me! against thee, O thou dweller in the vale on the level rock, Declareth Yahweh, —Ye who are saying, Who shall come down upon us? Who shall enter our habitations?
Ina gāba da ku, mazaunan Urushalima, ku da kuke zama a bisa wannan kwari kan dutsen da yake a fili, in ji Ubangiji ku da kuke cewa, “Wa zai iya yaƙe mu? Wa zai iya shiga mafakarmu?”
14 Yet will I bring punishment upon you according to the fruit of your doings, Declareth Yahweh, —and will kindle a fire in her forest, and it shall devour all things round about her.
Zan hukunta ku gwargwadon ayyukanku, in ji Ubangiji. Zan sa wuta a kurminku da za tă cinye kome da yake kewaye da ku.’”

< Jeremiah 21 >