< Isaiah 62 >

1 For Zion’s sake, will I not hold my peace, And for Jerusalem’s sake, will I not rest, —Until her righteousness, go forth as brightness, And her salvation, as a torch that is lighted.
Saboda Sihiyona ba zan yi shiru ba, saboda Urushalima ba zan huta ba, sai adalcinta ya haskaka kamar hasken safiya, cetonta kuma ya haskaka kamar fitila mai haske.
2 So shall nations see thy righteousness, And all kings, thy glory; And thou shalt be called by a new name, which, the mouth of Yahweh, will name.
Al’ummai za su ga adalcinki, sarakuna kuma za su ga ɗaukakarki; za a kira ki da sabon suna sunan da bakin Ubangiji zai ambata.
3 Then shalt thou become—A crown of adorning, in the hand of Yahweh, and A royal diadem in the hand of thy God.
Za ki zama rawanin daraja a hannun Ubangiji, rawanin sarauta a hannun Allahnki.
4 Thou shalt he termed no longer—Forsaken Nor shall thy land be termed any longer A desolation, But, thou, shalt be called Hephzibah ["My delight is in her"], And, thy land, Beulah ["married"], —For Yahweh hath found delight in thee, And thy land, shall be married.
Ba za a ƙara ce da ke Yasasshiya ba, ko a kira ƙasarki Kango. Amma za a ce da ke Hefziba ƙasarki kuma Bewula; gama Ubangiji zai ji daɗinki, ƙasarki kuma za tă yi aure.
5 For a young man marrieth, a virgin, Thy sons marry thee! And the bridegroom rejoiceth over the bride—Thy God, rejoiceth over thee.
Kamar yadda saurayi kan auri yarinya, haka’ya’yanki maza za su aure ki; kamar kuma yadda ango yakan yi farin ciki da amaryarsa, haka Allahnki zai yi farin ciki da ke.
6 Upon thy walls O Jerusalem, have I appointed watchmen, All the day and all the night through, let them not hold their peace, —O ye that put Yahweh in mind, Do not take rest to yourselves,
Na sa matsara a kan katangarki, ya Urushalima; ba za su taɓa yin shiru ba, dare da rana. Ku da kuke kira bisa sunan Ubangiji, kada ku ba kanku hutu,
7 Neither give rest, unto him, Until he establish and until he set forth Jerusalem as a praise in the earth!
kuma kada ku ba shi hutu sai ya kafa Urushalima ya kuma mai da ita yabon duniya.
8 Sworn hath Yahweh—By his own right hand, and By his own strong arm, —Surely I will give thy corn no more, as food to thine enemies, Nor shall the sons of the foreigner drink thy new wine, for which thou hast toiled;
Ubangiji ya rantse da hannunsa na dama ta hannunsa kuma mai iko cewa, “Ba zan ƙara ba da hatsinki ya zama abinci ga abokan gābanki ba, baƙi kuma ba za su ƙara shan ruwan inabin wanda kika sha wahala samu ba;
9 But they who have garnered it, shall eat it, and praise Yahweh, —And they who have gathered in its clusters, shall drink it in my holy courts.
amma waɗanda suka girbe shi za su ci shi su kuma yabi Ubangiji, waɗanda kuma suka tattara’ya’yan inabi za su sha shi a filayen wurina mai tsarki.”
10 Pass ye through pass ye through the gates, Prepare ye the way of the people, —Cast ye up, cast ye up the highway, Clear it of stones, Lift ye high a standard unto the peoples.
Ku wuce, ku wuce ƙofofi! Ku shirya hanya saboda mutane. Ku gina, ku gina babbar hanya! Ku kawar da duwatsu. Ku ɗaga tuta saboda al’ummai.
11 Lo! Yahweh, hath sent a message unto the end of the earth: Say ye to the daughter of Zion, Lo! thy Salvation, is coming, —Lo! his reward, is with him, And, his recompense, before him:
Ubangiji ya yi shela ga iyakokin duniya cewa, “Faɗa wa Diyar Sihiyona, ‘Ga Mai Cetonki yana zuwa! Ga ladarsa tana tare da shi, sakamakonsa yana raka shi.’”
12 So shall men call them—The holy people The redeemed of Yahweh, —And, thou, shalt be called—Sought out, A city not forsaken,
Za a ce da shi Tsattsarkar Mutane, Fansassu na Ubangiji; za a kuma ce da ke Wadda Aka Nema Birnin da Ba Za a Ƙara Yashe ta ba.

< Isaiah 62 >