< Isaiah 6 >

1 In the year that King Uzziah died, I saw My Lord, sitting upon a throne high and lifted up, and, his skirts, did fill the temple,
A shekarar da Sarki Uzziya ya mutu, na ga Ubangiji zaune a kan kujerar sarauta a sama cike da ɗaukaka, zatinsa ya cika haikali.
2 Seraphim, were standing above him; six wings severally, had each one, —With twain, he covered his face And with twain, he covered his feet And with twain, he did fly.
A bisansa akwai serafofi, kowanne yana da fikafikai shida. Fikafikai biyu sun rufe fuskokinsu, da biyu suka rufe ƙafafunsu, biyu kuma da su suke tashi.
3 And they continued crying out one to another, and said, Holy—holy—holy, is Yahweh of hosts, —the fulness of the whole earth, is his glory.
Suna kiran juna, “Mai Tsarki, Mai Tsarki, Mai Tsarki! Ubangiji Maɗaukaki ne; duniya ta cika da ɗaukakarsa.”
4 And the foundations of the porch, were moved at the voice of him that cried, —and the house, was filled with smoke.
Da jin ƙarar muryoyinsu madogarai da madogaran ƙofa suka girgiza, haikali kuma ya cika da hayaƙi.
5 Then said I—Woe to me!—for I am undone, Because a man of unclean lips, am, I, And in the midst of a people of unclean lips, do I dwell, —For the King. Yahweh of hosts, have mine eyes seen!
Sai na tā da murya na ce, “Kaitona! Na shiga uku! Gama ni mutum ne mai leɓuna marar tsarki, kuma ina raye a cikin mutane masu leɓuna marasa tsarki, idanuna kuma sun ga Sarki, Ubangiji Maɗaukaki.”
6 Then flew unto me one of the seraphim, And in his hand, a live coal, —With tongs, had he taken it from off the altar.
Sai ɗaya daga cikin serafofin ya yi firiya zuwa wurina tare da garwashi mai wuta a hannunsa, wanda ya ɗiba da arautaki daga bagade.
7 Then touched he my mouth, and said—Lo! this hath touched thy lips, —Thus shall be taken away, thine iniquity, And, thy sin, by propitiation be covered.
Da shi ne ya taɓa bakina ya ce, “Duba, wannan ya taɓa leɓunanka, yanzu fa an kawar da laifofinka, an kuma gafarta maka zunubanka.”
8 Then heard I the voice of My Lord, saying, Whom shall I send? And who will go for us? And I said—Here am I—send me.
Sa’an nan na ji muryar Ubangiji tana cewa, “Wa zan aika? Wa zai tafi mana?” Sai na ce, “Ga ni! Ka aike ni!”
9 Then said he—Go and say unto this people, —Hear on but do not discern, See on but do not perceive:
Ya ce, “Je ka ka faɗa wa wannan mutane, “‘Kome yawan kasa kunne da za ku yi, ba za ku fahimta ba; Kome yawan dubar da za ku yi, ba za ku san abin da yake faruwa ba.’
10 Stupefy thou the heart of this people, And their ears, make thou heavy, And their eyes, overspread, —Lest they see with their eyes And with their ears, should hear, And their heart should discern and come back. And they be healed.
Ka sa zuciyar mutanen nan ta dushe; kunnuwansu su kurunce, idanunsu kuma su makance. In ba haka ba za su iya gani da idanunsu, su ji da kunnuwansu, su fahimta da zuciyarsu, su kuma juyo a kuma warkar da su.”
11 Then said I—How long, My Lord? And he said—Until the time that Cities be wasted through having no inhabitant And houses—through having no men, And, the ground, be laid waste unto desolation;
Sa’an nan na ce, “Har yaushe, ya Ubangiji?” Ya kuma amsa, “Sai an lalatar da biranen ba kowa a ciki, sai an mai da gidaje kangwaye ƙasa kuma ta zama kango ba amfani,
12 And Yahweh have far removed men, —And great! be the abandonment in the midst of the land.
sai lokacin da Ubangiji ya kori kowa aka kuma yashe ƙasar gaba ɗaya.
13 Yet still shall there be in it a tenth, Though it again be consumed, —Like an oak and like a terebinth Which when felled, have a stock in them, A holy seed, shall be the stock thereof.
Ko da yake kashi ɗaya bisa goma zai ragu a ƙasar, za tă sāke zama kango. Amma kamar yadda katambiri da itacen oak sukan bar kututturai sa’ad da aka yanke su, haka iri mai tsarkin nan zai zama kututture a ƙasar mai tsarki.”

< Isaiah 6 >