< Isaiah 44 >

1 Now, then—hear, O Jacob, my Servant, —and Israel whom I have chosen:
“Amma yanzu ka saurara, ya Yaƙub, bawana, Isra’ila, wanda zaɓa.
2 Thus, saith Yahweh—Who made thee and formed thee from birth, Who helpeth thee: Do not fear O my Servant Jacob, and Jeshurun whom I have chosen;
Ga abin da Ubangiji yana cewa, shi wanda ya yi ka, wanda ya siffanta ka a cikin mahaifa, wanda kuma zai taimake ka. Kada ka ji tsoro, ya Yaƙub, bawana, Yeshurun, wanda na zaɓa.
3 For I will pour, Water upon the thirsty soil, and Floods upon the dry ground, —I will pour My spirit upon thy seed, and My blessing upon thine offspring;
Gama zan zuba ruwa a ƙeƙasasshiyar ƙasa, rafuffuka kuma a busasshiyar ƙasa; zan ba da Ruhuna ga’ya’yanka, albarkata kuma ga zuriyarka.
4 So will they spring up among the grass, As willows by the water-courses:
Za su tsiro kamar ciyawa a wuriyar ruwa, kamar kurmi kusa da rafuffuka masu gudu.
5 This one, will say Yahweh’s, am I, and That one, will call himself by the name of Jacob, and Yonder one will write on his hand—Yahweh’s, And after the name of Israel, will one entitle himself.
Wani zai ce, ‘Ni na Ubangiji ne’; wani kuma zai kira kansa da sunan Yaƙub; har yanzu wani zai rubuta a hannunsa, ‘Na Ubangiji,’ ya kuma ɗauki sunan Isra’ila.
6 Thus saith Yahweh—King of Israel, Even his Redeemer, Yahweh of hosts, —I, am, First, and, I, Last, And besides me, there is no God.
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, Sarki da kuma Mai Fansar Isra’ila, Ubangiji Maɗaukaki. Ni ne farko ni ne kuma ƙarshe; in ban da ni babu wani Allah.
7 Who then, like me, can call, and declare it, and order it, for me, Seeing that I appointed an age-abiding people, —Or things yet to be, and that shall come to pass, Let them declare on their part.
Wane ne kuwa kama da ni? Ya faɗa a ji. Bari yă yi shela ya kuma nuna shi a gabana mene ne ya faru tun da na kafa mutanena na dā, mene ne kuma bai riga ya faru ba, I, bari yă faɗa abin da zai zo.
8 Do not ye dread, nor yet be alarmed, Have I not from olden time, told thee and declared? So that, ye, are my witnesses, —Whether there is a GOD besides me? Or is no Rock—I knew of none!
Kada ku firgita kada kuma ku ji tsoro. Ban furta wannan na kuma yi faɗar haka tuntuni ba? Ku ne shaiduna. Akwai wani Allah in ban da ni? A’a, babu wani Dutse; ban san da wani ba.”
9 The fashioners of an image—all of them, are emptiness, And, the things they delight in, cannot profit, —And, their, witnesses, they, neither see nor know, That they may be ashamed.
Duk masu yin gumaka ba kome ba ne, da kuma abubuwan da suke ɗauka da daraja banza ne. Waɗanda za su yi magana a madadinsu makafi ne; jahilai ne, marasa kunya.
10 Who hath fashioned a GOD, Oran image, hath molten? It cannot profit!
Waɗanda suke siffanta allah su kuma yi zubin gunki, waɗanda ba za su yi musu ribar kome ba?
11 Lo! all his partners, turn pale, Even, the artificers themselves, are of the sons of earth, —Let them gather themselves together—all of them. Let them take their stand, Let them dread, and turn pale, together!
Shi da irinsa za su sha kunya; masu sassaƙa ba kome ba mutane ne kurum. Bari su tattaru su ɗauki matsayinsu; za su firgita su kuma sha mummunan kunya.
12 As for the smith, [with his] cutting-tool, —When he hath wrought in the live coals, And, with hammers, hath fashioned it, —And hath wrought it with his strong arm, Anon he is hungry, and hath no strength, He hath drunk no water and so hath become faint!
Maƙeri yakan ɗauki kayan aiki ya yi aiki da shi a cikin garwashi; ya ƙera gunki da guduma, ya gyara shi da hannuwansa masu ƙarfi. Yakan ji yunwa ya kuma rasa ƙarfi; yakan sha ruwa ya kuma ji gajiya.
13 As for the carpenter, —He hath stretched out a line hath drawn it with a pencil, Hath made it with carving tools, With compasses, hath rounded it, —And so hath made it after the figure of a great man, After the beauty of a son of earth, that it may remain in a house!
Kafinta yakan gwada katako yă kuma zāna siffar da alli; yă goge shi da kayan aiki yă kuma zāna shi da alƙalami. Yă siffanta shi a kamannin mutum, mutum cikin dukan darajarsa, don yă ajiye shi a cikin masujada.
14 When one was cutting him down cedars, Then took he a holm-tree and an oak, And secured them for himself, among the trees of the forest, —He planted a fir-tree and the pouring rain made it grow;
Yakan ka da itacen saifires, ko kuwa ya ɗauki saifires ko oak. Yă bar shi yă yi girma a cikin itatuwan kurmi, ko yă shuka itacen fir, ruwan sama kuma yă sa yă yi girma.
15 So it serveth for a man to burn, And he hath taken of the branches and warmed himself, Also he kindleth a fire, and baketh bread, —Also he maketh a GOD, and hath bowed himself down, Hath made of it a carved image, and adored it:
Abin hura wutar mutum ne; yakan ɗebi waɗansu yă hura wuta don yă ji ɗumi, ya hura wuta yă gasa burodi. Amma yakan ƙera zinariya yă kuma yi masa sujada; yakan yi gunki sa’an nan yă rusuna masa.
16 The half thereof, hath he burned in the fire, Over half thereof, he eateth flesh, He roasteth roast, that he may be satisfied, —Also he warmeth himself, and saith, Aha, I am warm, I have seen a blaze;
Rabin katakon yakan ƙone a wuta; a kansa yakan dafa abincinsa, yă gasa namansa yă kuma ci sai ya ƙoshi. Yakan ji ɗumi yă kuma ce, “Aha! Na ji ɗumi; na gan wutar.”
17 And the residue thereof, Into a GOD, he maketh, Into his carved image, —Adoreth it, and boweth down and prayeth unto it, And saith Deliver me, for, my GOD, thou art!
Da sauran itacen yakan yi allah, gunkinsa; yă rusuna masa yă kuma yi sujada. Yakan yi masa addu’a yă ce, “Ka cece ni; kai ne allahna.”
18 They have not taken note, neither can they perceive, —He hath besmeared—past seeing—their eyes, Past understanding, their hearts;
Ba su san kome ba, ba su fahimci kome ba; an rufe idanunsu don kada su gani, tunaninsu kuma a rufe don kada su fahimta.
19 And no one reflecteth—There is neither knowledge nor discernment—to say, Half thereof, have I burned up in the fire Moreover also I have baked, on the coals thereof, bread, I roasted flesh, and have been eating, —And of the remainder thereof, an abomination, shall I make? And, to a log of wood, shall I pay adoration?
Ba wanda yakan dakata ya yi tunani, ba wanda yake da sani ko fahimi ya ce, “Da rabinsa na yi amfani da shi don hura wuta; na ma gasa burodi a kan garwashinsa, na gasa nama na kuma ci. Ya kamata in yi abin ƙyama daga abin da ya rage? Ya kamata in rusuna wa guntun katako?”
20 He is feeding on ashes, A deluded heart, hath turned him aside, —And he cannot deliver his own soul nor say, Is there not a falsehood in my right hand?
Yana cin toka, zuciyar da ta ruɗe tana ɓad da shi; ba zai iya cece kansa ba, ko ya ce, “Wannan abin da yake hannun dama na ba ƙarya ba ne?”
21 Remember these things, O Jacob, And, Israel, —for, my Servant, thou art, —I have fashioned thee, a Servant of mine, thou art.
“Tuna da waɗannan abubuwa, ya Yaƙub, gama kai bawana ne, ya Isra’ila. Na yi ka, kai bawana ne; Ya Isra’ila, ba zan manta da kai ba.
22 O Israel, thou shalt not be forgotten of me, I have wiped out, As with a thick cloud, thy transgressions, And as with a broad cloud, thy sins, —Return unto me, for I have redeemed thee.
Na shafe laifofinka kamar girgije, zunubanka kamar hazon safe. Ka komo wurina, gama na kuɓutar da kai.”
23 Shout in triumph ye heavens for Yahweh, hath effectually wrought. Shout, O ye underparts of the earth, Ring out, Ye mountains, into cries of triumph, Thou forest, and every tree therein, —For, Yahweh, hath redeemed, Jacob, And in Israel, will he get himself glory.
Ku rera don farin ciki, ya sammai, gama Ubangiji ya aikata wannan; ku yi sowa, ya duniya a ƙarƙashi. Ku ɓarke da waƙoƙi, ku duwatsu, ku jeji da dukan itatuwanku, gama Ubangiji ya kuɓutar da Yaƙub, ya nuna ɗaukakarsa a cikin Isra’ila.
24 Thus, saith Yahweh Who hath redeemed thee, Who hath fashioned thee from birth, —I—Yahweh, am the maker of all things, Stretching out the heavens, alone, Spreading forth the earth, of myself;
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansarka, wanda ya yi ka a cikin mahaifa. “Ni ne Ubangiji, wanda ya yi dukan abubuwa, wanda ya shimfiɗa sammai ya kuma kafa harsashen duniya da kansa,
25 Frustrating the signs of praters, And, diviners, he confoundeth, —Turning wise men backwards, And their knowledge, he maketh folly;
wanda ya sassāke alamun annabawan ƙarya ya masu duba suka zama wawaye, wanda ya tumɓuke koyon masu hikima ya mai da shi banza,
26 Establishing the word of his Servant, And the counsel of his Messengers, he maketh good, —Who saith of Jerusalem—She shall be inhabited! And of the cities of Judah—They shall be built! And the ruins thereof, will I set up!
wanda ya tabbatar da maganganun bayinsa ya kuma cika annabce-annabcen’yan aikansa, “wanda ya ce game da Urushalima, ‘Za a zauna a cikinta,’ game da garuruwan Yahuda, ‘Za a gina su,’
27 Who saith to the deep—Be dry and Thy rivers, will I drain!
wanda ya ce wa zurfin ruwaye, ‘Ku bushe, zan kuma busar da rafuffukanku,’
28 Who saith of Cyrus—My Shepherd! and All my pleasure, shall he make good Even saying of Jerusalem—She shall be built! And of the temple—Be her foundation laid!
wanda ya yi zancen Sairus ya ce, ‘Shi ne makiyayina zan kuma cika dukan abin da na gan dama; zai yi zancen Urushalima cewa, “Bari a sāke gina ta,” game da haikali kuma cewa, “Bari a kafa harsashinsa.”’

< Isaiah 44 >