+ Genesis 1 >

1 In the beginning, God created the heavens and the earth.
A farko-farko, Allah ya halicci sama da ƙasa.
2 Now, the earth, had become waste and wild, and darkness, was on the face of the roaring deep, —but, the Spirit of God, was brooding on the face of the waters,
To, ƙasa dai ba ta da siffa, babu kuma kome a cikinta, duhu ne kawai ya rufe ko’ina, Ruhun Allah kuwa yana yawo a kan ruwan.
3 And God said—Light, be, And light was.
Sai Allah ya ce, “Bari haske yă kasance,” sai kuwa ga haske.
4 And God saw the light, that it was, good, and God divided the light, from the, darkness;
Allah ya ga hasken yana da kyau, sai ya raba tsakanin hasken da duhu.
5 and God called the light, day, but the darkness, called he, night. So it was evening—and it was morning, one day.
Allah ya kira hasken “yini,” ya kuma kira duhun “dare.” Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta fari ke nan.
6 And God said, Let there be an expanse in the midst of the waters, and let it be a means of dividing, between waters and waters,
Allah ya ce, “Bari sarari yă kasance tsakanin ruwaye domin yă raba ruwa da ruwa.”
7 And God made the expanse, and it divided between the waters that were under the expanse and the waters that were above the expanse. And it was so.
Saboda haka Allah ya yi sarari ya raba ruwan da yake ƙarƙashin sararin da ruwan da yake bisansa. Haka kuwa ya kasance.
8 And God called the expanse, heavens. So it was evening—and it was morning, a, second day.
Allah ya kira sararin “sama.” Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta biyu ke nan.
9 And God said—Let the waters under the heavens be gathered together, into one place, and let the dry—ground appear. And it was so.
Allah ya ce, “Bari ruwan da yake ƙarƙashin sama yă tattaru wuri ɗaya, bari kuma busasshiyar ƙasa tă bayyana.” Haka kuwa ya kasance.
10 And God called, the dry-ground, land, but the gathering together of the waters, called he seas. And God saw that it was good.
Allah ya kira busasshiyar ƙasar “doron ƙasa,” ruwan da ya taru kuma, ya kira “tekuna.” Allah ya ga yana da kyau.
11 And God said—Let the land put-forth vegetation—herb yielding seed, fruit-tree, bearing fruit after its kind, whose seed is within it on the land. And it was so,
Sa’an nan Allah ya ce, “Bari ƙasa tă fid da tsire-tsire, da shuke-shuke, da itatuwa a bisa ƙasa masu ba da amfani da’ya’ya a cikinsu, bisa ga irinsu.” Haka kuwa ya kasance.
12 And the land brought-forth vegetation—herb yielding seed after its kind, and tree bearing fruit, whose seed is within it, after its kind, And God saw that it was good.
Ƙasar ta fid da tsire-tsire, da shuke-shuke masu ba da’ya’ya bisa ga irinsu, ta fid kuma da itatuwa masu ba da’ya’ya da iri a cikinsu bisa ga irinsu. Allah ya ga yana da kyau.
13 So it was evening—and it was morning, a third day.
Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta uku ke nan.
14 And God said—Let there be luminaries in the expanse of the heavens, to divide between the day and the night, —and let them be for signs, and for seasons, and for days and years;
Allah kuma ya ce, “Bari haskoki su kasance a sararin sama domin su raba yini da dare, bari su zama alamu domin su nuna yanayi, da ranaku, da kuma shekaru,
15 yea let them be for luminaries in the expanse of the heavens, to give light on the earth. And it was so.
bari kuma haskokin su kasance a sararin sama domin su ba da haske a duniya.” Haka kuwa ya kasance.
16 And God made the two great luminaries, —the greater luminary to rule the day, and the lesser luminary to rule the night, also the stars.
Allah ya yi manyan haskoki biyu, babban hasken yă mallaki yini, ƙaramin kuma yă mallaki dare. Ya kuma yi taurari.
17 And God set them in the expanse of the heavens, —to give light on the earth;
Allah ya sa su a sararin sama domin su ba da haske a duniya,
18 and to rule over the day and over the night, and to divide the light from the darkness. And God saw that it was good.
su mallaki yini da kuma dare, su kuma raba haske da duhu. Allah kuwa ya ga yana da kyau.
19 So it was evening—and it was morning, a fourth day.
Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta huɗu ke nan.
20 And God said—Let the waters swarm with an abundance of living soul, and, birds, shall fly over the earth, over the face of the expanse of the heavens.
Allah ya ce, “Bari ruwa yă cika da halittu masu rai, bari tsuntsaye kuma su tashi sama a bisa duniya a sararin sama.”
21 And God created the great sea-monsters, —and every living soul that moveth—[with] which the waters swarmed after their kind and every winged bird—after its kind. And God saw that it was good.
Allah ya halicci manyan halittun teku, da kowane mai rai da abin da yake motsi a ruwa, bisa ga irinsu, da kuma kowane tsuntsu mai fiffike bisa ga irinsa. Allah kuwa ya ga yana da kyau.
22 And God blessed them, saying, —Be fruitful and multiply, and fill the waters in the seas, and let, the birds, multiply in the land.
Allah ya albarkace su ya ce, “Ku yi ta haihuwa ku kuma ƙaru da yawa, ku cika ruwan tekuna, bari kuma tsuntsaye su yi yawa a bisa duniya.”
23 So it was evening—and it was morning, a fifth day.
Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta biyar ke nan.
24 And God said—Let the land, bring forth, living soul, after its kind, tame-beast and creeping thing and wild-beast, of the land, after its kind. And it was so.
Allah kuwa ya ce, “Bari ƙasa tă ba da halittu masu rai bisa ga irinsu; dabbobi da halittu masu rarrafe, da kuma namun jeji, kowane bisa ga irinsa.” Haka kuwa ya kasance.
25 And God made the wild-beast of the land after its kind, and the tame-beast after its kind, and every creeping thing of the ground, after its kind. And God saw that it was good.
Allah ya halicci namun jeji bisa ga irinsu, dabbobi bisa ga irinsu, da kuma dukan halittu masu rarrafe a ƙasa bisa ga irinsu. Allah kuwa ya ga yana da kyau.
26 And God said—Let us make man in our image after our likeness—and let them have dominion over the fish of the sea, and over the bird of the heavens and over the tame-beast—and over all the land, and over every creeping thing, that creepeth on the land.
Sa’an nan Allah ya ce, “Bari mu yi mutum cikin siffarmu, cikin kamanninmu, bari kuma su yi mulki a bisa kifin teku, tsuntsayen sama, da kuma dabbobi, su yi mulki a bisa dukan duniya, da kuma a bisa dukan halittu, da masu rarrafe a ƙasa.”
27 And God created the man in his own image, In the image of God, created he him, —Male and female, created he, them.
Saboda haka Allah ya halicci mutum cikin siffarsa. Cikin kamannin Allah, Allah ya halicci mutum. Miji da mace ya halicce su.
28 And God blessed them, and God said to them Be fruitful and multiply and fill the earth and subdue it, —and have dominion over the fish of the sea and over the bird of the heavens, and over every living thing that moveth on the land.
Allah ya albarkace su, ya kuma ce musu, “Ku yi ta haihuwa ku ƙaru da yawa, ku mamaye duniya, ku mallake ta. Ku yi mulki a bisa kifin teku, da tsuntsayen sararin sama, da kuma bisa kowace halitta mai rai wadda take rarrafe a ƙasa.”
29 And God said—Lo! I have given to you—every herb yielding seed which is on the face of all the land, and every tree wherein is the fruit of a tree yielding seed, —to you, shall it be, for food;
Sa’an nan Allah ya ce, “Ga shi, na ba ku kowane tsiro mai ba da’ya’ya masu kwaya da suke a fāɗin duniya, da dukan itatuwa masu ba da’ya’ya, don su zama abinci a gare ku.
30 and to every living thing of the land—and to every bird of the heavens, and to every thing that moveth on the land, wherein is a living soul, every green herb for food. And it was so.
Na kuma ba da dukan dabbobin ƙasa, da dukan tsuntsayen sama, da dukan abin da yake rarrafe a ƙasa, da dai iyakar abin da yake numfashi; haka kuma na ba da ganyaye su zama abinci.” Haka kuwa ya kasance.
31 And God saw every thing which he had made, and lo! it was very good. So it was evening—and it was morning, the sixth day.
Allah ya ga dukan abin da ya yi, yana da kyau ƙwarai. Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta shida ke nan.

+ Genesis 1 >