< Ezra 8 >

1 Now, these, are their ancestral heads, and their genealogical register, —even of those who came up with me, in the reign of Artaxerxes the king, out of Babylon: —
Waɗannan su ne shugabannin iyalai, da kuma waɗanda suka dawo tare da ni daga Babilon a zamanin mulkin Sarki Artazerzes.
2 Of the sons of Phinehas, Gershom, of the sons of Ithamar, Daniel, —of the sons of David, Hattush;
Daga zuriyar Finehas, Gershom ne shugaba; daga zuriyar Itamar, Daniyel ne shugaba; daga zuriyar Dawuda, Hattush
3 Of the sons of Shecaniah, of the sons of Parosh, Zechariah, —and, with him—by genealogical registry of males, a hundred and fifty:
ɗan zuriyar Shekaniya ne shugaba, daga zuriyar Farosh, Zakariya ne shugaba, tare da shi akwai mutum 150;
4 Of the sons of Pahath-moab, Eliehoenai, son of Zerahiah, —and, with him, two hundred males;
daga Fahat-Mowab, Eliyehoyenai ɗan Zerahiya ne shugaba, tare da shi akwai mutum 200;
5 Of the sons of Zattu, Shecaniah, the son of Jehaziel, —and, with him, three hundred males;
daga zuriyar Zattu, Shekaniya ɗan Yahaziyel ne shugaba, tare da shi akwai mutum 300;
6 And, of the sons of Adin, Ebed, son of Jonathan, —and, with him, fifty males;
daga zuriyar Adin, Ebed ɗan Yonatan ne shugaba, tare da shi akwai mutum 50;
7 And, of the sons of Elam, Jeshaiah, son of Athaliah, —and, with him, seventy males;
daga zuriyar Elam, Yeshahiya ɗan Ataliya ne shugaba, tare da shi akwai mutum 70;
8 And, of the sons of Shephatiah, Zebadiah, son of Michael, —and, with him, eighty males;
daga zuriyar Shefatiya, Zebadiya ɗan Mika’ilu ne shugaba, tare da shi akwai mutum 80;
9 Of the sons of Joab, Obadiah, son of Jehiel, and, with him, two hundred and eighteen males;
daga iyalin Yowab, Obadiya ɗan Yehiyel ne shugaba, tare da shi akwai mutum 218;
10 And, of the sons of Bani, Shelomith, son of Josiphiah, —and, with him, a hundred and sixty males;
daga Bani, Shelomit ɗan Yosifiya ne shugaba, tare da shi akwai mutum 160;
11 And, of the sons of Bebai, Zechariah, son of Bebai, and, with him, twenty-eight males;
daga Bebai, Zakariya ɗan Bebai ne shugaba, tare da shi akwai mutum 28;
12 And, of the sons of Azgad, Johanan, son of Hakkatan, —and, with him, a hundred and ten males;
daga iyalin Azgad, Yohanan ɗan Hakkatan ne shugaba, tare da shi akwai mutum 110;
13 And, of the later sons of Adonikam, these being their names, Eliphelet, Jeuel, and Shemaiah, —and, with them, sixty males;
zuriya ta Adonikam ne suka zo daga ƙarshe, sunayensu kuwa su ne Elifelet, Yehiyel da Shemahiya, tare da su akwai mutum 60;
14 And, of the sons of Bigvai, Uthai and Zabbud, —and, with him, seventy males.
daga zuriyar Bigwai, Uttai da Zakkur ne shugabanni, tare da su akwai mutum 70.
15 And I gathered them together, unto the river that cometh into Ahava, and we encamped there three days, —and I informed myself among the people and the priests, and, of the sons of Levi, found I none there.
Na kuma tattara su a bakin rafi wanda yake gangarawa zuwa Ahawa, muka kafa sansani a can kwana uku. Da na bincika cikin mutane da firistoci, sai na tarar babu Lawiyawa.
16 So I sent for Eliezer, for Ariel, for Shemaiah, and for Elnathan, and for Jarib, and for Elnathan, and for Nathan, and for Zechariah, and for Meshullam, chief men, —also for Joiarib and for Elnathan, teachers.
Saboda haka sai na aika a kira Eliyezer, da Ariyel, da Shemahiya, da Elnatan, da Yarib, da Natan, da Zakariya, da Meshullam waɗanda su ne shugabanni. Na kuma sa a kira Yohiyarib da Elnatan waɗanda masana ne.
17 And I sent them forth unto Iddo the chief, at the place Casiphia, —and I put into their mouth words, to speak unto Iddo and his brethren the Nethinim, at the place Casiphia, to bring unto us attendants for the house of our God.
Na sa su je wurin Iddo wanda yake shugaba a Kasifiya. Aka gaya musu abin da za su gaya wa Iddo da’yan’uwansa masu aiki a haikali a Kasifiya don su aiko mana waɗanda za su yi mana hidima a haikalin Allahnmu.
18 So they brought unto us, according to the good hand of our God upon us, a man of discretion, of the sons of Mahli, son of Levi, son of Israel, —and Sherebiah, and his sons and his brethren, eighteen;
Da yake Allah yana tare da mu, sai suka aiko mana da Sherebiya, wanda ya iya aiki, shi daga zuriyar Mali ɗan Lawi ne, ɗan Isra’ila. Sai ya zo tare da’ya’yansa da kuma’yan’uwansa. Dukansu dai mutum 18 ne.
19 and Hashabiah, and, with him, Jeshaiah, of the sons of Merari, —his brethren and their sons, twenty;
Suka kuma aika da Hashabiya tare da Yeshahiya daga zuriyar Merari, da’yan’uwansu da kuma’ya’yansu, su kuma mutum 20 ne.
20 and, of the Nethinim whom David and the rulers had given for the service of the Levites, Nethinim, two hundred and twenty, —all of them, expressed by name.
Sun kuma kawo masu aiki a haikali mutum 220, ƙungiyar da Dawuda da abokan aikinsa suka keɓe don su taimaki Lawiyawa aiki. Duk aka rubuta waɗannan da sunayensu.
21 Then proclaimed I there a fast, by the river Ahava, that we might humble ourselves before our God, —to seek of him a smooth way, for us and for our little ones, and for all our substance.
A can, a bakin rafin Ahawa, na sa mu yi azumi, domin mu ƙasƙantar da kanmu a gaban Allah, mu kuma roƙe shi yă kiyaye mana hanya, da mu da’ya’yanmu da kayanmu duka.
22 For I was ashamed to ask of the king, a band of soldiers and horsemen, to help us against the enemy in the way, because we had spoken unto the king, saying, The hand of our God, is upon all who seek him, for good, But, his power and his anger, are against all who forsake him.
Na ji kunya in roƙi sarki yă haɗa mu da sojoji da masu dawakai don su yi mana rakiya su kāre mu daga magabta a kan hanya, gama mun ce wa sarki, “Alherin Allah yana tare da duk wanda yake dogara gare shi, amma kuma fushinsa yana kan duk wanda ya juya masa baya.”
23 So we fasted and sought of our God, concerning this, —and he suffered himself to be entreated by us.
Saboda haka sai muka yi azumi, muka kai roƙonmu a wurin Allah, ya kuwa amsa mana.
24 Then I separated, from among the rulers of the priests, twelve, —even Sherebiah, Hashabiah, and, with them, from among their brethren, ten;
Sai na keɓe manyan firistoci guda goma sha biyu tare da Sherebiya, Hashabiya da kuma’yan’uwansu guda goma.
25 and weighed unto them, the silver and the gold, and the utensils, —the heave-offering for the house of our God, which the king and his counselors and his rulers and all Israel who were present, had offered:
Na auna musu zinariya da azurfa, da kwanoni waɗanda sarki da mashawartansa, da sauran abokan aikinsa, da Isra’ilawan da suke can suka bayar domin haikalin Allahnmu.
26 I even weighed unto their hand, of silver, six hundred and fifty talents, and, of utensils of silver, a hundred talents, —of gold, a hundred talents;
Na auna musu talenti 650 na azurfa, talenti ɗari na kwanonin azurfa, talenti 100 na zinariya,
27 and, bowls of gold, twenty, of a thousand drams, —and, utensils of fine bright bronze, two, precious as gold.
kwanonin zinariya guda 20 da darajarsu ya kai darik 1,000, da kwanoni biyu na gogaggen tagulla, wanda yake darajarsa daidai da zinariya.
28 Then said I unto them, Ye, are hallowed unto Yahweh, and, the utensils, are hallowed, —and, the silver and the gold, are a freewill offering, unto Yahweh, God of your fathers:
Na ce masa, “Ku da kayan nan tsarkaka ne ga Ubangiji. Azurfa da zinariya ɗin, bayarwa ce ta yardar rai ga Ubangiji, Allah na kakanninku.
29 Watch and guard, until ye weigh [them] before the rulers of the priests and the Levites and the ancestral rulers of Israel, in Jerusalem, —in the chambers of the house of Yahweh.
Ku lura da su da kyau har sai kun isa Urushalima. Ku auna su a shirayin haikalin Ubangiji a Urushalima, a gaban manyan firistoci, da Lawiyawa, da shugabannin iyalai na Isra’ila.”
30 So the priests and the Levites accepted the weight of the silver and the gold, and the utensils, —to bring to Jerusalem, unto the house of our God.
Sa’an nan sai firistoci, da Lawiyawa suka karɓi azurfa da zinariya da kuma tsarkakan kwanonin da aka auna don a kai haikalin Allahnmu a Urushalima.
31 Then brake we up from the river of Ahava, on the twelfth of the first month, to journey unto Jerusalem, —and, the hand of our God, was upon us, and he delivered us from the grasp of the enemy and of the lier in wait, by the way.
A rana ta goma sha biyu ga watan farko, muka tashi daga bakin rafin Ahawa don mu tafi Urushalima. Alherin Allahnmu yana tare da mu, ya kuma kāre mu daga magabta da’yan fashi.
32 So we came to Jerusalem, —and we rested there, three days.
Muka iso Urushalima, inda muka huta kwana uku.
33 And, on the fourth day, was weighed—the silver and the gold and the utensils, in the house of our God, unto the hand of Meremoth son of Uriah, the priest, and, with him, was Eleazar son of Phinehas, —and, with them, were Jozabad son of Jeshua and Noadiah son of Binnui, Levites:
A rana ta huɗu muka tafi haikalin Allah, muka auna azurfa, da zinariya, da tsarkakan kwanonin, muka ba Meremot ɗan Uriya firist, da Eleyazar ɗan Finehas yana tare da shi, da kuma Lawiyawan nan, wato, Yozabad ɗan Yeshuwa, da Nowadiya ɗan Binnuyi.
34 by the number and by the weight of the whole, —and all the weight, was written down, at that time.
Aka yi lissafi aka auna kome aka tarar yana nan daidai, aka kuma rubuta yawan nauyin a lokacin.
35 They who came in out of the captivity, Sons of the Exile, offered as ascending-sacrifices unto the God of Israel—bullocks twelve for all Israel, rams ninety-six, young sheep seventy-seven, he-goats for bearing sin, twelve, —the whole, as an ascending-sacrifice unto Yahweh.
Sa’an nan sai waɗanda suka dawo daga bauta suka miƙa hadaya ta ƙonawa ga Allah na Isra’ila. Wato, bijimai guda goma sha biyu don Isra’ilawa duka, raguna tasa’in da shida,’yan raguna saba’in da bakwai, bunsurai kuma guda goma sha biyu. Aka miƙa su hadaya don zunubi. Wannan duka hadaya ta ƙonawa ce ga Ubangiji.
36 Then delivered they the decrees of the king, unto the satraps of the king, and the pashas Beyond the River, —and they upheld the people and the house of God.
Suka kuma kai saƙon sarki zuwa ga wakilansa, da kuma gwamnoni na Kewayen Kogin Yuferites waɗanda suka taimaki mutane da kuma gidan Allah.

< Ezra 8 >