< Ezra 6 >

1 Then, Darius the king, issued an edict, —and they made search in the house of the books, where the treasures were laid up in Babylon.
Sarki Dariyus kuwa ya ba da umarni a bincika a duba cikin littattafan tarihin da suke a ajiye a wurin ajiyarsu a Babilon.
2 And there was found in Achmetha, in the fortress which is in the province of Media, a roll, —and, thus, was it written therein, as a record: —
Sai aka sami takarda a Ekbatana a yankin Mediya, ga kuma abin da yake rubuce a ciki. Abin tunawa.
3 In the first year of Cyrus the king, Cyrus the king, issued an edict, as to the house of God in Jerusalem, Let the house be built, the place where they used to offer sacrifices, and let the foundations thereof be reared, —the height thereof, sixty cubits, the breadth thereof, sixty cubits;
A shekara ta farko ta mulkin sarki Sairus, sarki ya ba da umarni game da haikalin Allah a Urushalima, ya ce, Bari a sāke gina haikalin yă zama wurin miƙa hadayu, a kuma aza harsashin ginin haikalin. Tsayinsa zai zama ƙafa tasa’in, fāɗinsa kuma kamu tasa’in.
4 layers of large stones, three, and one layer of new timber, —and, as for the expenses, out of the house of the king, let them be given.
Za a jera manyan duwatsu jeri uku, da jeri ɗaya na katako. Daga asusun sarki kuma za a biya kuɗin aikin.
5 Moreover also, the utensils of the house of God, of gold and silver, which, Nebuchadnezzar, took forth out of the temple that was in Jerusalem, and brought unto Babylon, let them again be taken to the temple which is in Jerusalem every one to its place, and lay them up in the house of God.
Kwanonin zinariya da na azurfan gidan Allah waɗanda Nebukadnezzar ya kwashe daga haikali a Urushalima ya kawo Babilon, a mayar da su wurinsu a haikali a Urushalima; a sa su cikin gidan Allah.
6 Now, therefore, Tattenai pasha Beyond the River, Shethar-bozenai, and their associates, the Apharsachites, who are Beyond the River, —be ye far from thence:
Saboda haka Tattenai, gwamnan Kewayen Kogin Yuferites, da Shetar-Bozenai, da ku masu muƙami na yankin, ku bar wurin.
7 let alone the work of this house of God, —the pasha of Judah, and the elders of Judah, this house of God, shall build upon its place;
Kada ku hana wannan aiki na haikalin Allah. Bari gwamnan Yahudawa, da dattawan Yahudawa su sāke gina wannan gidan Allah a wurin da yake a dā.
8 And, from me, is issued an edict, as to that which ye shall do, with these elders of Judah, for the building of this house of God, —That, of the resources of the king, even the tribute Beyond the River, forthwith, the expenses be given unto these men, for they must not be hindered.
Na kuma ba da umarni game da abin da za ku yi wa dattawan Yahudawa cikin aikin ginin wannan gidan Allah. Daga asusun sarki a kuɗin da yake shigo wa Kewayen Kogin Yuferites za a biya mutanen nan duka, domin kada aikin yă tsaya.
9 And, whatever may be the need—whether young bullocks or rams or lambs for ascending-sacrifices unto the God of the heavens, wheat, salt, wine or oil, according to the command of the priests who are in Jerusalem, —that it he given to them day by day, without fail;
A tanada musu duk abin da suke bukata. A ba su’yan bijimai, da raguna, da’yan tumaki domin miƙa hadaya ta ƙonawa ga Allah na sama, haka kuma dole a tanada wa firistoci alkama, da gishiri, da ruwan inabi, da mai, kullum ba fasawa yadda firistoci suke yi a Urushalima
10 that they may be offering sweet-smelling sacrifices unto the God of the heavens, —and be praying for the life of the king, and his sons.
domin su miƙa hadayu masu daɗi ga Allah na Sama, su kuma yi addu’a domin lafiyar sarki da’ya’yansa.
11 And, from me, is issued an edict, that, any man who shall alter this message, let timber be torn out of his house, and being lifted up let him be fastened thereunto, —and his house, a dunghill, be made for this;
Na kuma yi umarni cewa duk wanda ya karya wannan doka sai a fitar da itace daga cikin gidansa, a fiƙe kan itacen, a tsire mutumin, sa’an nan a mai da gidansa juji.
12 and, the God who hath caused his Name to dwell there, destroy any king or people, who shall put forth their hand to alter to destroy this house of God, which is in Jerusalem. I, Darius, have issued an edict, forthwith, let it be done.
Bari Allah yă sa sunansa yă kasance, yă hamɓarar da duka wani sarki ko mutanen da za su sa hannu don a sāke wannan doka, ko kuma don su rushe haikalin nan a Urushalima. Ni Dariyus na ba da wannan umarni, bari a yi biyayya babu wasa.
13 Then, Tattenai the pasha Beyond the River, Shethar-bozenai, and their associates, —according as Darius the king had sent, so, forthwith, they did.
Saboda umarnin da sarki Dariyus ya aika, sai Tattenai, gwamnan Kewayen Kogin Yuferites da Shetar-Bozenai da abokansu suka yi biyayya da umarnin babu wasa.
14 And, the elders of the Jews, went on building and prospering, through the prophesying of Haggai the prophet, and Zechariah son of Iddo, —they both built and finished, owing to the edict of the God of Israel, and owing to the edict of Cyrus and Darius, and Artaxerxes king of Persia.
Dattawan Yahuda kuwa suka ci gaba da ginin suna yin nasara ta wurin wa’azin Haggai annabi da Zakariya ɗan Iddo. Suka kuma gama ginin haikalin bisa ga umarnin Allah na Isra’ila da kuma umarnin Sairus da Artazerzes, sarakunan Farisa.
15 And this house was finished, by the third day of the month Adar, —the which was the sixth year of the reign of Darius the king.
An gama ginin haikalin a rana ta uku na watan Adar a shekara ta shida ta mulkin Sarki Dariyus.
16 Then did the sons of Israel, the priests and the Levites, and the rest of the Sons of the Exile, keep the dedication of this house of God, with joy;
Sai mutanen Isra’ila, firistoci, Lawiyawa da kuma sauran waɗanda suka dawo daga bauta suka yi bikin keɓe gidan Allah, cike da farin ciki.
17 and offered, for the dedication of this house of God, bullocks, one hundred, rams, two hundred, lambs, four hundred, —and, he-goats, as a sin-offering for all Israel, twelve, according to the number of the tribes of Israel.
Suka miƙa bijimai guda ɗari, da raguna ɗari biyu, da’yan raguna ɗari huɗu. Suka kuma miƙa hadayu don zunubi saboda dukan Isra’ila, suka kuma miƙa bunsurai guda goma sha biyu don hadaya ta zunubi, kowane bunsuru ɗaya don kowace kabila ta Isra’ila.
18 And they set up the priests in their divisions, and the Levites in their courses, over the service of God, which was in Jerusalem, —as it is written, in the Book of Moses.
Suka kuma naɗa firistoci a gundumominsu da kuma Lawiyawa a ƙungiyoyinsu don hidimar Allah a Urushalima, bisa ga abin da aka rubuta a Littafin Musa.
19 And the Sons of the Exile kept the passover, —on the fourteenth of the first month;
A rana ta goma sha huɗu ga watan farko, sai waɗanda suka dawo daga bauta suka yi Bikin Ƙetarewa.
20 for the priests and the Levites, had purified themselves, as one man, all of them, were pure, —so they slaughtered the passover for all the Sons of the Exile, and for their brethren the priests, and for themselves.
Firistoci da Lawiyawa suka tsarkake kansu, suka zama da tsabta. Lawiyawa suka yanka ragon Bikin Ƙetarewa domin dukan waɗanda suka dawo daga bauta, da kuma domin’yan’uwansu firistoci, da kuma domin kansu.
21 Therefore the sons of Israel who had returned from the Exile and all who had separated themselves from the impurity of the nations of the land unto them, did eat, —to seek Yahweh, God of Israel;
Sai Isra’ilawa waɗanda suka dawo daga bauta suka ci tare da duk waɗanda suka keɓe kansu daga halin ƙazanta na Al’ummai maƙwabtansu, don su nemi Ubangiji, Allah na Isra’ila.
22 and kept the festival of unleavened cakes seven days, with joy, —for Yahweh had made them joyful, and had turned the heart of the king of Assyria towards them, to strengthen their hands, in the work of the house of God, the God of Israel.
Suka yi kwana bakwai suna Bikin Burodi Marar Yisti, suna cike da farin ciki, gama Ubangiji ya cika su da farin ciki don ya sa sarkin Assuriya ya canja tunaninsa, ya taimake su cikin aikin gidan Allah, Allah na Isra’ila.

< Ezra 6 >