< Ezekiel 36 >

1 Thou therefore. Son of man, Prophesy unto the mountains of Israel, —and thou shalt say, Ye mountains of Israel Hear ye the word of Yahweh.
“Ɗan mutum, ka yi annabci wa duwatsun Isra’ila ka ce, ‘Ya duwatsun Isra’ila, ku ji maganar Ubangiji.
2 Thus saith My Lord, Yahweh, Because the enemy hath said concerning you Aha! Even the high places of age-past times, for a possession have become ours
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa abokin gāba yana magana game da ku cewa, “Yauwa! Tsofaffin tuddai sun zama mallakarmu yanzu.”’
3 Therefore, prophesy, and thou shalt say, Thus saith My Lord Yahweh-Because even because they have desolated and panted for you on every side That ye should become a possession to the rest of the nations, And ye have come up into the talk of the tongue and the slander of the people
Saboda haka ka yi annabci ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin sun lalace ku suka kuma maishe ku kufai marar amfani a kowane gefe saboda ku zama mallakar sauran al’ummai da kuma abin magana da tsegumi ga mutane,
4 Therefore ye mountains of Israel, hear ye the word of My Lord Yahweh, — Thus saith My Lord, Yahweh, To the mountains and to the hills, to the channels and to the valleys, and to the desolate waste places and to the cities that are forsaken, which have become a prey and a derision, to the rest of the nations which are on every side:
saboda haka, ya duwatsun Isra’ila, ku ji maganar Ubangiji Mai Iko Duka, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana faɗa wa duwatsu da tuddai, wa kwazazzabai da kwaruruka, wa kufai da garuruwan da suka zama kango waɗanda aka washe aka wulaƙanta suka zama ganimar sauran al’ummai da suke kewaye da ku,
5 Therefore, Thus, saith My Lord, Yahweh, Surely in the fire of my jealousy, have I spoken against the rest of the nations and against Edom all of it, — Who have given my land to themselves for a possession, In the rejoicing of all the heart In contempt of soul, To make of its produce a prey.
ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa cikin kishina mai ƙuna na yi magana gāba da sauran al’ummai, da kuma gāba da Edom, gama da farin ciki da reni a zukatansu suka mai da ƙasata mallakarsu don su washe wuraren kiwonta.’
6 Therefore prophesy, concerning the soil of Israel, —and say to the mountains and to the hills to the channels and to the valleys, Thus, saith My Lord Yahweh, Behold me! In my jealousy and in mine indignation, have I spoken, Because the insult of the nations, ye have borne;
Saboda haka ka yi annabci game da ƙasar Isra’ila ka kuma ce wa duwatsu da tuddai, wa kwazazzabai da kwaruruka, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ga shi, na yi magana da kishina da hasalata saboda sun sha zargi wurin al’ummai.
7 Therefore Thus saith My Lord Yahweh, I myself have lifted my hand, - Surely the nations which are yours round about, they their own shame, shall bear:
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa na ɗaga hannuna sama na rantse cewa al’ummai da suke kewaye da ku za su sha ba’a.
8 But ye O mountains of Israel Your boughs, shall ye shoot forth, And your fruit, shall ye bear For my people Israel, For they have drawn near to enter.
“‘Amma ku, ya duwatsun Isra’ila, za ku miƙa rassanku ku ba da amfani ga mutanena Isra’ila, gama ba da daɗewa ba za su komo gida.
9 For lo! I am towards you, Therefore will I turn towards you, And ye shall be tilled and sown;
Na damu da ku kuma zan dube ku da tausayi; za ku nome ku kuma shuka,
10 And I will multiply, upon you—men, All the house of Israel All of it, Then shall the cities be inhabited, And the waste places, shall be built,
zan kuma riɓaɓɓanya mutane a kanku, dukan gidan Isra’ila ke nan. Za a zauna a birane a kuma sāke gina rusassun wurare.
11 And I will multiply upon you—man and beast, And they shall multiply and be fruitful, — And I will cause you to be inhabited as in your former estates. And will do you more good than at your beginnings, So shall ye know that am Yahweh;
Zan sa mutane da dabbobi su yi yawa a kanku, za su kuma ba da’ya’ya su kuma yi yawa. Zan zaunar da mutane a kanku kamar dā zan kuma sa ku wadaita fiye da dā. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
12 And I will bring upon you—men even my people Israel That they may possess thee, So shalt thou be theirs, as an inheritance, -And thou shalt no more again make them childless.
Zan sa mutanena Isra’ila su yi tafiya a kanku. Za su mallake ku, za ku kuma zama gādonsu; ba za ku ƙara sa su rasa’ya’yansu ba.
13 Thus saith My Lord, Yahweh, Because they are saying to you. A devourer of men, thou art, And one that didst make childless thy nations, hast thou been
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin mutane suna magana game da ku cewa, “Kun cinye mutane kuka kuma sa al’ummarku ta rasa’ya’yanta,”
14 Therefore, men, shalt thou not devour any more, - And thy nations, shalt thou make childless no more, Declareth My Lord Yahweh;
saboda haka ba za ku ƙara cinye mutane ko ku sa al’ummarku ta rasa’ya’ya ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
15 And I will not suffer to be heard against thee any more, the insult of the nations, And the reproach of the peoples, shalt thou not bear any more, - And thy nations, shalt thou not cause to stumble any more, Declareth My Lord Yahweh.
Ba zan ƙara bari ku ji maganar banza ta al’ummai ba, ba kuwa za ku ƙara shan ba’ar mutane ko in sa al’ummarku ta fāɗi ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
16 And the word of Yahweh came unto me saying:
Maganar Ubangiji ta sāke zuwa mini cewa,
17 Son of man The house of Israel were dwelling upon their own soil, But they defiled it by their way, and by their doings. Like the defilement of her that is removed, became their way before me.
“Ɗan mutum, sa’ad da mutanen Isra’ila suke zama a ƙasarsu, sun ƙazantar da ita ta wurin halinsu da kuma ayyukansu. Halinsu ya yi kamar rashin tsarkin mace a lokacin al’adarta a gabana.
18 So I poured out mine indignation upon them, Because of the blood which they had shed upon the land, - Yea with their manufactured gods, had they defiled it.
Saboda haka na husata da su domin sun yi kisankai a ƙasar kuma domin sun ƙazantar da ita da gumakansu.
19 So I dispersed them among the nations, And they were scattered throughout the lands, — According to their way and according to their doings, I judged them.
Na warwatsa su cikin al’ummai, suka kuwa warwatsu cikin dukan ƙasashe; na hukunta su gwargwadon halinsu da ayyukansu.
20 But when they entered among the nations where they did enter, then profaned they my holy Name, —in that it was said of them The people of Yahweh, these! Yet from his land, have they come forth!
Kuma ko’ina da suka tafi a cikin al’ummai sun ɓata sunana mai tsarki, gama an yi magana a kansu cewa, ‘Waɗannan mutanen Ubangiji ne, duk da haka dole su bar ƙasarsa.’
21 So then I had tender regard for my holy Name, - Which the house of Israel had profaned, among the nations, where they had entered.
Na damu saboda sunana mai tsarki, wanda gidan Isra’ila ya ɓata a cikin al’ummai inda suka tafi.
22 Therefore say thou to the house of Israel Thus saith My Lord Yahweh, Not for your sakes, am I working. O house of Israel, But for my holy Name which ye have profaned, among the nations where ye have entered;
“Saboda haka ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ba dominku ba ne, ya gidan Isra’ila da nake yin waɗannan abubuwa, amma saboda sunana ne mai tsarki, wanda kuka ɓata a cikin al’ummai inda kuka tafi.
23 Therefore will I hallow my great Name, that hath been profaned among the nations, which ye have profaned in their midst, -So shall the nations know that I am Yahweh Declareth My Lord, Yahweh, When I have hallowed myself in you, before their eyes.
Zan nuna tsarkin girman sunana, wanda aka ɓata a cikin al’umma, sunana da kuka ɓata a cikinsu. Sa’an nan al’ummai za su san cewa ni ne Ubangiji, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, sa’ad da na nuna kaina mai tsarki ta wurinku a idanunsu.
24 Therefore will I take you from among the nations, And gather you out of all the lands, - And will bring you upon your own soil;
“‘Gama zan fitar da ku daga al’ummai; zan tattara ku daga dukan ƙasashe in komo da ku zuwa ƙasarku.
25 And I will throw upon you clean water and ye shall be clean, — From all your uncleannesses and from all your manufactured gods, will I cleanse you;
Zan yayyafa muku ruwa mai tsabta, zan kuwa tsarkake ku daga dukan ƙazantarku daga kuma dukan gumakanku.
26 And I will give you a new heart, And a new spirit, will I put within you, -And I will take away the heart of stone out of your flesh, And will give you a heart of flesh;
Zan ba ku sabuwa zuciya in kuma sa sabon ruhu a cikinku; zan fid da zuciyar dutse in kuma ba ku zuciyar nama.
27 And my spirit, will I put within you, And will cause That in my statutes, ye shall walk, And my regulations, ye shall observe, and do;
Zan kuma sa Ruhuna a cikinku in kuma motsa ku ku bi ƙa’idodina ku kuma kiyaye dokokina.
28 And ye shall dwell in the land which I gave to your fathers, - And ye shall become my people, And I will become your God;
Za ku zauna a ƙasar da na ba wa kakanninku; za ku zama mutanena, ni kuwa zan zama Allahnku.
29 And I will save you out of all your uncleannesses, —And will call for the corn and will increase it, And will not lay upon you famine; And I will save you out of all your uncleannesses, —And will call for the corn and will increase it, And will not lay upon you famine;
Zan cece ku daga dukan rashin tsabtarku. Zan sa hatsi ya yi yalwa ba zan kawo yunwa a kanku ba.
30 And I will multiply The fruit of the tree, and The increase of the field, — To the end that ye may not receive any more the reproach of famine among the nations.
Zan ƙara’ya’yan itatuwa da amfanin gona, saboda kada ku ƙara shan kunya a cikin al’ummai saboda yunwa.
31 Then shall ye call to mind Your ways that were wicked, and Your doings that were not good, - And shall become loathsome in your own sight. For your iniquities and For your abominations.
Sa’an nan za ku tuna mugayen hanyoyinku da mugayen ayyukanku, za ku kuwa ji ƙyamar kanku saboda zunubanku da kuma ayyukanku na banƙyama.
32 Not for your sakes, am I working, Declareth My Lord Yahweh be it known to you, — Turn ye pale and then blush for your ways. O house of Israel.
Ina so ku san cewa ba na yi wannan saboda ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ku ji kunya ku kuma giggita saboda halinku, ya gidan Isra’ila!
33 Thus saith My Lord, Yahweh, In the day when I cleanse you, from all your iniquities, Then will I cause the cities to be inhabited, And the waste places shall be built;
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar da na tsarkake ku daga dukan zunubanku, zan sāke zaunar da ku a garuruwanku, a kuma sāke gina kufai.
34 And the land that was made desolate shall be tilled, — Whereas it was a desolation, before the eyes of every passer-by;
Ƙasar da take kango a dā za ku nome ta a maimakon zama kango a idon dukan masu ratsawa a cikinta.
35 And they shall say, This land that was made desolate hath become like the garden of Eden, - And the cities that were waste and deserted and thrown down, now fenced, are inhabited;
Za su ce, “Wannan ƙasar da take kango a dā ta zama kamar lambu Eden; biranen da dā suke kufai, kango da kuma aka lalata, yanzu suna da katanga ana kuma zama a ciki.”
36 So shall the nations that may be left remaining round about you know that, I Yahweh— Have built that which was thrown down, and Have planted that which was made desolate, — I Yahweh, have spoken and performed.
Sa’an nan al’ummai kewaye da ku da suka rage za su san cewa Ni Ubangiji na sāke gina abin da aka lalace na kuma sāke shuka abin da yake kango. Ni Ubangiji na faɗa, kuma zan aikata.’
37 Thus, saith My Lord Yahweh, Even yet—for this, will I be prevailed upon by the house of Israel to work for them, — I will multiply them-Like a flock—with men:
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa har yanzu zan ji roƙon gidan Isra’ila in kuma yi musu wannan. Zan sa mutanensu su yi yawa kamar tumaki,
38 Like a flock of holy offerings Like the flock of Jerusalem in her appointed feasts, So, shall the waste cities be filled with flocks of men, - And they shall know that, I, am Yahweh.
yawansu ya yi kamar garken tumaki don hadaya a Urushalima a ƙayyadaddun lokuta bukukkuwarta. Haka biranen da suke kufai za su cika da ɗumbun mutane. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”

< Ezekiel 36 >