< Ezekiel 16 >

1 And the word of Yahweh came unto me, saying:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Son of man Let Jerusalem know her abominations,
“Ɗan mutum, ka sa Urushalima ta san ayyukanta masu banƙyama
3 Therefore shalt thou say— Thus saith My Lord. Yahweh To Jerusalem, Thine origin and thy birth, were of the land of the Canaanite, — Thy father was the Amorite And thy mother a Hittite
ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wa Urushalima, Asalinki da haihuwarki daga ƙasar Kan’ana ne; mahaifinki mutumin Amoriyawa ne, mahaifiyarki kuma mutuniyar Hitti ce.
4 And, as for thy birth, in the day thou wast born, Thy navel-cord was not cut, And, in water, wast thou not bathed to cleanse thee, — And, as for being salted, thou was not salted, And, as for being bandaged, thou wast not bandaged.
A ranar da aka haife ki ba a yanke cibiyarki ba, ba a kuma yi miki wanka don a tsabtacce ki ba, ba a kuma goge ki da gishiri ba ko a naɗe ki cikin tsummoki.
5 No eye, threw a shield over thee, by doing for thee one of these things taking pity on thee, - But thou wast cast out on the face of the field Because thy person, was abhorred, in the day thou wast born.
Ba wanda ya dube ki da tausayi ko ya nuna miki isashen jinƙai don yă yi miki ɗaya daga cikin waɗannan abubuwa. A maimako, sai aka jefar da ke a fili, gama a ranar da aka haife ki an ji ƙyamarki.
6 And I passed by thee, and looked upon thee, thrusting about thee in thy blood, And said to thee— Despite thy blood, live! Yea I said to thee— Despite thy blood, live!
“‘Sa’an nan na wuce na ga kina birgima cikin jininki, yayinda kike kwance can cikin jininki sai na ce miki, “Ki rayu!”
7 Into myriads—like the bud of the field, made I thee, And thou didst increase and become well grown, and didst attain to most excellent adornments, — Thy breasts were well-formed And thy hair was grown, But thou thyself wast utterly naked.
Na sa kin yi girma kamar tsiro a fili. Kin yi girma kika kuma yi tsayi kika zama mafiya kyau na kayan ado. Nononki suka fito, gashinki kuwa suka yi girma, duk da haka tsirara kike tik.
8 And I passed by thee and looked upon thee and lo! thy time was the time for endearments, So I spread my skirt over thee, and covered thy shame, And took an oath to thee And entered into covenant with thee. Declareth My Lord. Yahweh. And thou didst become mine.
“‘Daga baya na wuce, da na dube ki sai na ga cewa kin yi girma sosai har kin kai a ƙaunace ki, na yafa gefen tufafina a kanki na kuma rufe tsiraincinki. Na rantse miki, na ƙulla alkawari da ke, kin kuwa zama tawa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
9 And I bathed thee in water, and rinsed thy blood from off thee, And anointed thee with oil;
“‘Na yi miki wanka na wanke miki jini daga gare ki na kuma shafa miki mai.
10 And clothed thee with an embroidered dress, And sandalled thee in red leather, And wrapped thee about with fine linen, And put over thee a mantle of silk.
Na rufe ki da rigar da aka yi wa ado na kuma sa miki takalman fata. Na sa miki riga ta lilin mai kyau na kuma rufe ki da riguna masu tsada.
11 Then decked I thee with ornaments, And put bracelets upon thy hands, And a neckchain upon thy throat;
Na yi miki ado da kayan ado masu daraja, na sa miki mundaye a hannuwanki da abin wuya a wuyanki,
12 And put a nose-jewel upon thy nose, And earrings in thine ears, And a crown of adorning, upon thy head.
na kuma sa miki zobe a hancinki, abin kunne a kunnuwanki da rawani mai kyau a kanki.
13 Thus wast thou adorned with gold and silver, And thy raiment was of fine linen and silk and embroidered work, Fine flour and honey and oil, didst thou eat, — And so thou becamest exceedingly beautiful, And didst attain unto royalty.
Haka kuwa aka caɓa miki zinariya da azurfa; tufafinki kuwa na lilin mai kyau da riguna masu tsada waɗanda aka yi musu ado. Abincinki na gari mai laushi ne, zuma da man zaitun. Kika zama kyakkyawa har kika kuma zama sarauniya.
14 Then went forth thy fame among the nations. for thy beauty, - For perfect, it was—in my splendour which I had put upon thee, Declareth My Lord, Yahweh.
Sunanki ya yaɗu a cikin al’ummai saboda kyanki, domin darajar da na ba ki ya sa kyanki ya zama cikakke, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
15 Then didst thou trust in thy beauty, And become unchaste, because of thy fame, - And didst pour out thine unchastity upon every passer-by, his it was!
“‘Amma kika dogara ga kyanki kika kuma yi amfani da sunan da kika yi don ki zama karuwa. Kin yi ta jibga alherai a kan kowa da ya wuce, sai kyanki ya zama naki.
16 Yea thou didst take of thy raiment and madest thee high places of hangings, And didst commit unchastity thereon, - Which ought not to have befallen And not to have come to pass.
Kin ɗauki waɗansu tufafinki don ki yi wa kanki masujadai masu ado, inda kike karuwancinki. Irin waɗannan abubuwa bai kamata su faru ba, bai kuma kamata su taɓa faruwa ba.
17 But thou didst take thine adorning jewels Of my gold and of my silver which I had given thee, And didst make thee images of the male, — And didst act unchastely with them;
Kika kuma ɗauki kayan ado masu kyau da na ba ki, kayan adon da aka yi da zinariya da azurfa, kika yi wa kanki gumakan maza kika kuma yi ta yin karuwanci da su.
18 And thou didst take thine embroidered raiment, and cover them, - And mine oil and mine incense, didst thou set before them;
Kika ɗauki rigunanki masu ado don ki sa a kansu, kika kuma miƙa maina da turarena a gabansu.
19 And my food which I had given thee, Fine flour and oil and honey wherewith I fed thee, And didst set it before them for a satisfying odour Yea so it was, — Saith My Lord Yahweh.
Haka ma abincin da na tanada miki, lallausan gari, man zaitun, da zuman da na ba ki ki ci, kin miƙa su kamar turare mai ƙanshi a gabansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
20 And thou didst take thy sons and thy daughters, Whom thou hadst borne unto me, And didst sacrifice them unto them to be devoured, - Is this of thine unchastity. a light thing?
“‘Kika kuma kwashe’ya’yanki maza da mata waɗanda kin haifa mini kika miƙa su kamar abinci ga gumakanki. Karuwancinki bai isa ba ne?
21 Yea thou didst slay my children, — And didst deliver them up. that they should be caused to pass through the fire unto them.
Kin kashe’ya’yana kika kuma miƙa su ga gumaka.
22 And in all thine abominations, and thine unchaste ways, thou rememberedst not the days of thy youth, When thou wast utterly naked. When thou wast thrusting about thee in thy blood!
Cikin dukan ayyukan banƙyamarki da karuwancinki ba ki tuna da kwanakin ƙuruciyarki ba, sa’ad da kike tsirara tik, kina birgima cikin jininki.
23 And it came to pass after all thy wickedness, Woe! Woe! to thee, Exclaimeth My Lord Yahweh;
“‘Kaito! Kaitonki, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Bugu da ƙari a kan dukan waɗansu muguntarki,
24 That thou didst build thee a brothel, — and didst make thee a height in every broadway:
kin gina wa kanki ɗakunan sama da gidajen tsafi a kowane dandali.
25 At the head of every road, didst thou build thy height, And bring thy beauty into disgust, And open thy feet to every passer-by, So didst thou make thine unchaste ways to abound.
A kowane titi kin gina ɗakin tsafi kika kuma wulaƙanta kyanki, kina miƙa jikinki da ƙarin fasikanci ga duk mai wucewa.
26 Then didst thou extend thine unchaste acts unto the sons of Egypt—thy neighbour great of flesh, - And caused thine unchaste ways to abound provoking me to anger.
Kin yi karuwanci da Masarawa, maƙwabtanki masu kwaɗayi, kika tsokane ni har na yi fushi da ƙarin fasikancinki.
27 Lo! therefore, I have stretched out my hand against thee, And diminished thine allotted portion, — And have delivered thee up unto the desire of them who hate thee The daughters of the Philistines, who are ashamed of thy lewd way.
Saboda haka na miƙa hannuna gāba da ke na kuma rage iyakarki; na ba da ke ga abokan gābanki masu haɗama,’yan matan Filistiyawa, waɗanda suka sha mamaki saboda halinki na lalata.
28 Thou didst also extend thine unchastity unto the sons of Assyria, because thou wast insatiable. Yet though thou didst behave unchastely with them, yet even so couldst thou not be satisfied,
Kin kuma yi karuwanci da Assuriyawa, domin ba kya ƙoshi; kai ko bayan wannan, ba ki ƙoshi ba.
29 Thou didst therefore cause thine unchaste ways to abound unto the land of Canaan as towards Chaldea. Yet even herewith, wast thou not satisfied.
Sai kika ƙara fasikancinki da ya haɗa da ƙasar cinikin Babilon, amma duk da haka ba ki ƙoshi ba.
30 How weak was thy heart! Exclaimeth My Lord Yahweh, — That thou couldst have done all these things, The doing of a lewd woman without shame:
“‘Kina da rashin ƙarfi a zuci, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, sa’ad da kika yi duk waɗannan abubuwa, kina yi kamar karuwar da aka watsa!
31 That thou couldst have built thy brothel at the head of every road, And thy height, couldst have made in every broadway, - Yet becamest not as a harlot to lay claim to a harlot’s hire.
Sa’ad da kika gina ɗakunan samanki a kowane gefen titi kika kuma gina ɗakunan tsafinki a kowane dandali, ba kamar karuwa kike ba, domin kin karɓi kuɗi.
32 A wife who committeth adultery, instead of her husband accepteth strangers.
“‘Ke mazinaciyar mace! Kin gwammace baƙi a maimakon mijinki!
33 To all harlots, they give a present, — But, thou, didst give thy presents to all thy lovers, And didst bribe them to come in unto thee from every side, in thine unchastity!
Kowace karuwa kan karɓi kuɗi, amma kina ba da kyautai ga dukan kwartayenki, kina ba su cin hanci don su zo wurinki daga ko’ina don alherai marasa ƙa’ida.
34 And so there came about in thee, the reverse of women, in thine unchastity, In that they did not follow thee for purposes of lewdness, — And in that thou gavest a present while, no present, was given to thee So didst thou become, the reverse.
Saboda haka cikin karuwancinki kin sha bamban da saura; babu wanda yake binki saboda alheranki. Ke dai dabam ce, gama kikan biya kuma ba mai biyanki.
35 Therefore O harlot, hear thou the word of Yahweh;
“‘Saboda haka, ke karuwa, ki ji maganar Ubangiji!
36 Thus saith My Lord Yahweh, — Because thy money, was poured out, and thy shame, was uncovered, in thine unchastity, unto thy lovers, —and unto all thine abominable manufactured gods, even as the blood of thy children, whom thou didst deliver up unto them,
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kin zubar da dukiyarki kika bayyana tsiraicinki cikin fasikancinki da kwartayenki, kuma saboda dukan gumakan banƙyamarki, kuma saboda kin ba su jinin’ya’yansu,
37 Therefore behold me! gathering together all thy lovers unto whom thou didst make thyself pleasant, Even all whom thou lovedst, With all whom thou hatedst, — Yea I will gather them together unto thee from every side And will uncover thy shame unto them, And they shall see all thy shame.
saboda haka zan tattara dukan kwartayenki, waɗanda kike jin daɗinsu, waɗanda kike ƙauna da waɗanda kike ƙi. Zan tattara su gāba da ke daga dukan kewaye zan kuma tuɓe ki a gabansu, za su kuwa ga dukan tsiraicinki.
38 So will I judge thee. with the judgments meted out to adulteresses and shedders of blood, - And will repay thee with the blood of indignation and jealousy;
Zan hukunta ki da hukuncin matan da suke zina da kuma waɗanda suke zub da jini; zan kawo hakkin jini na fushina da kuma fushin kishina.
39 And will deliver thee into their hand. And they shall pull down thy brothel And break in pieces thy heights, And strip thee of thy raiment, And take away thine adorning jewels, - And leave thee utterly naked.
Sa’an nan zan miƙa ki ga kwartayenki, za su kuwa rurrushe ɗakunan samanki su kuma farfashe ɗakunan tsafinki. Za su tuɓe miki tufafinki su kuma kwashe kayan adonki masu kyau su bar ki tsirara tik.
40 Then will they bring up against thee a gathered host, And they will stone thee with stones, - And cut thee to pieces with their swords;
Za su kawo taron jama’a a kanki, waɗanda za su jajjefe ki da dutse su sassare ki gunduwa-gunduwa da takubansu.
41 And burn up thy houses with fire, And execute upon thee judgments before the eyes of many women, —So will I cause thee to cease from acting unchastely, Moreover also a present, shalt thou not give any more.
Za su ƙone gidajenki su kuma hukunta ki a idon mata masu yawa. Zan kawo ƙarshen karuwancinki, ba za ki kuma ƙara biyan kwartayenki ba.
42 So will I let mine indignation find rest in thee, And my jealousy shall depart from thee, —And I will be quiet, and not be provoked any more.
Sa’an nan fushina a kanki zai huce fushin kishina kuma ya kwanta; zan huce ba kuwa zan ƙara yin fushi ba.
43 Because thou hast not remembered the days of thy youth, But hast enraged me with all these things Therefore also behold! I thy way, upon thine own head, will place Declareth My Lord Yahweh, And thou shalt not commit a crime above all thine abominations
“‘Domin ba ki tuna da kwanakin ƙuruciyarki ba amma kika husatar da ni da waɗannan abubuwa, tabbatacce zan sāka miki alhakin ayyukanki, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ba kin ƙara lalata ga dukan waɗansu ayyuka masu banƙyamarki ba?
44 Lo! every one who useth proverbs, against thee, shall use a proverb saying, — Like the mother, so her daughter!
“‘Duk mai yin amfani da karin magana zai faɗi wannan karin magana a kanki cewa, “Kamar yadda mahaifiya take haka’yar take.”
45 The daughter of thy mother, thou art! One abhorring her own husband and her own children, — Yea the sister of thy sisters, thou art Who abhorred their own husbands and their own children, Your mother was a Hittite, And your father an Amorite.
Ke’yar mahaifiyarki ce da gaske, wadda ta ƙi mijinta da’ya’yanta; ke kuma’yar’uwar’yar’uwanki mata ce da gaske, waɗanda suka ƙi mazansu da’ya’yansu. Mahaifiyarki mutuniyar Hitti ce, mahaifinki kuma mutumin Amoriyawa ne.
46 And thine elder sister, was Samaria, she and her daughters, dwelling on thy left hand, — And thy sister younger than thou dwelling on thy right hand was Sodom and her daughters.
Babbar’yar’uwarki mutuniyar Samariya ce, wadda take zaune da’ya’yanta mata wajen arewa da ke; ƙanuwarki ita ce Sodom wadda take zaune kudu da ke tare da’ya’yanta mata.
47 Yet not in their ways, didst thou walk, nor according to their abominations, didst thou do, — As though that were quite too little, thou didst corrupt thyself beyond them in all thy ways.
Ba ki bi hanyoyinsu da abubuwansu na banƙyama kaɗai ba, sai ka ce wannan ya yi miki kaɗan, amma kin lalace fiye da su.
48 As I live, Declareth My Lord Yahweh, Very! Sodom thy sister had not done, neither she nor her daughters, —as thou and thy daughters have done.
Muddin in raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka,’yar’uwarki Sodom da’ya’yanta mata ba su yi abin da’ya’yanki mata suka yi ba.
49 Lo! this became the iniquity of Sodom thy sister, — Pride, fulness of bread, and careless security came to her and to her daughters, And the hand of the oppressed and the needy, she strengthened not.
“‘To, fa, ga zunubin’yar’uwarki Sodom. Ita da’ya’yanta mata sun yi girman kai, sun ƙoshi fiye da kima kuma ba su kula da wani abu ba; ba su taimaki matalauta da kuma masu bukata ba.
50 So then they became haughty, and committed abomination before me, - And I took them away. when I saw [it],
Su masu girman kai ne kuma suka aikata abubuwa masu banƙyama a gabana. Saboda haka na kau da su kamar yadda ka gani.
51 Nor did, Samaria, commit, one-half thy sins, — But thou didst multiply thine abominations more than they, And didst cause thy sisters to appear righteous, by all the abominations which thou didst commit.
Samariya ba tă aikata ko rabin zunubanki ba. Kin aikata abubuwa masu banƙyama fiye da su, suka kuma sa’yan’uwanki mata suka zama kamar masu adalci ta wurin dukan waɗannan abubuwa da kika aikata.
52 Thou also bear thine own reproach, which thou didst adjudge to thy sisters, by thy sins in which thou wast more abominable than they, thou didst make them appear more righteous than thou, — Thou also, therefore turn thou pale and bear thine own reproach, for making thy sisters appear righteous!
Ki sha kunyarki, gama kin yi rangwame wa’yan’uwanki mata. Saboda zunubanki sun yi muni fiye da nasu, sai suka zama kamar sun fi ki adalci. Saboda haka, ki sha kunya ki kuma sha ƙasƙancinki, gama kin sa’yan’uwanki mata suka zama kamar su masu adalci ne.
53 When therefore I bring back their captivity, The captivity of Sodom and her daughters, And the captivity of Samaria and her daughters Then will I bring back thy captivities in their midst:
“‘Amma fa, zan komo da nasarar Sodom da’ya’yanta mata da ta Samariya da’ya’yanta mata, nasararki kuma tare da su,
54 That thou mayest bear thine own reproach, And take to thyself reproach because of all that thou didst in comforting them.
domin ki sha ƙasƙancinki ki kuma sha kunyar dukan abin da kika aikata ta wurin ta’azantar da su.
55 When thy sisters Sodom and her daughters shall return to their former estate, And Samaria and her daughters shall return to their former estate Then thou and thy daughters, shall return to your former estate.
’Yan’uwanki kuwa, Sodom da’ya’yanta mata da Samariya tare da’ya’yanta mata, za su koma kamar yadda suke a dā; ke kuma da’ya’yanki mata za ku koma kamar yadda kike a dā.
56 And Sodom thy sister was never heard in thy mouth, —In the day of thy pride:
Ba za ki ma iya ambaci’yar’uwarki Sodom a ranar fariyarki ba,
57 Before thy wickedness was discovered, As now, [thou art] the reproach of the daughters of Syria and all round about her the daughters of the Philistines, —who are despising thee on every side.
kafin a tone muguntarki. Ko da ma haka, yanzu’ya’yan Arameyawa mata da dukan maƙwabtanta da kuma’ya’yan Filistiyawa mata suna miki dariyar, dukan waɗanda suke kewaye da ke da suka rena ki.
58 As for thy crime and thine abominations, thou thyself, dost bear them, — Declareth Yahweh.
Za ki ɗauki hakkin lalatarki da kuma ayyukanki masu banƙyama, in ji Ubangiji.
59 For Thus, saith My Lord, Yahweh, Therefore will I deal with thee just as thou hast dealt, - In that thou didst despise an oath by breaking a covenant.
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan hukunta kamar yadda ya dace da ke, domin kin ƙyale rantsuwana ta wurin karya alkawari.
60 Therefore will I remember my covenant with thee in the days of thy youth, — And will establish for thee a covenant age-abiding.
Duk da haka zan tuna da alkawarin da na yi da ke a kwanakin ƙuruciyarki, zan kuma kafa madawwamin alkawari da ke.
61 Thou shalt therefore remember thy ways and take to thyself reproach, by receiving thy sisters. The older than thou, And the younger than thou, - And I will give them unto thee for daughters Though not by thine own covenant.
Sa’an nan za ki tuna da hanyoyinki ki kuma ji kunya sa’ad da kika karɓi’yan’uwanki mata, waɗanda suka girme ki da kuma waɗanda kika girme su. Zan ba da su kamar’ya’ya mata gare ki, amma ba bisa alkawarina da ke ba.
62 But I myself, will establish my covenant with thee— And thou shalt know that I, am Yahweh:
Ta haka zan kafa alkawarina da ke, za ki kuma san cewa ni ne Ubangiji.
63 To the end thou mayest remember and turn pale, and there be to thee no more, an opening of mouth, because of thy reproach, - In that I have accepted a propitiatory covering for thee as to all that thou hast done, Declareth My Lord. Yahweh.
Sa’an nan, sa’ad da na yi kafara saboda ke domin dukan abin da kika aikata, za ki tuna ki kuma ji kunya har ki kāsa buɗe bakinki saboda kunya, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”

< Ezekiel 16 >