< Deuteronomy 4 >

1 Now, therefore, O Israel, hearken thou unto the statutes, and unto the regulations, which, I, am teaching you, to do [them], —to the end ye may live and enter and possess the land, which, Yahweh, the God of your fathers, is giving unto you.
To, ku ji, ya Isra’ila, ku kasa kunne ga ƙa’idodi da dokokin da nake shirin koya muku. Ku bi su domin ku yi tsawon rai, ku kuma shiga ku mallaki ƙasar da Ubangiji, Allahn kakanninku yake ba ku.
2 Ye shall not add unto the word which, I, am commanding you, neither shall ye take away therefrom, —that ye may keep the commandments of Yahweh your God, which, I, am commanding you.
Kada ku ƙara, kada ku rage daga cikin abin da nake umarce ku. Amma ku kiyaye umarnan nan na Ubangiji Allahnku, da na ba ku.
3 Yours are the eyes, that have seen what Yahweh did in Baal-peor, for every man who went after Baal-peor, did Yahweh thy God destroy out of thy midst;
Da idanunku, kun ga abin da Ubangiji ya yi a Ba’al-Feyor. Yadda Ubangiji Allahnku ya hallaka waɗansu daga cikinku waɗanda suka yi wa Ba’al-Feyor sujada,
4 but, ye who kept on cleaving unto Yahweh your God, alive, are ye all to-day.
Amma ku da kuka manne ga Ubangiji Allahnku, kuna da rai har wa yau.
5 See! I have taught you statutes, and regulations, as Yahweh my God commanded me, —that ye should do so, in the midst of the land whereinto ye are entering to possess it.
Ga shi, na koya muku ƙa’idodi da dokoki, yadda Ubangiji Allahna ya umarce ni, don ku bi su a ƙasar da za ku shiga ku mallaki.
6 Therefore shall ye observe, and do [them], for that, will be your wisdom, and discernment, in the eyes of the peoples, —who will hear all these statutes, and will say—Nevertheless, a people wise and discerning, is this great nation.
Ku kiyaye su, ku aikata su, gama yin haka zai tabbatar wa sauran al’ummai, kuna da hikima da ganewa. Sa’ad da al’ummai za su ji waɗannan dokoki, za su ce, “Ba shakka, wannan babbar al’umma tana da hikima da ganewa.”
7 For what great nation is there which hath gods nigh unto it, —like Yahweh our God, whensoever we have cried out unto him.
Wace al’umma ce mai girma haka wadda allolinta take kusa da su yadda Ubangiji Allahnmu yake kusa da mu a duk sa’ad da muka yi addu’a gare shi?
8 Or what great nation which hath righteous statutes and regulations, like all this law, which, I, am setting before you to-day?
Wace al’umma ce mai girma haka wadda take da ƙa’idodi da dokoki masu adalci kamar waɗannan ƙunshin dokokin da nake sa a gabanku a yau?
9 Only take thou heed to thyself and keep thy soul diligently, so that thou forget not the things which thine own eyes have seen, and so that they go not out of thy heart, all the days of thy life, —but thou shalt make them known unto thy sons and unto thy sons’ sons: —
Ku kula, ku kuma lura da kanku sosai, don kada ku manta da abubuwan da idanunku suka gani, ko kuwa ku bari su fita daga zuciyarku muddin ranku. Ku koyar da su ga’ya’yanku, da’ya’yan’ya’yanku.
10 What day thou didst stand before Yahweh thy God, in Horeb, when Yahweh said unto me, Gather unto me the people, that I may let them hear my words, —which they must learn that they may revere me all the days which they are living upon the soil, their children also, must they teach.
Ku tuna da ranar da kuka tsaya a gaban Ubangiji Allahnku a Horeb, sa’ad da ya ce mini, “Ka tara mutane a gabana, don su ji maganata, su koya yin mini bangirma muddin ransu a ƙasar, su kuma iya koyar da su ga’ya’yansu.”
11 So ye drew near and stood, under the mountain. Now, the mountain, was burning with fire, up to the midst of the heavens, —darkness, cloud, and thick gloom.
Sai kuka matso kusa, kuka tsaya a gindin dutse yayinda yana cin wuta har zuwa sararin sama, ga kuma baƙin gizagizai da kuma baƙin duhu.
12 Then spake Yahweh unto you out of the midst of the fire, —a voice of words, ye were hearing, no form, were ye seeing, there was only a voice.
Sai Ubangiji ya yi magana daga wutar. Kuka ji furcin kalmomin, amma ba ku ga siffar kome ba, sai dai murya kaɗai kuka ji.
13 Then declared he unto you his covenant which he commanded you to do, the ten words, —and wrote them upon two tables of stone.
Ya furta alkawarinsa gare ku, Dokoki Goma, waɗanda ya umarce ku ku bi, ya kuma rubuta su a alluna biyu.
14 And unto me, gave Yahweh command, at that time, to teach you statutes and regulations, —that ye should do them, in the land whereinto ye are passing over to possess it.
Sa’an nan Ubangiji ya umarce ni a wannan lokaci, in koya muku ƙa’idodi da dokokin da za ku bi a ƙasar da kuke hayewa Urdun don mallake.
15 Ye must take diligent heed, therefore unto your own souls, for ye saw no manner of form, on the day Yahweh spake unto you in Horeb out of the midst of the fire;
Ba ku ga wata siffa a ranar da Ubangiji ya yi magana da ku a Horeb daga wuta ba. Saboda haka ku lura da kanku sosai,
16 lest ye should break faith, and make you an image, a form of any likeness, —a model of male or female;
don kada ku lalace, ku kuma yi wa kanku gunki, siffa ta wani kama, ko a kamannin namiji, ko kuwa ta mace,
17 a model of any beast that is in the earth, —a model of any winged bird, that flieth in the heavens;
ko a kamannin wata dabba a duniya, ko na wani tsuntsun da yake tashi a sama,
18 a model of any thing that creepeth on the ground, —a model of any fish that is in the waters beneath the earth;
ko kuwa a kamannin wata halittar da take rarrafe a ƙasa, ko na wani kifi a cikin ruwaye a ƙarƙashi.
19 or lest thou shouldest lift up thine eyes towards the heavens and see the sun and the moon, and the stars—all the host of the heavens, and shouldest be seduced, and shouldest bow thyself down to them and he led to serve them, —the which Yahweh thy God hath assigned unto all the peoples under all the heavens;
Sa’ad da kuka ɗaga ido kuka kali sama, kuka ga rana da wata, da taurari, da dukan halittun sama, sai ku kula fa, kada ku jarrabtu, ku ce za ku yi musu sujada, ko ku bauta musu; abubuwan nan Ubangiji Allahnku ne ya rarraba wa dukan al’umman da suke ko’ina a ƙarƙashin sararin sama.
20 whereas you, hath Yahweh taken, and brought you forth out of a smelting-pot of iron, out of Egypt, —that ye might become his own inherited people as at this day.
Amma ku, Ubangiji ya ɗauke ku, ya fid da ku daga matuya mai narken ƙarfe, wato, daga Masar, domin ku zama jama’arsa ta musamman kamar yadda kuke a yau.
21 But, Yahweh shewed himself angry with me, for your sakes, —and sware that I should not pass over the Jordan, and that I should not enter into the good land, which, Yahweh thy God, is giving unto thee as an inheritance;
Ubangiji ya yi fushi da ni saboda ku, ya kuma yi rantsuwa cewa ba zan haye Urdun, in shiga ƙasan nan mai kyau da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo ba.
22 for, I, am about to die in this land, I am not to pass over the Jordan, —but, ye, are to pass over, and possess this good land.
Zan mutu a wannan ƙasa; ba zan haye Urdun ba; amma kuna gab da ƙetarewa, ku mallaki wannan ƙasa mai kyau.
23 Take heed to yourselves lest ye forget the covenant of Yahweh your God, which he hath solemnised with you, —and so make for yourselves an image, the form of anything, the which Yahweh thy God hath forbidden thee;
Ku yi hankali kada ku manta da alkawarin da Ubangiji Allahnku ya yi da ku; kada fa ku yi wa kanku gunki a kamannin wani abin da Ubangiji Allahnku ya hana.
24 seeing that as for Yahweh thy God, a consuming fire, he is, —a jealous GOD.
Gama Ubangiji Allahnku wuta ne mai ƙuna, Allah ne mai kishi.
25 When thou shalt beget sons, and sons’ sons, and become careless in the land and break faith and make an image the form of any thing, and shalt do the thing that is wicked in the eyes of Yahweh thy God provoking him to anger,
Bayan kun haifi’ya’ya da jikoki, kuka kuma zauna na dogon lokaci a ƙasar, in har kuka lalace, kuka kuma yi wani irin gunki, kuna aikata mugunta a gaban Ubangiji Allahnku, kuna kuma sa shi fushi.
26 I take both the heavens and the earth to witness against you to-day, that ye shall, perish, speedily, from off the land which ye are passing over the Jordan to possess, —ye shall not prolong your days thereupon; for, ye shall surely be laid waste;
Yau, na kira sama da duniya, su zama shaidata a kanku. Idan kuka yi rashin biyayya, lalle za ku hallaka nan da nan daga ƙasar da kuke ƙetare Urdun ku gāda. Ba za ku daɗe a cikinta ba, amma za a kawar da ku ƙaƙaf.
27 and Yahweh will scatter you among the peoples, —and ye shall have left remaining of you men easily counted, among the nations whither Yahweh will drive you;
Ubangiji zai watsar da ku a cikin mutane, ɗan kaɗan ne kaɗai za su ragu a cikin al’umman da Ubangiji zai kai ku.
28 and ye will serve there gods made by the hands of man, —wood or stone, which neither see nor hear nor eat nor smell.
A can za ku bauta wa allolin da mutum ya yi, na itace da dutse da ba sa gani, ba sa ji, ba sa ci, ba kuma iya sansanawa.
29 If thou shalt seek from thence, Yahweh thy God, then shalt thou find him, —when thou shalt search after him with all thy heart, and with all thy soul.
Amma daga can in kuka nemi Ubangiji Allahnku, da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku, za ku same shi.
30 In thy distress, when all these things have found thee out—in the afterpart of the days, thou wilt return unto Yahweh thy God, and wilt hearken to his voice.
Sa’ad da kuke cikin wahala saboda waɗannan abubuwan da suka same ku nan gaba, to, sai ku juyo ga Ubangiji Allahnku, ku kuma yi masa biyayya.
31 For, a GOD of compassion, is Yahweh thy God, he will not forsake thee neither will he destroy thee, —nor forget the covenant of thy fathers which he sware unto them.
Gama Ubangiji Allahnku, Allah ne mai jinƙai; ba zai yashe ku ko yă hallaka, ko kuma yă manta da alkawarin da ya yi da kakanninku, wanda ya tabbatar da su da rantsuwa ba.
32 For ask, I pray you, of the former days which were before thee, even from the day when God created man upon the earth, yea from one end of the heavens even to the other end of the heavens, —whether aught was ever brought to pass, like this great thing, or was ever heard of like it:
Ku bincika dukan tarihi mana, tun daga lokacin da Allah ya halicci mutane a cikin duniya har yă zuwa yanzu; ku tantambaya daga wannan kusurwa ta samaniya zuwa waccan, ko wani babban abu irin wannan ya taɓa faruwa, ko kuma an taɓa jin labarin irinsa?
33 Did a people ever hear the voice of a god speaking out of the midst of fire, as, thou, didst hear, and yet live?
Akwai waɗansu mutanen da suka taɓa jin muryar Allah yana magana daga wuta, kamar yadda kuka ji har suka rayu?
34 Or did a god ever make trial of entering in to take unto him a nation out of the midst of a nation, by provings, by signs and by wonders and by fighting, and by a firm hand and by a stretched-out arm, and by great terrors, —according to all that Yahweh your God did for you in Egypt, before your eyes?
Akwai wani allahn da ya taɓa yin ƙoƙari yă ɗauko wa kansa wata al’umma daga wata al’umma, ta wurin gwaje-gwaje, ta wurin alamu masu banmamaki da al’ajabai, ta wurin yaƙi, ta wurin hannu mai iko, da kuma hannu mai ƙarfi, ko kuwa ta wurin ayyuka masu bangirma da na banmamaki, kamar dukan abubuwan da Ubangiji Allahnku ya yi saboda ku a Masar, a kan idanunku?
35 Thou, wast allowed to see that thou mightest know, that Yahweh, he is God, there is none other than he alone.
An nuna muku dukan waɗannan abubuwa saboda ku san cewa Ubangiji, shi ne Allah; ban da shi, babu wani.
36 Out of the heavens, he let thee hear his voice to instruct thee, —and, upon the earth, he let thee see his great fire, and his own words, thou didst hear out of the midst of the fire.
Daga sama ya sa kuka ji muryarsa, don yă hore ku. A duniya ya nuna muku wutarsa mai girma, kuka kuma ji kalmominsa daga wuta.
37 And because that he loved thy fathers, therefore chose he his seed after him, —and brought thee forth with his presence with his great might, out of Egypt;
Domin ya ƙaunaci kakanninku, ya kuma zaɓi zuriyarsu a bayansu, ya fitar da ku daga Masar ta wurin kasancewarsa da kuma ƙarfinsa mai girma,
38 to dispossess nations, greater and stronger than thou from before thee, —to bring thee in. to give unto thee their land for an inheritance: As at this day.
don yă fitar da ku a gaban al’ummai da suka fi ku girma da kuma ƙarfi, ya kawo ku cikin ƙasarsu, don yă ba ku ita ta zama gādonku, kamar yadda yake a yau.
39 So then thou must consider to-day, and bring it back to thy heart, that, Yahweh, he is God in the heavens above and upon the earth beneath, —there is none other.
Ku sani, ku kuma riƙe a zuciya a wannan rana, cewa Ubangiji shi ne Allah a sama da kuma a ƙasa. Babu wani kuma.
40 So shalt thou keep his statutes and his commandments which, I, am commanding thee to-day, that it may go well with thee, and with thy sons after thee, —and to the end thou mayest prolong thy days upon the soil, which Yahweh thy God, is giving thee, all the days.
Ku kiyaye ƙa’idodi da umarnai, waɗanda nake ba ku a yau, domin zaman lafiyarku da kuma na zuriyarku bayan ba ku, domin kuma ku yi tsawon rai a ƙasa wadda Ubangiji Allahnku yake ba ku har abada.
41 Then, did Moses set apart three cities, over the Jordan, —towards the rising of the sun:
Sa’an nan Musa ya keɓe birane uku gabas da Urdun,
42 that the manslayer might flee thither who should slay his neighbour unawares, he, not having hated him, aforetime, —and might flee unto one of these cities, and live:
waɗanda duk wanda ya yi kisankai, in ba da gangan ba ne ya kashe maƙwabcinsa, wanda babu ƙiyayya tsakaninsu a dā, zai iya gudu zuwa. Zai iya gudu zuwa cikin ɗaya daga waɗannan birane, yă tsira da ransa.
43 namely Bezer, in the desert of the table-land, for the Reubenites, —and Ramoth in Gilead for the Gadites, and Golan in Bashan, for the Manassites.
Biranen kuwa su ne, Bezer a dutsen hamada, don mutanen Ruben; Ramot Gileyad, don mutanen Gad; da kuma Golan a Bashan, don mutanen Manasse.
44 This, then is the law which Moses set before the sons of Israel:
Wannan ita ce dokar da Musa ya sa a gaban Isra’ilawa.
45 These, are the testimonies, and the statutes and the regulations, —which Moses spake unto the sons of Israel when they came forth out of Egypt:
Waɗannan su ne farillai, ƙa’idodi da kuma dokokin da Musa ya ba su, sa’ad da suka fito daga Masar.
46 over the Jordan in the valley over against Beth-peor, in the land of Sihon king of the Amorites, who dwelt in Heshbon, —whom Moses and the sons of Israel smote, when they came forth out of Egypt:
Sa’ad da suke a kwari kusa da Bet-Feyor, gabas da Urdun, a ƙasar Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulki a Heshbon, da Musa da Isra’ilawa suka ci da yaƙi sa’ad da suka fito daga Masar.
47 so they took possession of his land, and the land of Og king of Bashan the two kings of the Amorites, who were over the Jordan, —towards the rising of the sun;
Suka mallaki ƙasarsa da kuma ƙasar Og sarkin Bashan, sarakuna biyu na Amoriyawa, gabas da Urdun.
48 from Aroer which is on the edge of the ravine of Arnon, even unto Mount Sion, the same, is Hermon;
Wannan ƙasa ta tashi daga Arower a kewayen Kwarin Arnon zuwa Dutsen Siyon (wato, Hermon),
49 and all the waste plain over the Jordan, towards sunrise, even unto the sea of the waste plain, —under the slopes of the Pisgah.
ya kuma haɗa da dukan Araba gabas da Urdun, har zuwa tekun Araba a gindin gangaren Fisga.

< Deuteronomy 4 >