< 2 Samuel 10 >

1 And it came to pass, after this, that the king of the sons of Ammon died, —and that Hanun his son reigned in his stead.
Ana nan sai sarkin Ammonawa ya rasu, ɗansa Hanun kuwa ya gāje shi a matsayin sarki.
2 Then said David—I will shew lovingkindness unto Hanun son of Nahash, as his father shewed, unto me, lovingkindness. So David sent to comfort him, by the hand of his servants, as to his father, —and the servants of David came into the land of the sons of Ammon.
Dawuda ya yi tunani a ransa ya ce, “Zan yi wa Hanun ɗan Nahash alheri kamar yadda mahaifinsa ya yi mini.” Saboda haka sai Dawuda ya aiki jakadu su yi masa ta’aziyyar mutuwar mahaifinsa. Sa’ad da mutanen Dawuda suka isa ƙasar Ammonawa,
3 Then said the rulers of the sons of Ammon unto Hanun their lord—Is David honouring thy father, in thine eyes, that he hath sent unto thee comforters? Is it not, for the sake of exploring the city, and spying it out, and overthrowing it, that David hath sent his servants unto thee?
sai manyan mutanen Ammonawa suka ce wa Hanun shugabansu, “Kana tsammani Dawuda yana girmama mahaifinka ne da ya aiko da jakadu su kawo maka ta’aziyya? Ai, wayo ya yi don yă ga asirin birninmu, yă san ƙarfinmu, yă kuma ci mu da yaƙi.”
4 Wherefore Hanun took David’s servants, and shaved off half their beards, and cut off their upper garments in the middle, as far as their buttocks, —and let them go.
Saboda haka Hanun ya kama mutanen Dawuda ya aske rabin gemun kowannensu, ya yayyage rigunarsu daidai ɗuwawu, sa’an nan ya sallame su.
5 And, when they told David, he sent to meet them, because the men were greatly ashamed, —and the king said—Tarry at Jericho, until your beards be grown, then shall ye return.
Sa’ad da aka gaya wa Dawuda game da wannan, sai ya aiki manzanni su taryi waɗannan mutanen da aka ci mutuncinsu, gama an wulaƙanta su ƙwarai. Sai sarki ya ce musu, “Ku dakata a Yeriko har sai gemunku ya sāke girma, sa’an nan ku dawo.”
6 And, when the sons of Ammon saw that they had made themselves odious with David, the sons of Ammon sent and hired the Syrians of Beth-rehob, and the Syrians of Zoba—twenty thousand footmen, and of king Maacah—a thousand men, and men of Tob—twelve thousand men.
Da Ammonawa suka gane cewa Dawuda ya ji fushi da su sosai saboda abin da suka yi, sai suka yi hayar sojojin ƙasar Arameyawa dubu ashirin daga Bet Rehob da Aram-Zoba, suka kuma yi hayar sarkin Ma’aka tare da mutum dubu ɗaya, suka kuma yi hayar maza dubu goma sha biyu daga Tob.
7 And, when David heard of it, he sent Joab and all the army of heroes,
Da jin haka, Dawuda ya tura Yowab da dukan sojojin yaƙi.
8 And the sons of Ammon came out, and set in array for battle, at the entrance of the gate, —whereas, the Syrians of Zoba, and of Rehob, and the men of Tob and of Maacah, were by themselves, in the field.
Ammonawa suka fita suka ja dāgār yaƙi a ƙofar shiga birninsu, yayinda Aram-Zoba, da na Rehob, da mutane Tob, da kuma na Ma’aka, suka ja tasu dāgār a karkara.
9 And, when Joab saw that the front of the battle was towards him, before and behind, he chose out of all the chosen men of Israel, and set them in array against the Syrians;
Yowab ya ga cewa an ja masa dāgār yaƙi gaba da baya; saboda haka sai ya zaɓi waɗansu shahararrun sojoji cikin Isra’ila, ya sa su gabza da Arameyawa.
10 while, the rest of the people, he delivered into the hand of Abishai his brother, —and set [them] in array against the sons of Ammon.
Ya sa sauran mutanen a ƙarƙashin Abishai ɗan’uwansa, ya sa su gabza da Ammonawa.
11 And he said—If the Syrians be too strong for me, then shalt thou become my deliverance, —but, if, the sons of Ammon, be too strong for thee, then will I come with deliverance to thee.
Yowab ya ce, “In Arameyawa suka fi ƙarfina, sai ku kawo mini gudummawa; amma in Ammonawa suka fi ƙarfinku, sai mu kawo muku gudummawa.
12 Be strong, and let us put forth our strength, for the sake of our people, and for the sake of the cities of our God, —and, Yahweh, do what is good in his own eyes.
Ku yi ƙarfin hali, mu kuma yi yaƙi da ƙarfin zuciya saboda mutanenmu da kuma birane Allahnmu. Ubangiji zai yi abin da yake da kyau a idanunsa.”
13 And Joab drew nigh, and the people that were with him, to fight against the Syrians, —and they fled before him.
Sa’an nan Yowab da rundunar da take tare da shi suka ci gaba don su gabza da Arameyawa, Arameyawa kuwa suka gudu a gabansa.
14 And, when, the sons of Ammon, saw that the Syrians had fled, then fled they before Abishai, and entered the city, —so Joab returned from the sons of Ammon, and entered Jerusalem.
Da Ammonawa suka ga Arameyawa suna gudu, sai su ma suka ruga da gudu a gaban Abishai, suka shiga cikin birni. Sa’an nan Yowab ya komo Urushalima daga wurin yaƙin da ya yi da Ammonawa.
15 And, when the Syrians saw that they were defeated before Israel, they gathered themselves together;
Bayan Arameyawa suka ga Isra’ila ta ci su da yaƙi, sai suka sāke tattara kansu.
16 and Hadadezer sent and brought out the Syrians that were beyond the River, and they entered Helam, —Shobach the prince of the host of Hadadezer being before them.
Hadadezer sarkin Zoba ya aika a kawo Arameyawan da suke ƙetaren Kogin Yuferites. Suka iso Helam a ƙarƙashin shugabancin Shobak, shugaban dukan sojojin Hadadezer.
17 And, when it was told David, he gathered together all Israel, and passed over the Jordan, and entered Helam, —and the Syrians set themselves in array to meet David, and fought with him.
Da aka gaya wa Dawuda wannan, sai ya tattara dukan Isra’ila, ya ƙetare Urdun, ya je Helam. Arameyawa suka ja dāgār yaƙinsu, suka kara da Dawuda.
18 Then fled the Syrians before Israel, and David slew of the Syrians seven hundred chariots, and forty thousand horsemen, —Shobach also, prince of their host, smote he, that he died, there.
Amma Arameyawa suka gudu a gaban Isra’ila, Dawuda kuwa ya kashe mahayan keken yaƙinsu ɗari bakwai, da sojojin ƙasa dubu arba’in. Ya bugi Shobak, shugaban ƙungiyar sojansu ya kuwa mutu a can.
19 And, when all the kings who were servants to Hadadezer saw that they were defeated before Israel, they made peace with Israel, and served them, —and the Syrians feared to give help any more unto the sons of Ammon.
Sa’ad da dukan sarakuna waɗanda suke abokan tarayya na Hadadezer suka ga Isra’ila sun ci su da yaƙi, sai suka yi sulhu da Isra’ilawa, suka kuma zama bayinsu. Wannan ya sa Arameyawa suka ji tsoron ƙara kai wa Ammonawa gudummawa.

< 2 Samuel 10 >