< 2 Kings 10 >

1 Now, Ahab, had seventy sons in Samaria, —so Jehu wrote letters, and sent to Samaria, unto the rulers of Jezreel—the elders, and unto them who had been foster-parents for Ahab, saying:
To, akwai’ya’ya maza saba’in na gidan Ahab a Samariya. Saboda haka Yehu ya rubuta wasiƙu, ya aika su Samariya, zuwa ga shugabannin Yezireyel, da kuma ga masu lura da’ya’yan Ahab. Ya ce,
2 Now, therefore, when this letter cometh in unto you, there being, with you, the sons of your lord, —and, with you, the chariots and the homes, and a fortified city, and the armour,
“Da zarar wasiƙan nan ta sadu da ku, da yake’ya’yan maigidanku suna tare da ku, kuna kuma da kekunan yaƙi da dawakai, da birni mai katanga da makamai,
3 ye shall look out the goodliest and fittest of the sons of your lord, and set on the throne of his father, and ye shall do battle for the house of your lord.
sai ku zaɓi mafi cancanta a cikin’ya’yan maigidanku ku sa shi a kan kursiyin mahaifinsa. Sa’an nan ku yi yaƙi don gidan maigidanku.”
4 Then feared they very greatly, and said, Lo! two kings, stood not before him; how then, should, we, stand?
Amma suka razana suka ce, “Idan sarakuna biyu ba su iya yin tsayayya da shi ba, wane mu?”
5 So he that was over the house, and he that was over the city, and the elders, and the foster-parents sent unto Jehu, saying—Thy servants, we are! and, all that thou shalt say unto us, will we do, —we will make no man king, whatsoever is good in thine own eyes, do!
Saboda haka sarkin fada, da gwamnan birnin, da dattawa, da kuma masu lura da’ya’yan suka aika da saƙo ga Yehu, cewa, “Mu bayinka ne, za mu kuma yi duk abin da ka ce. Ba za mu naɗa kowa sarki ba; sai ka yi abin da ka ga ya fi kyau.”
6 Then wrote he unto them a second letter, saying—If, mine, ye are, and, unto my voice, ye intend to hearken, take ye the heads of the men who are sons of your lord, and come in unto me about this time to-morrow, in Jezreel. Now, the sons of the king, seventy persons, were with the great men of the city, who had been bringing them up.
Sai Yehu ya sāke rubuta musu wasiƙa ta biyu, ya ce, “In a gefena kuke, to, sai ku yi biyayya da ni, ku fille kawunan’ya’yan maigidanku, ku kawo mini a Yezireyel war haka gobe.” To,’ya’yan sarki, su saba’in, suna tare da manyan birni waɗanda suke lura da su.
7 And it came to pass, when the letter reached them, that they took the sons of the king, and slew them, seventy persons, —and put their heads in baskets, and sent unto him to Jezreel.
Sa’ad da wasiƙar ta iso, sai mutanen nan suka ɗauki dukan’ya’yan sarkin nan saba’in, suka kashe su, suka sa kawunansu cikin kwanduna, suka aika wa Yehu a Yezireyel.
8 And there came in a messenger and told him, saying, They have brought in the heads of the sons of the king. And he said—Lay ye them in two heaps, at the entrance of the gate, until the morning.
Da ɗan saƙon ya iso, sai aka ce wa Yehu, “Sun kawo kawunan’ya’yan sarki.” Sai Yehu ya ce, “Ku ajiye su kashi biyu a ƙofar gari har safiya.”
9 And it came to pass, in the morning, that he went out and took his stand, and said unto all the people, Righteous, are, ye! Lo! I, conspired against my lord, and slew him, but, who, smote, all these?
Da gari ya waye, sai Yehu ya fita ya tsaya a gaban dukan jama’a ya ce, “Ba ku da laifi. Ni ne na ƙulla wa maigidana maƙarƙashiya, na kuma kashe shi, amma wa ya karkashe dukan waɗannan?
10 Know ye, then, that there shall fall nought of the word of Yahweh, to the ground, which Yahweh spake concerning the house of Ahab, —but, Yahweh, hath done that which he spake through his servant Elijah.
Ku sani fa, ba kalmar da Ubangiji ya faɗa game da gidan Ahab da ba za tă cika ba. Ubangiji ya yi abin da ya alkawarta ta bakin bawansa Iliya.”
11 Then Jehu smote all that were left remaining unto the house of Ahab, in Jezreel, and all his great men, and his acquaintances and his priests, —until there was not left remaining to him, a survivor.
Saboda haka Yehu ya kashe duk waɗanda suka rage na iyalin Ahab a Yezireyel, tare da dukan fadawansa da aminansa da firistocinsa, ba a bar masa kowa ba.
12 Then arose he, and came in, and departed for Samaria, —the sheep-shearing house itself being on the road;
Sa’an nan Yehu ya nufi Samariya. Da ya kai Bet-Eked na Makiyaya,
13 so, Jehu, lighted upon the brethren of Ahaziah king of Judah, and said, Who are, ye? And they said—Brethren of Ahaziah, are, we; so we came down to salute the sons of the king, and the sons of the queen.
sai ya gamu da waɗansu daga dangin Ahaziya sarkin Yahuda, sai ya tambaye su, ya ce, “Ku, su wane ne?” Suka ce, “Mu dangin Ahaziya ne, mun kuma zo ne mu gai da iyalan sarki da kuma mahaifiyar sarauniya.”
14 Then said he, —Take them alive. So they took them alive, and slew them [casting them] into the pit of the shearing house, —forty-two men, neither left he remaining a man of them.
Sai ya umarta ya ce, “A kama su da rai!” Aka kuwa kama su aka yayyanka kusa da rijiyar Bet-Eked, su arba’in da biyu. Ba a bar wani da rai ba.
15 Then departed he from thence, and lighted on Jehonadab son of Rechab coming to meet him, and he blessed him, and said unto him—Is thy heart, right, as my heart is with thy heart? And Jehonadab said—It is. Then, if it is, give me thy hand. So he gave him his hand. And he took him up to him, into the chariot;
Bayan ya bar wurin, sai ya gamu da Yehonadab ɗan Rekab wanda yake kan hanyarsa don yă sadu da shi. Sai Yehu ya gaishe shi, ya ce, “Ka amince da ni yadda na amince da kai?” Yehonadab ya ce, “I.” Yehu ya ce, “To, in haka ne ka ba ni hannunka.” Sai ya miƙa masa, Yehu kuwa ya ja shi cikin keken yaƙin.
16 and said—Do come with me, and see my jealousy for Yahweh. So he made him ride in his chariot.
Yehu ya ce, “Zo tare da ni ka ga himmata saboda Ubangiji.” Sa’an nan ya sa suka tafi tare cikin keken yaƙinsa.
17 And, when he came into Samaria, he smote all that were left remaining unto Ahab, in Samaria, until he had destroyed him, —according to the word of Yahweh, which he had spoken unto Elijah.
Da Yehu ya isa Samariya, sai ya karkashe dukan sauran iyalin Ahab, ya hallaka su, bisa ga maganar da Ubangiji ya faɗa ta bakin Iliya.
18 Then Jehu gathered together all the people, and said unto them, —Ahab, served Baal, a little, —Jehu, will serve him, much.
Sa’an nan Yehu ya tattara dukan jama’a ya ce musu, “Ahab ya bauta wa Ba’al kaɗan ne kawai; amma Yehu zai bauta masa sosai.
19 Now, therefore, all the prophets of Baal, all his servants and all his priests, call ye for me; do not let, a man, be missing; for, a great sacrifice, have I, to Baal, no one that is missing, shall live. But, Jehu, acted, craftily, to the end he might destroy the servants of Baal.
Yanzu sai ku kira dukan annabawan Ba’al, dukan masu yin masa hidima da kuma dukan firistocinsa. Ku tabbata ba a manta da wani ba, gama zan yi wa Ba’al babbar hadaya. Duk wanda bai zo ba, a bakin ransa.” Amma Yehu yana wayo ne domin yă hallaka masu yi wa Ba’al sujada.
20 And Jehu said—Hallow ye a solemn festival unto Baal. And they made proclamation.
Yehu ya ce, “Ku kira jama’a don a girmama Ba’al.” Saboda haka suka yi shela.
21 And Jehu sent throughout all Israel, and all the servants of Baal came in, so that there was not left remaining a man, who had not come in, —and they entered the house of Baal, and the house of Baal was filled, from door to door.
Sa’an nan ya aika saƙo ko’ina a Isra’ila, dukan masu yi wa Ba’al hidima kuwa suka tattaru, ba mutumin da bai zo ba. Suka yi cincirindo a haikalin Ba’al har sai da ya cika makil.
22 Then said he to him who was over the wardrobe chamber, Bring forth vestments for all the servants of Baal. And he brought forth for them the vestments.
Sai Yehu ya ce wa mai ajiyar tufafi, “Ka kawo riguna domin dukan masu yi wa Ba’al hidima.” Sai ya fito musu da riguna.
23 Then entered Jehu, with Jehonadab son of Rechab, into the house of Baal, —and he said unto the servants of Baal—Search ye and see, that there be not here, with you, any of the servants of Yahweh, none but the servants of Baal, alone.
Sa’an nan Yehu da Yehonadab ɗan Rekab, suka shiga haikalin Ba’al. Yehu ya ce wa masu yi wa Ba’al sujada, “Ku dudduba ku tabbatar cewa babu wani bawan Ubangiji a nan tare da ku, sai masu hidimar Ba’al kawai.”
24 And, when they entered to offer sacrifices and ascending-offerings, Jehu, set him, outside, eighty men, and said—The man who shall escape, of the men whom I am bringing into your power, his own life, shall be for, his life.
Saboda haka suka shiga don su miƙa hadayu da kuma hadaya ta ƙonawa. To, Yehu ya riga ya ba wa mutane takwas wannan kashedi a waje cewa, “In waninku ya bar ɗaya daga cikin mutanen nan da nake danƙa a hannunku ya tsere, to, a bakin ransa.”
25 And it came to pass, as soon as he had made an end of offering the ascending-sacrifice, that Jehu said to the runners and to the officers—Enter, smite them, let not, a man, get out. So they smote them, with the edge of the sword, —and the runners and the officers cast them out, and then went as far as the city of the house of Baal,
Nan da nan sa’ad da Yehu ya gama yin hadayar, sai ya umarci masu gadin da hafsoshi, “Ku shiga ku karkashe su; kada ku bar wani yă tsere.” Saboda haka suka karkashe su da takobi. Masu gadin da hafsoshin suka wuwwurga gawawwakinsu waje, suka kuma shiga ciki cikin haikalin Ba’al ɗin,
26 and brought forth the idolatrous pillars that were in the house of Baal, and then burned it;
suka fitar da dutsen tsafi daga haikalin Ba’al, suka kuma ƙone shi.
27 and they brake down the pillars of Baal, —and brake down the house of Baal, and appointed it for a sewer-house—until this day.
Suka farfasa dutsen tsafin Ba’al, suka kuma rushe haikalin, mutane suka mai da wurin salga har yă zuwa yau.
28 Thus Jehu destroyed Baal out of Israel.
Ta haka Yehu ya hallaka butar Ba’al a Isra’ila.
29 Nevertheless, as for the sins of Jeroboam son of Nebat, which he caused, Israel, to commit, Jehu turned not away from following them, —the calves of gold, one being in Bethel, and the other in Dan.
Duk da haka, bai rabu da zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata ba, wato, yin sujada ga siffofin maruƙa na zinariya a Betel da kuma Dan.
30 And Yahweh said unto Jehu: Because thou hast done well, by doing that which was right in mine eyes—according to all that was in my heart, hast done to the house of Ahab, sons, of thine, unto the fourth generation, shall sit upon the throne of Israel.
Ubangiji ya ce wa Yehu, “Tun da yake ka aikata abin da yake mai kyau a idanuna, ka kuma yi wa gidan Ahab dukan abin da yake a zuciyata, ina yin maka alkawari cewa zuriyarka za su yi mulkin Isra’ila har tsara ta huɗu.”
31 But, Jehu, took not heed to walk in the law of Yahweh God of Israel, with all his heart, —he turned not away from the sins of Jeroboam, which he caused, Israel, to commit.
Duk da haka, Yehu bai mai da hankali ya kiyaye dokokin Ubangiji, Allah na Isra’ila da dukan zuciyarsa ba. Bai rabu da zunubin Yerobowam, wanda ya sa Isra’ila ta aikata ba.
32 In those days, began Yahweh to make inroads in Israel, —and Hazael smote them in all the boundaries of Israel;
A kwanakin sai Ubangiji ya fara rage girman Isra’ila, Hazayel ya yi nasara a bisa Isra’ila a ko’ina a yankinsu
33 from the Jordan, towards sunrise, all the land of Gilead, the Gadites, and the Reubenites, and the Manassites, —from Aroer, which is by the torrent of Arnon, both Gilead and Bashan.
gabas da Urdun, cikin dukan ƙasar Gileyad (yankin Gad, da na Ruben, da na Manasse), daga Arower wajen Kwarin Arnon ya ratsa Gileyad zuwa Bashan.
34 Now, the rest of the story of Jehu, and all that he did, and all his might, are they not written in the book of the Chronicles of the Kings of Israel?
Game da sauran ayyukan mulkin Yehu, da dukan abin da ya yi, a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
35 And Jehu slept with his fathers, and they buried him in Samaria, —and, Jehoahaz his son, reigned, in his stead.
Yehu ya huta tare da kakanninsa, aka binne shi a Samariya. Yehoyahaz kuma ya ci sarauta bayansa.
36 Now, the days that Jehu reigned over Israel, were twenty-eight years, in Samaria.
Yehu ya yi sarautar Isra’ila a Samariya shekara ashirin da takwas.

< 2 Kings 10 >