< 2 Chronicles 24 >

1 Seven years old, was Joash when he began to reign, and, forty years, reigned he, in Jerusalem, —and, the name of his mother, was Zibiah, of Beersheba.
Yowash yana da shekara goma sha bakwai sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi sarauta a Urushalima shekara arba’in. Sunan mahaifiyarsa Zibiya ce; ita daga Beyersheba.
2 And Joash did that which was right, in the eyes of Yahweh, -all the days of Jehoiada the priest.
Yowash ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji duka shekarun Yehohiyada firist.
3 And Jehoiada took for him two wives, —and he begat sons and daughters.
Yehohiyada ya zaɓi mata biyu dominsa, yana kuma da’ya’ya maza da’ya’ya mata.
4 And it came to pass, after this, that it was near the heart of Joash to renew the house of Yahweh.
Wani lokaci daga baya Yowash ya yanke shawara yă gyara haikalin Ubangiji.
5 So he gathered together the priests and the Levites, and said unto them—Go ye out unto the cities of Judah, and gather out of all Israel silver to repair the house of your God, year by year, and, ye, shall hasten the matter, —but the Levites hastened it not.
Ya tara firistoci da Lawiyawa wuri ɗaya ya ce musu, “Ku je garuruwan Yahuda ku karɓa kuɗin da ya kamata a biya shekara-shekara daga dukan Isra’ila, don gyaran haikalin Allahnku. Ku yi haka yanzu.” Amma Lawiyawa ba su yi haka nan da nan ba.
6 Then the king called for Jehoiada the chief, and said unto him, Wherefore hast thou not required of the Levites, to bring in out of Judah and out of Jerusalem the tribute of Moses the servant of Yahweh, and of the convocation of Israel, —for the tent of testimony?
Saboda haka sarki ya kira Yehohiyada babban firist ya ce masa, “Me ya sa ba ka bukaci Lawiyawa su kawo harajin da Musa bawan Ubangiji ya ce a biya daga Yahuda da Urushalima da kuma taron Isra’ila domin Tentin Sujada Shaida ba?”
7 For, as for Athaliah the Lawless, her sons, brake up the House of God, —moreover, all the hallowed things of the house of Yahweh, offered they unto the Baalim.
Yanzu’ya’ya muguwar macen nan Ataliya maza sun fasa zuwa cikin haikalin Allah, suka kuma yi amfani da kayayyaki masu tsarki ma wa Ba’al.
8 So the king bade [them], and they made a certain chest, —and set it in the gate of the house of Yahweh, outside.
Bisa ga umarnin sarki, aka yi akwati aka sa a waje, a mashigin haikalin Ubangiji.
9 And they made a proclamation, throughout Judah and Jerusalem, to bring in unto Yahweh the tribute of Moses the servant of God, laid upon Israel in the desert.
Aka yi umarni a Yahuda da Urushalima cewa ya kamata suka kawo wa Ubangiji harajin da Musa bawan Allah ya bukaci daga Isra’ila a hamada.
10 And all the rulers and all the people rejoiced, —and brought in and cast into the chest, until they had finished.
Dukan hafsoshi da dukan mutane suka kawo nasu kuɗin da aka sa musu da farin ciki, suna zuba su cikin akwatin sai da ya cika.
11 And it came to pass, what time the chest was brought into the office of the king by the hand of the Levites, and when they had seen that abundant was the silver, that the scribe of the king came in, and the officer of the chief priest, and they emptied the chest, and bare it, and put it back in its place, —thus, they did, day by day, and collected silver, in abundance;
Duk sa’ad da Lawiyawa suka fito da akwatin zuwa ga hafsoshin sarki, suka kuma ga cewa akwatin yana da kuɗi mai yawa, sai magatakardan fada da hafsan babban firist su zo su juya kuɗin daga akwatin su mai da shi wurinsa. Sun riƙa yin haka kullum suka tara kuɗi mai yawa.
12 and the king and Jehoiada gave it unto such as were doing the work of labouring upon the house of Yahweh, and they were hiring masons and carpenters, to renew the house of Yahweh, —moreover also, such as were fashioners of iron and bronze, to repair the house of Yahweh.
Sarki da Yehohiyada suka ba da shi ga mutanen da suka yi aikin da ake bukata don haikalin Ubangiji. Suka ɗauki masu gini da kafintoci don su gyara haikalin Ubangiji, da kuma ma’aikatan ƙarafa da tagulla don su gyara haikalin.
13 So the doers of the work wrought, and the work of restoration went forward, in their hand, —and they caused the house of God to stand forth according to its due proportions, and made it strong.
Mutanen da suke lura da aikin natsattsu ne, kuma gyare-gyaren suka ci gaba a ƙarƙashinsu. Suka sāke gina haikalin Allah bisa ga ainihin fasalinsa suka ƙara masa ƙarfi.
14 And, when they had finished, they brought in before the king and Jehoiada the rest of the silver, and he made it into utensils for the house of Yahweh, utensils of attendance, and bowls and spoons, even utensils of gold and silver. Then were they offering ascending-sacrifices in the house of Yahweh, continually, all the days of Jehoiada.
Da suka gama, suka kawo sauran kuɗin wa sarki da Yehohiyada, da su ne kuwa aka yi kayayyaki domin hidima da kuma domin hadayun ƙonawa, haka kuma kwanoni da sauran kayayyakin zinariya da azurfa. Muddin Yehohiyada yana raye, aka riƙa kawo hadayun ƙonawa a haikalin Ubangiji.
15 But Jehoiada waxed old and became satisfied with days, and died, —a hundred and thirty years old, when he died.
Yanzu Yehohiyada ya tsufa kuma cike da shekaru, ya kuwa mutu yana da shekara ɗari da talatin.
16 And they buried him in the city of David, with the kings, —because he had done good in Israel, both toward God and his house.
Aka binne shi tare da sarakuna a cikin Birnin Dawuda, saboda kirkin da ya yi a Isra’ila wa Allah da haikalinsa.
17 Now, after the death of Jehoiada, came the rulers of Judah, and bowed themselves down unto the king, —then, hearkened the king unto them.
Bayan mutuwar Yehohiyada, hafsoshin Yahuda suka zo suka yi mubaya’a wa sarki, ya kuma saurare su.
18 And they forsook the house of Yahweh, God of their fathers, and served the Sacred Stems, and the images, —so there was wrath against Judah and Jerusalem, for this their guilt.
Suka yashe haikalin Ubangiji Allah na kakanninsu, suka bauta wa ginshiƙan Ashera da kuma gumaka. Saboda laifinsu, fushin Allah ya sauko a kan Yahuda da Urushalima.
19 And he sent among them prophets, to bring them back unto Yahweh, —and they testified against them, but they would not give ear.
Ko da yake Ubangiji ya aiki annabawa zuwa wurin mutane don su dawo da su gare shi, kuma ko da yake sun ba da shaida a kansu, ba su saurara ba.
20 And, the spirit of God, clothed Zechariah son of Jehoiada the priest, and he took his stand above the people, —and said unto them, Thus, saith God, Wherefore are, ye, transgressing the commandments of Yahweh, so that ye cannot prosper, because ye have forsaken Yahweh, therefore hath he forsaken you.
Sai Ruhun Allah ya sauko a kan Zakariya ɗan Yehohiyada firist. Ya tsaya a gaban mutane ya ce, “Ga abin da Allah ya ce, ‘Me ya sa ba ku yi biyayya da umarnan Ubangiji ba? Ba za ku yi nasara ba. Domin kun yashe Ubangiji, shi ma ya yashe ku.’”
21 So they conspired against him, and stoned him with stones, by the commandment of the king, —in the court of the house of Yahweh.
Amma suka yi masa maƙarƙashiya, kuma ta wurin umarnin sarki suka jajjefe shi da duwatsu har ya mutu a filin haikalin Ubangiji.
22 Thus Joash the king, remembered not, the lovingkindness which Jehoiada his father had done for him, but slew his son, —and, as he died, he said, Yahweh see and require!
Sarki Yowash bai tuna da alherin da Yehohiyada mahaifin Zakariya ya nuna masa ba, sai ya kashe ɗansa, wanda ya ce yayinda yake mutuwa, “Bari Ubangiji yă dubi wannan yă kuma sāka maka.”
23 And it came to pass, when the year had gone round, that the force of Syria came up against him, and they entered Judah, and Jerusalem, and destroyed all the rulers of the people, from among the people, —and, all the spoil of them, sent they unto the king of Damascus.
Da shekara ta kewaye, mayaƙan Aram suka yi gāba da Yowash suka kai hari wa Yahuda da Urushalima suka kuma kashe dukan shugabannin mutane, suka aika da dukan ganima zuwa ga sarkinsu a Damaskus.
24 Although, with a comparatively few men, came the force of Syria, yet, Yahweh, delivered into their hand an exceeding large force, —because they had forsaken Yahweh, the God of their fathers, —and, upon Joash, executed they judgments.
Ko da yake mayaƙan Arameyawa sun zo da mutane kaɗan kawai, Ubangiji ya sa suka ci nasara a kan sojojin Yahuda mafi yawa, don mutanen Yahuda sun rabu da Ubangiji Allah na kakanninsu, aka kuma hukunta Yowash.
25 And, when they had departed from him, for they left him with sore diseases, his own servants conspired against him, for the blood of the son of Jehoiada the priest, and slew him upon his bed, and he died, —and, though they buried him in the city of David, yet did they not bury him in the sepulchres of the kings.
Sa’ad da Arameyawa suka janye, suka bar Yowash da mummunan rauni. Hafsoshinsa suka haɗa baki a kansa saboda kisan ɗan Yehohiyada firist da ya yi, suka kashe shi a kan gadonsa. Ta haka ya mutu aka kuma binne shi makabartan sarakuna.
26 Now, these, are they that conspired against him, —Zabad son of Shimeath the Ammonitess, and Jehozabad son of Shimrith the Moabitess.
Waɗanda suka haɗa bakin kuwa su ne Zabad ɗan Shimeyat wata mutuniyar Ammon da Yehozabad ɗan Shimrit wata mutuniyar Mowab.
27 But, as for his sons, and the greatness of the oracle on him, and the foundation of the house of God, lo! there they are written, in the commentary of the Book of Kings, —and Amaziah his son reigned in his stead.
Labarin’ya’yansa maza, annabce-annabce masu yawa game da shi, da tarihin gyaran haikalin Allah suna a rubuce a rubuce-rubuce a littafin sarakuna. Amaziya ɗansa kuwa ya gāje shi a matsayin sarki.

< 2 Chronicles 24 >