< 2 Chronicles 2 >

1 Then Solomon gave word to build a house for the Name of Yahweh, and a house for his kingdom.
Solomon ya ba da umarni don a gina haikali domin sunan Ubangiji da kuma fada wa kansa.
2 And Solomon numbered seventy thousand men to bear burdens, and eighty thousand men to hew in the mountain, —and, to oversee them, three thousand six hundred.
Ya ɗebi mutane dubu saba’in su zama’yan ɗauko, mutane dubu tamanin su zama masu fasa dutse a tuddai, da kuma mutane dubu uku da ɗari shida su zama masu lura da su.
3 And Solomon sent unto Huram king of Tyre, saying, —As thou didst deal with David my father, and didst send him cedars to build him a house to dwell in,
Solomon ya aika wannan saƙo ga Hiram sarkin Taya. “Ka aika mini gumaguman al’ul kamar yadda ka yi wa mahaifina Dawuda sa’ad da ka aika masa al’ul don yă gina fada yă zauna a ciki.
4 lo! I, am about to build a house for the Name of Yahweh my God, to hallow unto him—to burn before him sweet incense, and for a continual setting in array, and to offer ascending-sacrifices morning and evening, on the sabbaths, and on the new moons, and on the appointed feasts of Yahweh our God, -age-abiding, is this [law] for Israel.
Yanzu ina shirin ginin haikali domin Sunan Ubangiji Allahna, in kuma keɓe shi gare shi don ƙona turare mai ƙanshi a gabansa, don kuma ajiyar burodi mai tsarki kullum, da kuma don miƙa hadayun ƙonawa kowace safiya, kowace yamma, da a Asabbatai da Sababbin Wata, da kuma a ƙayyadaddun bukukkuwan Ubangiji Allahnmu. Wannan dawwammamiyar farilla ce don Isra’ila.
5 And, the house which I am about to build, [must be] great, —for great is our God, above all gods.
“Haikalin da zan gina zai zama mai girma, domin Allahnmu ya fi dukan sauran alloli girma.
6 But who is able to build unto him a house? for, the heavens, even the heaven of heavens, cannot contain him, —who then am, I, that I should build unto him a house, though only to burn incense before him?
Amma wa zai iya gina haikali dominsa, shi wanda sammai, har ma da sama sammai, ba za su iya riƙe shi ba? To, wane ne ni da zan gina haikali dominsa, in ba dai wurin ƙona hadayu a gabansa ba?
7 Now, therefore, send me a wise man, to work in gold and in silver and in bronze and in iron, and in purple and crimson and blue, and skilful to execute gravings, —with the wise men who are with me, in Judah and in Jerusalem, whom my father David did provide.
“Saboda haka sai ka aiko mini da mutum wanda ya gwanince a aiki da azurfa, tagulla, baƙin ƙarfe, da kuma shunayya, da garura, da shuɗɗan zare, da wanda kuma ya gwanince da aikin sassaƙa, domin yă yi aiki tare da gwanayen mutane da nake da su a Yahuda da Urushalima, waɗanda mahaifina Dawuda ya tanada.
8 And send me—timbers of cedar, cypress and sandal-wood, out of the Lebanon, for, I, know that, thy servants, are skilful, to cut the timbers of Lebanon, —and lo! my servants shall be with thy servants:
“Ka kuma aika mini al’ul, fir da gumaguman algum daga Lebanon, gama na san cewa mutanenka sun gwanince a yakan katakai a can. Mutanena kuwa za su yi aiki tare da naka
9 yea to prepare me timbers in abundance, —for, the house which I am about to build, [must be] great and most wonderful.
don su tanada mini katakai da yawa, domin haikalin da zan gina dole yă zama mai girma da kuma ƙasaitacce.
10 And lo! for the hewers that cut the timbers, have I given wheat as food for thy servants, twenty thousand measures, and barley, twenty thousand measures, and wine, twenty thousand baths, and oil, twenty thousand baths.
Zan ba wa bayinka masu yankan katakai waɗanda suka yanka katako, garwa niƙaƙƙen alkama dubu ashirin, garwan sha’ir dubu ashirin da randunan ruwan inabi dubu ashirin da kuma randunan man zaitun dubu ashirin.”
11 Then answered Huram king of Tyre, in writing, which he sent unto Solomon, —Because Yahweh hath loved his people, hath he set thee over them as king.
Hiram sarkin Taya ya amsa ta wurin rubuta wasiƙa zuwa ga Solomon. “Domin Ubangiji yana ƙaunar mutanensa, ya naɗa ka sarkinsu.”
12 And Huram said, Blessed be Yahweh, God of Israel, who made the heavens and the earth, —who hath given, unto David the king, a wise son, skilled in prudence and understanding, who will build a house for Yahweh, and a house for his kingdom.
Hiram ya ƙara da cewa, “Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya yi sama da ƙasa! Ya ba Sarki Dawuda ɗa mai hikima, cike da wayo da kuma sani, wanda zai gina haikali domin Ubangiji da kuma fada wa kansa.
13 Now, therefore, have I sent a wise man, skilled in understanding, pertaining to Huram my father:
“Zan aika maka Huram-Abi, wani gwani wanda ya iya aiki, kuma mai hikima,
14 son of a woman of the daughters of Dan, whose father was a man of Tyre, skilled to work in gold and in silver, in bronze, in iron, in stones and in timber, in purple, in blue and in fine white linen, and in crimson, and to grave any manner of graving, and to devise any manner of device that may be given to him, with thy wise men, and the wise men of my lord David thy father.
wanda mahaifiyarsa ta fito daga Dan, mahaifinsa kuma daga Taya. An horar da shi a aikin zinariya, azurfa, tagulla, baƙin ƙarfe, dutse, itace, da kuma shuɗi, shunayya, garura, da lilin mai kyau. Ya gogu a kowane irin zāne-zāne, zai kuma iya yin kowane zānen da aka ba shi. Zai yi aiki tare da masu sana’arka, da kuma tare da waɗanda ranka yă daɗe, Dawuda mahaifinka ya tanada.
15 Now, therefore, the wheat and the barley, the oil and the wine, whereof my lord hath spoken, let him send unto his servants;
“Yanzu fa, bari ranka yă daɗe, yă aiko wa bayinsa alkama da sha’ir da kuma man zaitun da ruwan inabin da ka alkawarta,
16 and, we, will cut down timbers out of the Lebanon, according to all thy need, and will bring them unto thee in floats, upon the sea to Joppa, —and, thou, shalt fetch them up to Jerusalem.
za mu kuwa yanka dukan gumagumai daga Lebanon da kake bukata za mu kuwa yi fitonsu ta teku, su gangara zuwa Yaffa. Za ka iya kwashe su daga can ka haura zuwa Urushalima.”
17 So Solomon numbered all the men that were sojourners, who were in the land of Israel, after the numbering, wherewith David his father had numbered them, —and they were found to be—a hundred and fifty-three thousand and six hundred.
Solomon ya ƙidaya dukan baƙin da suke cikin Isra’ila, bayan ƙidayan da mahaifinsa Dawuda ya yi; aka kuma tarar sun kai 153,600.
18 And he made up from among them—seventy thousand, to bear burdens, and eighty thousand to hew in the mountain, —and three thousand and six hundred, as overseers, to keep the people at work.
Ya sa 70,000 a cikinsu su zama’yan ɗauko, 80,000 kuma su zama masu fasan dutse a tuddai, sa’an nan 3,600 su zama shugabanni masu lura da aiki.

< 2 Chronicles 2 >