< 2 Chronicles 19 >

1 And Jehoshaphat the king of Judah returned unto his own house in peace, to Jerusalem.
Sa’ad da Yehoshafat sarkin Yahuda ya dawo zuwa fadansa a Urushalima lafiya,
2 And there came out to meet him, Jehu son of Hanani, the seer, who said unto King Jehoshaphat, Unto the lawless, was it [right] to give help? and, on them who hate Yahweh, to bestow thy love? For this cause, therefore, is there wrath against thee, from before Yahweh;
Yehu mai duba, ɗan Hanani, ya fita don yă tarye shi, ya kuma ce wa sarki, “Ya yi kyau ke nan da ka taimaki mugu ka kuma ƙaunaci waɗanda suke ƙin Ubangiji? Da yake ka yi haka fushin Ubangiji yana a kanka
3 howbeit, good things, are found with thee, -for that thou hast consumed the Sacred Stems out of the land, and hast fixed thy heart to seek God.
Duk da haka an sami wani abin kirki a wurinka, gama ka kawar da ginshiƙan Ashera a ƙasar, ka kuma sa zuciyarka a kan neman Allah.”
4 So Jehoshaphat dwelt in Jerusalem, —and he again went forth among the people, from Beersheba as far as the hill country of Ephraim, and brought them back unto Yahweh, the God of their fathers.
Yehoshafat ya zauna a Urushalima, ya kuma fita yana shiga cikin mutane daga Beyersheba zuwa ƙasar tudun Efraim ya kuma juyar da su ga Ubangiji Allah na kakanninsu.
5 And he stationed judges in the land, throughout all the fortified cities of Judah, city by city;
Ya naɗa alƙalai a kowanne daga cikin biranen katanga na Yahuda a ƙasar.
6 and said unto the judges, See what, ye, are doing, inasmuch as, not for man, must ye judge, but for Yahweh, —who will be with you, in the word of justice.
Ya faɗa musu, “Ku lura da abin da kuke yi, gama shari’ar da kuke yi ba ta mutum ba ce, amma ta Ubangiji ce, yana tare da ku sa’ad da kuke yanke shari’a.
7 Now, therefore, let the dread of Yahweh be upon you, —observe and do, for there is, with Yahweh our God, neither perversity nor respect of persons nor the taking of bribes.
Yanzu fa ku ji tsoron Ubangiji. Ku yi hankali a kan abin da kuke yi, gama Ubangiji Allahnmu ba ya sonkai ko nuna wariya ko cin hanci.”
8 And, even in Jerusalem, did Jehoshaphat station some of the Levites and the priests, and of the ancestral chiefs of Israel, to pronounce the just sentence of Yahweh, and to settle disputes, —when they returned to Jerusalem.
A Urushalima kuma, Yehoshafat ya naɗa waɗansu Lawiyawa, firistoci da kawunan iyalan Isra’ilawa don su tabbatar da an bi dokar Ubangiji, su kuma sasanta tsakanin mutane. A Urushalima za su zauna.
9 And he laid charge upon them, saying, —Thus, shall ye act, in the fear of Yahweh, faithfully and with an undivided heart.
Ya ba su waɗannan umarnai, “Ku yi aikinku da aminci da tsoron Ubangiji da dukan zuciyarku.
10 Any dispute that shall come in unto you from among your brethren who are dwelling in their cities, between blood and blood, between law and commandment and statutes and regulations, then shall ye warn them, that they may not become guilty against Yahweh, and so wrath come upon you and upon your brethren, —Thus, shall ye act, and not incur guilt.
Cikin kowane batun da ya zo gabanku daga’yan’uwanku waɗanda suke zama a birane, ko batun na kisa ne ko kuwa waɗansu batuttuwan da suka shafi doka, umarnai, ƙa’idodi ko farillai, dole ku ja musu kunne kada su yi wa Ubangiji zunubi; in ba haka ba fushinsa zai sauko a kanku da’yan’uwanku. Ku yi wannan, ta haka ba za ku kuwa yi zunubi ba.
11 And lo! Amariah the chief priest, is over you as to every matter of Yahweh, and Zebadiah son of Ishmael the chief ruler for the house of Judah, as to every matter of the king, and, as officers, the Levites are before you, —Be strong and act, and Yahweh be with the good!
“Amariya, babban firist, shi ne zai shugabance ku a kan dukan al’amuran da suke na wajen Ubangiji, Zebadiya ɗan Ishmayel kuwa, shugabanku a kan dukan al’amuran da suka shafi sarki, Lawiyawa kuma za su zama a matsayin manya a gabanku. Ku yi abubuwa da ƙarfin hali, bari kuma Ubangiji yă kasance tare da masu yin gaskiya.”

< 2 Chronicles 19 >