< 2 Chronicles 13 >

1 In the eighteenth year of King Jeroboam, began Abijah to reign over Judah:
A shekara ta sha takwas ta sarautar Yerobowam, Abiya ya zama sarkin Yahuda,
2 three years, reigned he in Jerusalem, and, the name of his mother, was Maacah, daughter of Uriel of Gibeah, —and there was, war, between Abijah and Jeroboam.
ya kuma yi mulki a Urushalima shekaru uku. Sunan mahaifiyarsa Mikahiya ce,’yar Uriyel na Gibeya. Aka kasance da yaƙe-yaƙe tsakanin Abiya da Yerobowam.
3 And Abijah began the war with a force of heroes of war, four hundred thousand chosen men, —and, Jeroboam, set in array against him to battle, with eight hundred thousand chosen men, heroes of valour.
Abiya ya tafi yaƙi tare da mayaƙa dubu ɗari huɗu jarumawa, Yerobowam kuwa ya ja dāgār yaƙi a kan Abiya da mayaƙa dubu ɗari takwas jarumawa.
4 And Abijah stood up upon Mount Zemaraim, which is in the hill country of Ephraim, —and said, Hear me, O Jeroboam and all Israel!
Abiya ya tsaya a Dutsen Zemarayim, a ƙasar tudu ta Efraim ya ce, “Yerobowam da dukan Isra’ila, ku saurare ni!
5 Is it not yours to know, that, Yahweh God of Israel gave the kingdom to David, over Israel, unto times age-abiding, —to him and to his sons, by a covenant of salt?
Ba ku san cewa Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ba da sarautar Isra’ila ga Dawuda da zuriyarsa har abada ta wurin alkawarin gishiri ba?
6 Yet hath Jeroboam son of Nebat, servant of Solomon son of David, risen up, —and rebelled against his lord.
Duk da haka Yerobowam ɗan Nebat, ma’aikacin Solomon ɗan Dawuda, ya tayar wa maigidansa,
7 And there are gathered unto him vain men, sons of the Abandoned One, who emboldened themselves against Rehoboam son of Solomon, -when, Rehoboam, was young and tender of heart, and had not strengthened himself to meet them.
sai ya tara wa kansa’yan iska da mugayen mutane suka yi gāba da Rehobowam ɗan Solomon. Rehobowam lokacin kuwa ba shi da wayo, don haka bai iya tsai da su ba.
8 Now, therefore, ye, are thinking to strengthen yourselves against the kingdom of Yahweh, in the hand of the sons of David, —and, ye, are a great multitude, and, with you, are calves of gold, which Jeroboam hath made you for gods.
“Yanzu kuna shirin yin tsayayya da mulkin Ubangiji, wanda yake a hannuwan zuriyar Dawuda. Tabbatacce ku ƙasaitacciyar mayaƙa ne kuma kuna tare da ku maruƙan zinariyar da Yerobowam ya yi domin su zama allolinku.
9 Have ye not driven out the priests of Yahweh, the sons of Aaron, and the Levites, —and made for yourselves priests like the peoples of the countries? Whosoever cometh to install himself with a young bullock, and seven rams, then becometh he a priest unto the, no-gods.
Ba ku ne kuka kori firistocin Ubangiji,’ya’yan Haruna maza, da Lawiyawa kuka kuma zaɓi firistocinku kamar yadda sauran al’ummai suke yi ba? Duk wanda ya zo ya miƙa ɗan bijimi da raguna bakwai don yă tsarkake kansa, ya zama firist na gumaka ke nan, ba na Allah ba.
10 But, as for us, Yahweh, is our God, and we have not forsaken him, —and, the priests who are waiting upon Yahweh, are sons of Aaron, with Levites in the work;
“Gare mu kuwa, Ubangiji shi ne Allah, kuma ba mu yashe shi ba. Firistocin da suke bauta wa Ubangiji’ya’yan Haruna maza ne, Lawiyawa ne kuwa suke taimakonsu.
11 and they are making a perfume unto Yahweh, with ascending-sacrifices morning by morning, and evening by evening and an incense of sweet spices, and are putting in order bread upon the pure table, and the lampstand of gold with the lamps thereof, for lighting up evening by evening, for, observant, are we of the charge of Yahweh our God, —whereas, ye, have forsaken him.
Kowace safiya da kowace yamma sukan miƙa hadayun ƙonawa da turare mai ƙanshi ga Ubangiji. Sukan shirya burodi a tsarkaken tebur mai tsabta, sukan kuma ƙuna fitilu a alkukai kowace yamma. Muna kiyaye ƙa’idodin Ubangiji Allahnmu. Amma ku kun yashe shi.
12 And lo! with us as Head, is God himself, and his priests, and the trumpets of alarm, to sound an alarm against you, —O sons of Israel! do not fight against Yahweh God of your fathers, for ye shall not prosper.
Allah yana tare da mu; shi ne shugabanmu. Firistocinsa tare da ƙahoni za su busa kirarin yaƙi a kanku. Mutanen Isra’ila, kada ku yi yaƙi da Ubangiji Allah na kakanninku, gama ba za ku yi nasara ba.”
13 But, Jeroboam, sent round an ambush, to come up from behind them, —so they were before Judah and, the ambush, did come up from behind them.
To, fa, Yerobowam ya aiki mayaƙa su zagaya daga baya, domin yayinda yake a gaban Yahuda, sai’yan kwanto su kasance a bayansu.
14 And, when Judah turned and lo! as for them, the battle was before and behind, then made they outcry unto Yahweh, —and, the priests, kept on blowing with the trumpets.
Yahuda ya juya sai ya ga cewa ana yaƙe su gaba da baya. Sai suka yi kuka ga Ubangiji. Firistoci suka busa ƙahoni
15 Then the men of Judah gave a shout, —and it came to pass, when the men of Judah shouted, then, God himself, smote Jeroboam and all Israel, before Abijah and Judah.
mutanen Yahuda kuwa suka tā da kirarin yaƙi. Da ji kirarin yaƙi, Allah ya fatattake Yerobowam da dukan Isra’ila a gaban Abiya da Yahuda.
16 And the sons of Israel fled from before Judah, —and God delivered them into their hand.
Isra’ilawa suka gudu a gaban Yahuda, Allah kuwa ya bashe su a hannuwansu.
17 And Abijah and his people smote among them with a great smiting, —and there fell down slain, of Israel, five hundred thousand chosen men.
Abiya da mutanensa suka kashe su sosai, har mutum dubu ɗari biyar suka mutu a cikin jarumawan Isra’ila.
18 Thus were the sons of Israel subdued at that time, —and the sons of Judah prevailed, because they leaned upon Yahweh the God of their fathers.
Aka cinye mutanen Isra’ila a wannan lokaci, mutanen Yahuda kuwa suka yi nasara domin sun dogara ga Ubangiji Allah na kakanninsu.
19 And Abijah pursued after Jeroboam, and captured from him, cities, even Bethel, with the villages thereof, and Jeshanah, with the villages thereof, —and Ephron, with the villages thereof;
Abiya ya kori Yerobowam ya kuma ƙwace garuruwan Betel, Yeshana da Efron, tare da ƙauyukan da suke kewaye daga gare shi.
20 neither was Jeroboam strong any more, in the days of Abijah, —and Yahweh smote him that he died.
Yerobowam bai sāke yin ƙarfi a zamanin Abiya ba. Ubangiji ya buge shi ya kuma mutu.
21 And Abijah strengthened himself, and took him, fourteen wives, —and begat twenty-two sons, and sixteen daughters.
Amma Abiya ya ƙara ƙarfi. Ya auri mata goma sha huɗu, ya kuma kasance da’ya’ya maza ashirin da biyu da kuma’ya’ya mata goma sha shida.
22 And, the rest of the story of Abijah, both his ways and his words, —are written, in the commentary of the prophet Iddo.
Sauran ayyukan sauratar Abiya, abin da ya yi da abin da ya faɗa, a rubuce suke a cikin rubuce-rubucen annabi Iddo.

< 2 Chronicles 13 >