< 1 Kings 5 >

1 And Hiram King of Tyre sent his servants unto Solomon, for he had heard that, him, had they anointed king, in the room of his father, —for, Hiram, was, a lover, of, David continually.
Sa’ad da Hiram sarkin Taya ya ji an shafe Solomon sarki yă gāji mahaifinsa Dawuda, sai ya aika da jakadunsa zuwa wurin Solomon, gama shi da Dawuda abokai ne sosai dukan kwanakinsa.
2 So Solomon sent unto Hiram, saying: —
Solomon ya mayar da wannan saƙo ga Hiram ya ce,
3 Thou, knewest David my father, how that he could not build a house unto the Name of Yahweh his God, because of the wars that were about him on every side, —until Yahweh should put them under the soles of his feet;
“Ka san cewa saboda yaƙe-yaƙen da abokan gāba suka yi da mahaifina a kowane gefe, ya sa bai iya gina haikali domin Sunan Ubangiji Allahnsa ba, sai da Ubangiji ya sa abokan gābansa a ƙarƙashin ƙafafunsa.
4 but, now, Yahweh my God hath given me rest on every side, —there is neither adversary nor incident of evil.
Amma yanzu Ubangiji Allahna ya ba ni hutu a kowane gefe, babu kuma gāba ko masifa.
5 Behold me! then, purposing to build a house for the Name of Yahweh my God—even as Yahweh spake unto David my father, saying—Thy son, whom I will set in thy stead, upon thy throne, he, shall build the house for my Name.
Ina niyya in gina haikali domin Sunan Ubangiji Allahna, yadda Ubangiji ya faɗa wa mahaifina Dawuda, sa’ad da ya ce, ‘Ɗanka wanda zai gāje ka, shi zai gina haikali domin Sunana.’
6 Now, therefore, command thou that they fell me cedars, out of Lebanon, and, my servants, shall be, with thy servants, and, the hire of thy servants, will I give thee, according to all that thou shalt say, —for, thou, knowest, that, none amongst us, hath skill to fell timber, like the Zidonians.
“Don haka, ka ba da umarni a yanka mini itatuwan al’ul na ƙasar Lebanon. Ma’aikatana za su haɗa hannu da ma’aikatanka, ni kuwa zan biya ka albashin ma’aikatanka kamar yadda ka faɗa. Gama ka san cewa babu wani a cikinmu da ya iya yanka itacen katako kamar Sidoniyawa.”
7 And it came to pass, when Hiram heard the words of Solomon, that he rejoiced greatly, —and said: Blessed, be Yahweh, to-day, who hath given unto David a wise son, over this great people!
Da Hiram ya ji saƙon Solomon, sai ya ji daɗi ƙwarai, ya kuma ce, “Yabo ga Ubangiji a yau, gama ya ba wa Dawuda ɗa mai hikima yă yi mulki a bisa wannan al’umma mai girma.”
8 And Hiram sent unto Solomon, saying, I have heard that which thou hast sent unto me, —I, will do all thy desire, as to timber of cedar, and timber of fir.
Sai Hiram ya aike wa Solomon da kalmomin nan, “Na sami saƙon da ka aika mini, zan kuma yi duk abin da kake so ta wurin tanada katakan al’ul da na fir.
9 My servants, shall bring them down out of Lebanon unto the sea, and, I, will put them in rafts on the sea, unto the place of which thou shalt send me word, and will cause them to be discharged there, and, thou, shalt receive them, and, thou, shalt do my desire, by giving food for my household.
Ma’aikatana za su gangara da su daga Lebanon zuwa bakin teku. Zan sa a ɗaɗɗaura su su bi ruwan teku daga Lebanon zuwa bakin Bahar Rum da za ka nuna mini. A can zan kunce maka su, sa’an nan ka kwashe. Kai kuma za ka biya bukatata ta wurin tanadin abinci wa gidana.”
10 So then Hiram began giving unto Solomon timber of cedar, and timber of fir, even all his desire,
A haka Hiram ya ci gaba da aika wa Solomon al’ul da kuma fir da yake bukata.
11 and, Solomon, gave unto Hiram, twenty thousand measures of wheat, as food for his household, and twenty measures of beaten oil, —thus, used Solomon on to give unto Hiram, year by year.
Solomon kuma ya ba wa Hiram mudu gari dubu ashirin na alkama a matsayin abinci domin gidansa, ya ƙara da garwa dubu ashirin na tataccen man zaitun. Solomon ya ci gaba da yin haka ga Hiram, shekara-shekara.
12 And, Yahweh, gave wisdom unto Solomon, as he promised him, —and it came to pass that there was peace between Hiram and Solomon, and, they two, solemnised a covenant.
Ubangiji ya ba wa Solomon hikima, kamar yadda ya yi masa alkawari. Dangantakar zaman lafiya ta kasance tsakanin Hiram da Solomon, su biyun suka yi yarjejjeniya.
13 And King Solomon raised a labour-band, out of all Israel, —and it came to pass that, the labour-band, was thirty thousand men.
Sarki Solomon ya ɗebi ma’aikata daga dukan Isra’ila, su dubu talatin.
14 And he sent them to Lebanon, ten thousand a month, by courses, a month, were they in Lebanon, two months, at home, —and, Adoniram, was over the levy.
Ya riƙa aika su dubu goma-goma zuwa Lebanon kowane wata, saboda su yi wata ɗaya a Lebanon, watanni biyu kuma a gida. Adoniram ne ya lura da aikin gandun.
15 And it came to pass that, Solomon, had seventy thousand bearers of burdens, —and eighty thousand hewers in the mountain;
Solomon ya kasance da’yan ɗauko guda dubu saba’in da masu yankan duwatsu guda dubu tamanin a cikin tuddai,
16 besides the chiefs of Solomon’s officers, who were over the work, three thousand and three hundred, —who ruled over the people that wrought in the work.
ya kuma kasance da shugabanni dubu uku da ɗari uku waɗanda suke lura da aikin, su ne kuma suke bi da ma’aikatan.
17 And the king commanded, and they quarried great stones, costly stones, to found the house with hewn stones.
Bisa ga umarnin sarki sai suka cire manyan duwatsu masu kyau don a tanada tushen duwatsun da aka gyara domin haikalin daga wurin haƙar duwatsun.
18 And Solomon’s builders and Hiram’s builders with the Gebalites wrought them, —thus made they ready the timber and the stones, for building the house.
Gwanayen Solomon da na Hiram da kuma mutanen Gebal, su suka yanka, suka kuma shirya katako da dutse don ginin haikali.

< 1 Kings 5 >